• Farawa
  • Na Baya
  • 25 /
  • Na Gaba
  • Karewa
  •  
  • Gurzawa HTML
  • Gurzawa Word
  • Gurzawa PDF
  • Budawa: 4196 / Gurzawa: 2097
Girma Girma Girma
Imamanci Da Nassi

Imamanci Da Nassi

Mawallafi:
Hausa

IMAMANCI DA NASSI

Wallafar: Al-Majma'ul alami Li Ahlil-bait

Fassarar: Hafiz Muhammad Sa’id

DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI

Ahlul Baiti a Kur’ani da Hadisai :

“Kawai Allah yana son ya tafiyar da dauda daga gareku Ahlul Baiti kuma ya tsarkake ku tsarkakewa”[1].

“Ni na bar muku nauyaya biyu; Littafin Allah da Ahlin gidana, ba zaku taba bata ba bayana har abada matukar kun yi riko da su”[2] .

Gabatarwar Al-Majma'ul alami Li Ahlil-bait

Lallai yana daga cikin dabi’ar mutane su yi sabani a junansu, sai dai Allah yana son wannan sabanin ya takaita a cikin kewayen ingantaccen imani, saboda haka ne ba makawa ya zamanto akwai ma’auni tabbatacce da masu sabani zasu koma zuwa gare shi. Allah madaukaki ya saukar da littafi da gaskiya domin ya yi hukunci tsakanin mutane da gaskiya cikin abin da suka saba a cikinsa[3] . Da babu wannan gaskiya guda daya, to da al’amarin rayuwa ba zai daidaitu ba, Wannan shi ne abin da Kur’ani yake tabbatar da shi kuma yake bisa ka’idar tauhidi, sannan sai daga baya aka samu karkata da sabani da camfe-camfe har mutane suka nisanta daga wannan asasi nisanta mai girma.

Ta haka ne ta bayyana cewa mutane ba su ne masu cancantar su yi hukunci da gaskiya ko karya ba matukar sun kasance suna iya biye wa son rai da bata da zalunci. Duk da littafin Allah ya sauka da shiriya ya kuma isa zuwa ga mutane, tare da hakan son rai ya rinjayi mutane nan da can, kwadayi da tsoro da bata suka nisantar da mutane ga karbar hukuncin littafi da komawa zuwa ga gaskiya da yake dawo da su zuwa gareta. Bata shi ne ya jagoranci mutane a tsawon zamani zuwa ga sabani da shisshigi da kin Allah, Jahilci ya zama wani sababin sabani da rarraba, sai dai shi jahili ya kamata ne ya tambayi malamai kamar yadda Allah ya fada: “Ku tambayi ma’abota sani idan ba ku sani ba[4] ”.

Ta haka ne ketare iyakar jahili ya kasance zalunci da shisshigi ga wannan asali wanda hankali yake amincewa da shi, kuma ma’abota hankula suke karkata zuwa gareshi, kuma lallai wannan shi ne mafi bayyanar ka’idoji da hanyoyi wadanda zasu toshe hanyar rarraba da sabani. Musulunci shi ne addinin Allah dawwamamme da hakikarsa ta bayyana cikin nassin littafin Allah (S.W.T) da sunnar manzonsa (S.A.W) da ba ya magana da son rai sai da wahayi. Kuma Allah da manzonsa sun sani cewa al’ummarsa zata yi sabani bayansa kamar yadda ta yi sabani a lokacin rayuwarsa, don haka ne Kur’ani mai girma ya sanya wa al’umma makoma da zasu dogara da ita bayan wafatin manzo (S.A.W) tana tafiya tare da shi taku-taku tana kuma gabatar wa al’umma abin da suka takaita ga fahimtarsa da tafsirinsa, wannan kuwa su ne; Ahlul Baiti (A.S), sun tsarkaka ne daga dukkan dauda da kuma kazanta wadanda Kur’ani ya sauka ga kakansu Mustapha (S.A.W), suna karbarsa suna karanta shi suna hankaltarsa da kiyayewa, sai Allah ya ba su abin da bai ba waninsu ba... Kamar yadda manzo ya yi wasiyya da su a matsayin makoma ta gaba daya a hadisin sakalain mash’huri, sai suka kwadaitu wajan kare shari’ar musulunci da Kur’ani mai girma daga fahimta ta kuskure da tafsiri na barna, suka saba da bayanin ma’anarsa madaukakiya, sai suka zama makoma kuma madogara ga al’ummar musulmi, suna kore shubuha suna masu karbar tambayoyi da hakuri da juriya. Bayan nan abin da suka bari mai yawa yana shaidawa da kyawon mu’amalarsu tare da masu tambayarsu da tattaunawa da su, kuma komawa garesu da zurfin amsawarsu yana nuni zuwa ga kasancewarsu makoma ta ilimi a wannan fage.

Hakika koyarwarsu ta kare abin da suka bari, kuma mabiyansu suka kwadaitu a kan kare shi daga tozarta, abin da yake nuni zuwa ga koyarwarsu da ta tattaro dukkan wasu rassa na ilimomin da suke kunshe cikin koyarwar addinin musulunci. Kuma wannan makaranta ta iya tarbiyyatar da mutane da suke shirye domin kamfata daga wannan ilmi kuma ta fitar wa al’umma manyan malamai masu biyayya ga tafarkin Ahlul baiti (A.S), suna masu gamewa da sanin dukkan mas’alolin mazhabobi daban-daban, da kuma akidoji a cikin da’irar musulunci da wajanta, suna masu bayar da mafi kyawon amsa da bayanai a tsawon zamanin da ya gabata.

Hakika majma Ahlul baiti ya gaggauta yana mai farawa daga nauyin da yake kansa da ya dauka a kafadunsa domin kariya ga sakon musulunci wanda ma’abota mazhabobi da kuma masu akidu da suka saba wa musulunci suka damfaru da su, yana mai bin tafarkin Ahlul Baiti (A.S) da mabiyansu da suka kwadaitar da raddi kan kalubalen wannan zamani da kuma kokarin dawwama a kan tafarkin gwagwarmaya daidai gwargwadon abin da kowane zamani yake bukata. Ilimin da littattafan malamai masana ma’abota bin koyarwar Ahlul baiti (A.S) suka taskace shi a wannan al’amari ba shi da misali, domin shi madogara ce ta ilmi da yake karfafa da dogara da hankali da hujja, yake kuma nisantar son rai da zargi, yake kuma magana da malamai masu tunani daga ma’abota kwarewa, maganar da hankali yake yarda da ita kuma dabi’ar dan Adam kubutacciya take karbar ta.

Kokarin majma ya zo ne domin ganin an gabatar wa dalibai sabuwar marhalar wannan ilimi mai wadata a shafin tattaunawa da tambaya da kuma raddin shubuha da a kan tayar daga lokaci zuwa lokaci tsawon zamani, ko kuma ake kawo wa a yau musamman ma da taimakon wasu kungiyoyi masu kin musulunci da musulmi a cikin sarkar gizo-gizo ta intanet da makamantansu, muna masu nisantar abin da yake maras kyau, muna masu kwadayin motsa tunanin masu hankali da masu neman gaskiya domin su bude idanunsu a kan gaskiyar da koyarwar da Ahlul baiti (A.S) suka gabatar wa duniya baki daya a zamanin da hankula suke cika, alakar mutane da tunani take samuwa cikin gaggawa. Ba makawa mu yi nuni da cewa wannan tattararrun bahasosi an tanade su ne a lujna ta musamman da Hujjatul Islam Abul Fadal Islami yake shugabanta tare da wasu manya da suka hada da Sayyid Munzir Hakim, da Shaikh Abudlkarim Bahabahani, da Sayyid Abdurrahim Musawi, da Shaikh Abdul Amir Assuldani, da Shaikh Muhammadul Amini, da Shaikh Muhammad Hashimi Al’amili, da Sayyid Muhammad Rida aali Ayyub, da Shaikh Ali Baharami, da Husaini Salihi, da Aziz Al’ukabi. Kuma muna mika godiya mai yawa ga dukkan wadannan da kuma ma’abota falala da bincike da suka hada da: Shaikh Yusuf Garawi, da Shaikh Ja’afarul Hadi, da Ustaz Sa’ib Abdulhamid, domin bibiyar da kowannensu ya yi wa wadannan bahasosi da kuma bayanansu masu kima. Fatanmu shi ne ya zama mun gabatar da abin da zamu iya na kokarin sauke nauyin da yake kanmu game da wannan sako mai girma na ubangijinmu da ya aiko manzonsa da shiriya da kuma addinin gaskiya domin ya daukaka shi a kan dukkan wani addini kuma Allah ya isa shaida.

Al-Majma'ul alami Li Ahlil-bait

Birnin Kum – Iran

Imamanci Da Nassi

Allah ya halicci mutum bisa dabi’a da daukar mataki da iya daukar nauyi da zai iya kai shi ga halifancin Allah a bayan kasa, ba zai yiwu ga kowane mahaluki ba ya iya wannan al’amari koda kuwa mala’ika ne, domin su an umarce su da su yi sujada gareshi. A wani bangaren kuma mutum yana mallakar wata nau’in dabi’a da takan iya hana daukakarsa da cigaban kamalarsa. Wannan mutum yana dauke da siffofi madaukaka ta wata fuskar, da kuma siffar karkata zuwa ga kaskanci a gefe guda, abin da yake nuna cewa shi abin halitta ne daya da yake mallakar nufi da ‘yanci a kan ya zabi aiki mafi karfi da kuma matakin da ya dace domin gina rayuwarsa. An ba wa mutum wannan ne domin ba shi damar motsawa a dukkan sasanni mafi fadi da yake keta duniyar mariskai zuwa sama da hakan, da kuma nuna cewa samuwarsa tana da wani hadafi da hannun kudura ya zana shi. Ba a halicce shi don wasa ba, ba a kuma bar shi haka nan ba, kamar yadda ambato mai hikima ya fada yayin da ya ce: “Shin kuna tsammanin mun halicce ku don wasa, kuma ku ba masu komowa ne zuwa garemu ba[5] ”.

Kokari a cikin wannan hadafi da tsari da aka shirya su domin kaiwa ga hadafin asasi bai takaita da dan Adam ba, akwai sauran halittu da suke tarayya da shi a wani bangare da nassin Kur’ani mai girma yake cewa: “Ba mu halicci sammai da kasa da abin da yake tsakaninsu ba muna masu wasa[6] ”. Idan ya tabbata cewa halitta dukkanta tana tafiya da hikima, da tafiyarwar Ubangiji wacce ta hada da mutum, kuma dukkansu masu tafiya ne zuwa ga cimma wani hadifi da ake bukata, kuma cewa kowane abu yana da shiriyarsa, to menene hadafin da saboda shi ne aka halicci mutum? Kur’ani mai girma yana iyakance wannan hadafin da aka halicci mutum saboda shi da fadinsa: “Ban halicci mutum da aljani ba sai don su bauta mini[7] ”. A nan zamu yi la’akari da cewa kalmar taskacewa da togewa (sai don) tana nufin Allah ba shi da wani hadafi da manufa na halittar mutum sai ibada, kalmar don su bauta min tana bayanin sababi da dalilin halitta shi ne, wato mutum halitta ce don ibada ga Allah, Amma tambaya a nan ita ce: Idan hadafin halittar mutum yana takaituwa ne a ibada ba wani abu ba to mecece ibada? Menene kuma hakikaninta? Idan hadafi na karshe na halittar mutum shi ne kusancin Allah da bauta da dan Adam yake samun kamala da ita, to menene yake tunkuda shi domin kaiwa zuwa ga wannan kamalar?

Hakika mutum a dabi’arsa da fidirarsa yana riskar cewa, biyan bukatarsa tana zama ta hanyar da zai iya toshe tawayar da take samunsa, kamar yadda yake riskar bukatarsa ta hanyar abubuwan da sukan iya kai shi ga kamalarsa sai ya motsa domin nemanta, sai dai tambaya a nan ita ce: Ta yaya ne zai kai ga wannan kamalar? Daga nan ne zamu samu hikima ta Ubangiji ta hukumta sanya wa mutum abubuwan da ta hanyar su ne zai iya sani da tarbiyya da rikon hannunsa zuwa ga kamala. Yayin da abubuwan da dan Adam yake riska shi kadai da hankalinsa suka zama sun gajiya a kan su kama hannun shi wannan mutum domin su kai shi zuwa ga tafarkin tsira koda kuwa ya nemi taimakekeniya da dan’uwansa mutum, domin mafi nisan abin da dan Adam yake mallaka shi ne taimakekeniya don fahimtar gaskiya da hakika a iyakar fagen hankali da mariskai, alhalin wadannan fagage biyu ba su isa ba ga riskar hakikanin gaskiya da zata kai ga kamala.

Saboda haka ne hannun gaibi (Taimakon Ubangiji) ya miko domin toshe bukatar mutum wacce take ita ce mafi girman bukatarsa, sai mutum na farko ya zama dan aike daga Allah kuma mai shiryarwa zuwa ga tafarki madaidaici. Aikin annabawa ga mutane shi ne bayanin ilmi, da kyawawan dabi’u, da sanin gaskiya da zata kai ga kamala da tarbiyya mai kyau, da kuma bayanin ilmi da dan Adam zai iya fahimta, da kuma bukatuwarsa zuwa gareshi, sai dai shi ba ya iya kai wa ga hakikaninsu ta hanyar lalatacciyar tarbiyya, ko kuma mutum yana bukatar lokaci mai tsawo kafin ya kai ga gano su wadannan ilimomi, kamar sunnar Allah ta halakar da dan Adam sakamakon kaucewa gaskiya da kin ta, ko sunnar Allah a kan cewa abin da mutum ya zaba da sannu zai kai shi ga sa’ada da kamala, sai dai shi ne yake barin ta saboda karkatarsa zuwa ga duniya. Sai muhimmancin aiko Annabi ya bayyana a nan domin ya tunatar, ya yi gargadi. Ubangiji mai girma ya ce: “Ka tunatar domin kai mai tunatarwa ne kawai[8]”. Kamar yadda muhimmancin Annabi yake bayyana da wajabcin samar da shi da la’akari da cewa, shi yana misalta jagoranci ne na aiki na gari, domin shi mutum ne cikakke a ayyukansa da dabi’arsa da kuma sadaukarwarsa, wannan shi ne abin da ake cewa da shi muhimmancin tsarkake rai. Mai girma da daukaka yana cewa: “Yana tsarkake su yana sanar da su littafi da hikima”[9].

Idan hadafin halittar mutum ya zama shi ne bauta ga Allah, ga shi kuwa a bisa dabi’arsa an sanya masa damfaruwa da wasilar da zata kai shi zuwa ga kamala, domin shi yana karkata zuwa ga kamala da sonsa na fidira, da muhimmancin annabta domin bayanin hanyoyin wannan shiriya, kuma da bayyana hakikanin gaskiya da takan kai zuwa ga wannan kamalar. Idan haka ne al’amarin yake to menene zai sa bukatar cigaban wannan hadafin da mikuwar wannan sako ya zamanto ta hanyar imamanci da Shi’a suke shardanta nassi a cikinta, da sauran sharudda kamar ilimi na baiwa daga Allah, da kuma isma? Amsa a kan wannan tambaya da waninta na daga tambayoyi yana tilasta mana tambayar kawukanmu kamar haka;

Menenne imamanci a mahangar addinin Allah?

Menene muhimmancinsa?

Bayan mun fita daga mahallin jayayya zai iya yiwuwa mu amsa wannan tambayoyi da suke zowa kwakwalwa game da imamanci da sharuddansa da suka hada da ilmi, da isma, da makamancinsu na daga sharudda na dole a same su ga imami.

Mahallin Sabani Tsakanin Mahanga Biyu

Imamanci da halifanci a makarantun Sunna suna da matsayi daya da suka fuskanta da yake bayar da karfi a kan cewa, imami kuma halifa bayan Manzo (S.A.W) yana nufin shugaba, kuma jagora na siyasa da yake tafiyar da sha’anin tsarin musulunci bayan wafatin Manzo (S.A.W). A kan wannan asasin babu wani dalili na sanya jagora ya zama yana dogara da nassi da ayyanawa ta fusakacin Allah da kuma bayanin Manzo, al’amarin an bar shi ne ga al’umma ta zabi wanda ta so ta ga ya cancanta ga tsayuwa da wannan al’amari na jagoranci, domin muhimmancin imami kuma halifa a nazarin wannan koyarwa, ba ya wuce aikin jagorancin siyasa da tafiyar da al’umma ta fuskacin haddodi, kuma yana daga abu na hankali a wannan hanya al’umma ta tsayar da halifa ya zama ta hanyar shawara (shura), ko kuma ta hanyar wakilan al’umma, ko ta hanyar gado. Ya rage mu san menene sharuddan da suka wajaba ga halifa da aka zaba, haka nan zamu iya gani a wannan mahanga ta Ahlussunna suna ganin imamanci da halfanci bayan Manzo jagoranci ne na siyasa shi kenan, saboda haka ya isa ya zama wannan mutumin adali ne ta nahiyar aiki kamar yadda aka sani, kuma ba a shardanta masa ya zama yana da isma da ilimi da Allah ya ba shi ba, ya isa ya zama yana da iko da zai kai shi wannan matsayi a tsarin musulunci. Sakamakon ra’ayinsu game da imamanci da halifanci wani abu ne da bai wuce jagoranci na siyasa ba, kuma haka ya isa ya kasance ta hanyar zabe da shura, da kwace da karfi, da gado, ko wasiyya, kamar yadda yake a bayyane a aikace na ayyuka masu rikitarwa da suka faru bayan wafatin Manzo (S.A.W) da sharadin adalci, da ilimi daidai gwargwado. Saboda haka ne wasu suke tambayar larurar samuwar imami boyayye, ko kuma larurar ya zama ma’asumi, ko larurar ayyana shi da nassi daga manzon Allah (S.A.W).

Amma koyarwar Shi’a tana cewa ne, imamanci da halifanci bayan Manzo (S.A.W) abu ne mai girma na Ubangiji tamkar muhimmancin aiko da Manzo, kuma mai cigaba ce har karshen duniya, sai suka shardanta isma a cikinta hatta kafin balaga, hade da ilimi da yake daga Allah, da kuma nassi na shari’a ga imami. Saboda haka makarantar Sunna ba ta ganin wadannan sharudda da wata ma’ana da kima, kuma ba sa ganin sun dace da aikin da halifa zai yi, sharudda a nan gun mazhabin Ahlul Baiti (A.S) sun wuce na muhimmancin aikin siyasa kawai.

Wannan shi ne mataki na farko, kuma wajan sabani da yake fassara mana sabanin da ake da shi a fahimtar imamanci da kuma kokwanto a mas’alar isma, ko kuma dalili na wajabcin samuwar nassi. Wannan shi ne ya sanya wasu suka yi bincike game asalin nazarin samun nassi domin su kai ga natija zuwa ga cewa; babu wani tarihin da ya nuna hakan a rayuwar imamai. Wannan batun da aka tayar game da imamanci da halifanci da nazarin nassi da kokwanto game da hakan, ya faru ne sakamkon fahimta da Ahlussunna suka yi wa imamanci. Sai dai magana ingantacciya ita ce; imamanci a Kur’ani da Sunna sun wuce wannan fahimta, kuma ta saba gaba daya daga asasinta daga irin wannan fahimta maras zurfi ta ma’anar imamanci da jagorancin al’umma bayan Annabi. Koyarwar Ahlul Baiti (A.S) tana kudurce cewa imamai goma sha biyu suna da muhimmiyar rawar da suka taka da ta lizimta sharudda masu zurfi mafi tsanani daga sharuddan jagoranci na siyasa[10].

Alaka Tsakanin Isma Da Nassi

Idan aikin imami shi ne makoma na addini, kuma aikinsa a shari’ance yana mikuwa zuwa ga sasanni masu yawa da ya hada da akida, da hukuncin shari’a, da kyawawan dabi’u, da jagoranci, kuma wajibi ne binsa da karba daga gareshi, saboda haka zantuttukan imami ma’asumi da ayyukansa, da abin da ya tabbatar duk hujja ne na shari’a da take hawa kan baligi a wajabci ko uzuri ga wanda bai sani ba daidai da hujjar ayyukan Manzo (S.A.W). Wannan aiki mai girma yana lizimtar abubuwa da yawa kamar haka; Imami ya zama ma’asumi kamar ismar Manzo, da wajabci a kansa na isar da sako kuma da aiki, wannan yana bayyana cewa isma da wannan ma’ana ba sharadi ba ce ga aikin jagoranci na siyasa kawai.

Muhimmancin aikin imamanci ya wajabta kasantuwar imami ya zama masani da dukkan abin da al’umma take bukata zuwa gareshi na rayuwarta da makomarta, kuma dole ya zama mafifici daga duk wanda yake bayan kasa a zamaninsa domin ya samu bayar da hakkin wannan aiki mai nauyi. Shi’a suna da imani cewa Manzo (S.A.W) ba shi da kansa ne ya ayyana halifa ba, sai dai al’amari ne da Allah ya umarce shi da shi, domin hadafin imamanci da kuma al’amarinta ya doru a kan al’amarin cikar sakon annabci da kuma cigaban shiriyar Ubangiji a kan layi daya. Hikimar Allah ta sanya cigaban isar da sakon Allah ya zama ta hanyar ayyana imami ma’asumi ne, imami shi ne wanda ya lamunce samar da maslaha ta tilas ga al’ummar musulmi bayan Manzo (S.A.W).

Ashe kenan matsayin imamanci na akida ba kamar fikihu ba ne na daga hukuncin rassa, wannan shi ne abin da ya sanya imamanci ya zama yana da wadannan sharudda masu fadi masu girma, kuma ya wuce matsayin jagoranci na siyasa kawai. Idan muhimmancin imamanci yana da fadin da ya wuce jagorancin siyasa to dole ne ya zama yana da sharadi da zai tilasta gaskatawa da shi a matsayin wani asasi na addini kai tsaye, saboda abin da yake mai girma na sakon da yake dauke da shi. Shahidus sani a risalarsa: Asasi na hudu shi ne gaskatawa da imamancin imamai sha biyu (A.S), wannan asasi jama’ar imamiyya su na la’akari da shi wajan tabbatar imani, har ma ya zama wani larura daga larurai na mazhabarsu sabanin wasunsu na daga masu saba musu, su sun dauki wannan a matsayin furu’a ne[11].

Saboda haka ne zamu samu cewa, al’amarin ayyana imamai yana wajen hakkin dan Adam ne, kuma ba zai iya zabar wanda yake da isma ba, ko kuma ya gano wanda yake da ilmi na baiwa daga Allah da sauran siffofin da imamai (A.S) suke dauke da su. Rashin kasanewar zabin imamai ta hanyar dan Adam ya yi kama da zabin annabawa da Allah yake zabar wanda ya so, kuma a gane hakan ta hanyar wahayi da nassi. Bambanci tsakanin Annabi da imami shi ne, Allah yana nuna Annabi ta hanyar mu’ujiza da wahayi, imamai kuma ta hanyar mu’ujiza da nassi.

Sharif Murtada yana fadi a risalarsa cikin abin da yake wajibi a kudurce shi game da annabta: Duk sadda Allah madaukaki ya san akwai maslaha a cikin wasu daga ayyukanmu da tausasawarsa, ko kuma akwai fasadi da barna na addini a ciki, kuma hankali ba ya iya gano ta, wajibi ne ya aiko Annabi domin ya sanar da wannan ga mutane, kuma babu wata hanyar gano shi sai da mu’ujiza. Mu’ujiza kuma dole ta kasance ta saba wa al’ada, kuma ta yi daidai da da’awar Manzo din da abin da ya shafi da’awarsa, ta kuma kasance ba za a iya zuwa da ita ba ta bangaren wani mutum, kuma aikin ya zama ya yi daidai da yadda Allah (S.W.T) ya gudanar da shi, idan wannan duk ya faru to wajibi ne a gaskata shi, in ba haka ba to sai rashin gaskata shi ya zamanto ya munana. Daga abin da ya zo a babin abin da ya wajaba a kudurce shi a imamanci da kuma abin da ya biyo bayansa, ya wajabta kasancewar imami ya zama ma’asumi, domin da bai zama hakan ba, da bukatuwa a gareshi ba ta kare ba, wannan kuma yana tukewa zuwa ga samar da shugaba ma’asumi, kuma wajibi ne ya zama mafificin al’umarsa, mafi saninta, saboda munin gabatar da wanda aka fi a kan wanda ya fi shi a hankalce, Idan ya wajaba ya zama ma’asumi to wajibi ne a samu nassi daga Allah a kan hakan, kuma zabar imamanci ta bangaren mutane ya kawu kenan, domin babu wata hanya da mutane zasu iya sanin mai isma[12]. Don haka ne zamu samu nassi da yake daya daga rukunan isma a mahangar Shi’a da yake nuna ajiya ta Ubangiji da take tattare da wannan imami, daga nan ne zamu sami cewa nassi shi ne mai kai wa ga sanin halifa mai bin Manzo (S.A.W) a wannan aiki na addini da ci gabansa.

Nazarin Nassi Da Shura

Idan mahangar musulunci ga halifanci bayan mazo (S.A.W) ta lizimta samuwar nassi da wannan nazari yake gani bayan wucewar Manzo mai tsira da aminci, wanda ya wuce maganar jagoranci na siyasa, ashe kenan menene matsayin musulunci game da shura da wasu mutane suka lizimce ta a matsayin nazari ga shugabancin al’umma maimakon nassi? Kuma menene alakar shura da tabbatar da immanci da ake da nassi game da shi? Zamu bi wannan mas’ala ta fuskacin tarihi da farko, sannan sai mu bujuro da nassi kan halifancin Annabi (S.A.W), bayan haka sai mu yi bincike game da dokokin shura da kuma alakarta da shugabanci da aka yi nassi da shi, domin mu kai ga natija zuwa ga cewa shura ba kawai nazari ne na hukuncin musulunci ba, sai dai wani abu ne na fakewa da shi da ake amfani da shi wajan nuna wadatuwa ga barin shari’ar musulunci, da daukar wata hanya da ta saba mata da take fitar da dokoki da ba su yi daidai da abin da ma’asumi yake a kai ba. Kuma shura ba wani abu ba ne a musulunci sai hanya ce da aka samu domin gyara abin da ya faru na kuskure a tarihin musulunci, da kuma neman ba shi mazauni a cikin shari’ar musulunci, wato ana iya cewa hanya ce ta halatta kuskure da gyara shi, da ba shi mafita da uzuri, ba nazari ba ce da shari’a ta zo da ita ba.

Na Farko: Ta Fuskacin Tarihi

Sanannen abu shi ne musulunci bai bar al’umma haka nan babu fikira game da hukunci ba, domin al’amarin addini da duniya gaba daya ba ya cika sai da samuwar shugaba da zai jagoranci al’umma, yana shiryar da ita, yana jagorantarta ga abin da yake gyara ga rayuwar al’umma da makomarta. Saboda haka suka ce: Musulunci ya bar al’umma ta zaba wa kanta hanyar hukunci da kuma abin da take gani shi ne mafi maslaha ga kiyaye tsarinta da kuma kare shari’a, wannan kuwa ba yana nufin ya bar ta haka nan ba. Saboda haka wani ra’ayi ya bayyana a tarihin musulunci yana mai jingina al’amarin hukunci da jagoranci daidai da abin da ya faru a tarihi a lokacin sahabbai.

Ahlussunna suna ganin wannan mas’ala mai girma addini ya gafala ga barin ta a Kur’ani da Sunna, ya kuma dora nauyin yin hakan a kan al’umma da su zabi yadda suka so. Idan kuwa haka ne, muna iya tambaya cewa: Shin akwai wata ka’ida ayyananniya da al’umma zata iya dogara da ita wajan ayyana halifa? kuma yaya matsayinta yake a shari’a? Amsa: Sai suka ce: Akwai fuska uku ta ayyana halifa:

Ta farko: Zabin shugabannin al’umma da ayyana jagoranta, wannan kuma ana cewa da shi tsarin shura. Sai dai tsarin shura bai dauki salo daya ba gun sahabbai, saboda haka sai suka samu sabani suka ce shura kala biyu ce:

A-Tsarin shura na farko kamar yadda ya faru a bai’ar Abubakar da Ali dan Abi Dalib.

B-Tsarin shura ta hanyar ayyana wasu adadi da halifan da ya rigaya ya yi, kamar yadda Umar ya yi.

Ta biyu: Wasiyya: Ita ce halifa kafin ya mutu ya sanya wanda zai maye gurbinsa, kuma wannan ma ya dauki salo daban-daban har guda uku:

A- Ya sanya halifa daya kamar yadda Abubakar ya yi a lokacinsa ga Umar.

B- Ya sanya wasu jama’a da dayansu zai zama halifa kamar yadda Umar ya yi tsakanin mutane shida da zasu zabi halifa tsakaninsu.

C- Ya sanya halifanci ga mutane biyu ko sama da haka ya kuma sanya ta mai bin juna kamar ya ce: Halifa bayana shi ne wane, idan ya mutu sai wane. A wannan tsari halifanci yana zama a jere kamar yadda ya tsara shi, kamar yadda Sulaiman dan Abdulmalik ya yi ga Umar dan Abdul’Aziz, sannan Yazid dan Abdulmalik bayansa, haka nan Haruna ya sanya ta ga ‘ya’yansa uku.

Ta uku: Sa karfi, da mamaya, da kwace, da galaba da takobi: Ahmad dan Hanbal ya ce: Imamanci na wanda ya yi nasara ne[13].

A zahiri wannan nazarori gaba dayansu neman gyara kurakuran da wannan al’umma ta yi ne, domin wannan ba shi da wata madogara ko mahanga ta shari’a. Kawai wannan domin gyara abin da ya faru ne a tarihi da kuma neman ba shi halacci na shari’a da kuma neman kare kurakuran magabata na farko daga tuhumarsu daga wannan aiki mai hadari da suka gabatar ba tare da wani dalili na shari’a ba, da kuma neman wanke su daga munanan sakamakon abin da wadannan ayyuka na su suka haifar a sakamakon haka. Saboda haka ne ma kallafawa kai bayani da nema musu uzuri ya bayyana a wannan nazari kamar yadda yake a fili, wannan kuma saboda:

1- Kowanne daga wadannan hanyoyi uku babu wani dalili na shari’a da ya dogara da shi gaba daya, hatta da malamai daga sahabbai ba su san shi ba a bisa hakika.

2- Asalin shura da aka fada a fuska ta farko wanda aka samu daga bai’ar da aka yi wa Abubakar bai faru ba a bai’arsa, kuma ba wanda ya taba da’awar hakan, har ma Umar ya ambace ta da cewa ita bai’ar kuskure ce ba tare da shawara ba, Sai dai wadanda suka zo daga baya sun ba da surar shura domin su ba ta sabon tufafi na shari’a a zabar halifa na farko, wasu ma sun so su ba ta siffa na ijma’i[14].

3- Tsoron faruwar fitina ya zama uzuri da aka zaba wajan wanke farkon bai’ar da aka yi ga halifa na farko yayin da wannan ya faru ba tare da shawara ba, ba a kuma saurari manyan sahabbai ba daga Muhajirun da Ansar wadanda ya kamata su tsinkayi wannan uzurin da aka bayar na gaggautawa domin tsoron sabani da fitina ba, wannan kuwa ya bayyana a nassin hadubar Umar.

Sai dai abin mamaki! Sai ga fitina din ta zo ta dawo hanyar shari’a da ake amfani da ita wajan zaban halifa kamar yadda muka yi bayani a hanya ta uku, ta yadda ake ganin hatta da sa karfi da mamaya da rinjaye da takobi hanyoyi ne na kai wa ga halifanci, kuma wanda ya yi galaba shi ne halifa na shari’a kuma wajibi ne a bi, kuma wannan hanya budaddiya ce ga duk wanda yake mai kwadayi. Ashe akwai wata fitina da ta wuce wannan?!

Na Biyu: Nassin Halifanci Ya Zo Daga Manzo

Farra’u a littafin Ahkamus suldaniyya yana cewa: Babu jayayya a kan tabbacin hakkin halifa a kan wasiyya ga wanda zai maye gurbinsa, kuma babu kokwanto a kan zartuwar wannan wasiyya, domin imami shi ne ya fi cacanta ta da ita, zabinsa yana ga abin da ya zartar kuwa wannan ba ya dogara da ma’abota ra’ayi da fada aji na al’umma[15], wannan yana zama na halifa ne saboda tsoron faruwar fitina da kuma rashin zaman lafiyar al’umma[16] saboda haka wasu daga sahabbai suka rika koma wa Umar dan Khaddabi suna tambayarsa ya yi wasiyya ga wanda zai maye gurbinsa[17]. Ibn Hazam ya karfafi wannan ya ce: Mun samu cewa nada jagoranci yana inganta ta wasu fuskoki:

Na farko kuma mafi inganci mafifici shi ne shugaba mai mutuwa ya yi wasiyya zuwa ga wani mutum da yake zaba shugaba bayan mutuwarsa, shin ya yi hakan a lokacin lafiyarsa ko lokacin mutuwarsa ne, kamar yadda Manzo ya yi ga Abubakar, ko kuma Abubakar ya yi ga Umar, ko kuma Sulaiman dan Abdulmalik ga Umar dan Abdul’Aziz. Ya ce: Wannan fuska da muka zaba waninmu ya yi musunta, kuma mun zabe ta ne saboda abin da yake cikinta ne na cigaban saduwar jagoranci ba katsewa, da kuma tsaruwar al’amarin musulunci da ahlinsa, da kuma dauke abin da ake tsoro na sabani da rikici da ake zaton faruwarsa na daga rashin zaman lafiya, da kuma tsoron kada sirri ya yadu kuma kwadayin wasu ya tashi[18], Sai dai nassi da aka yi da’awrsa ga Abubakar daga Manzo bai tabbata ba, domin babu nassi ga Abubakar shi a kan kansa da cewa shi ne shugaba bayan Manzo (S.A.W), kai ba ma wanda ya taba cewa akwai shi, kai al’umma sun hadu a kan ma babu shi, domin duk wanda yake son ya tabbatar da nassi ga Abubakar to dole ya kore al’amarin da ya faru a Sakifa a dunkule da kuma a rarrabe, kuma ya karyata duk abin da ya zo a sihah na maganar Abubakar, da Umar, da Ali, da dan Abbas, da Zubair, game da halifanci. Saboda haka dole ya rusa dukkan abin da a zo na daga nazarin Ahlussunna game da Manzo (S.A.W) da imamanci, wannan nazari ba a gina shi a kan asasi daya, wato bai’a ga Abubakar ta wannan hanya da ta faru a Sakifa da kuma abin da ya biyo baya! Amma daga faruwar wannan abu ne nazarin shura ya samo asali tsakanin manyan al’umma, saboda haka babu wani ijma’i da ya tabbata, ijma’i a kan nassi game da Abubakar korarre ne[19]”. A nan ne Gazali ya kawo wata magana mai daidai da wannan ijma’i yana mai rushe maganar Ibn Hazam, Gazali yana fadi da alamar tambaya cewa: Don me ya sa ba ku ce nassi wajibi ne ya zo daga Annabi ko kuma daga halifa ba domin ku yanke cibiyar sabanin da ake yi? Sannan sai ya amsa da cewa: Da wasiyya ta kasance wajibi da Manzo (S.A.W) ya yi, alhalin bai yi wasiyya ba, Umar ma bai yi ba[20].

Yayin da Ibn Hazam ya ci gaba da kawo nazarinsa sai ga shi yana kore asalin nazarin shura da kuma kore maganar hakkin zabar shugaba ta hannun manyan al’umma, yana mai dogaro da zabar halifa ta hanyar nassi! Saboda ya nutsu da wajabcin nassi, sai dai shi yana nufin nassin da ya yi daidai da abin da ya faru, koda yake babu wani dalili a kan hakan. Hakika nassi bai saba da asalin nazarin shura ba har abada, shura a nan ba al’amari ne da ba shi da abin da ya kebance shi da wani yanayi ba, kuma dattijan al’umma ba su da hakkin su zabi wanda suka so haka nan kawai ba wani dalili, domin shura tana da iyaka, wannan kuma iyakar nassi ne ya zana mata ita. Suka ce: Daga sharadin shugaba ya kasance bakuraishe, imamanci ba zai yiwu ba sai da shi, suna masu kafa dalili da nassi tabbatacce a kan haka, hakika ya tabbata daga Annabi (S.A.W) ya ce: “Imamai daga Kuraish ne”. A wata ruwaya yana cewa: “Ku gabatar da Kuraish kada ku shiga gabanta” tare da samun wadannan nassosi da kowa ya sallama a kansu babu wata shubuha ta mai jayayya[21], ko zancen mai sabawa da za a yi la’akari da shi. Suka kuma shardanta wa wannan bakuraishe ya zama na ainihi daga kabilar Bani nadar dan Kinanata, domin ya yi daidai da nassi[22].

Ahmad dan Hanbal ya ce: “Ba yadda za a yi wani daga wanin kuraishawa ya zama halifa[23]”. Yana mai kafa dalili da wannan hadisi da tawaturinsa, da kuma fasawar da Ansar suka yi suna masu mika wuya ga muhajirai kuraishawa yayin da suka kafa musu dalili da wannan hadisi a Sakifa[24]. Ibn Khaldon ya ce: Jamhur sun tafi a kan sharadin kuraishanci da kuma ingantuwar halifanci ga bakuraishe koda kuwa ba zai iya daukar nauyin aikin tafiyar da al’amuran musulmi ba[25]. Haka nan nassin shari’a ya tabbatar da tawaturin magana a kan ingancinsa kuma ijma’i a kansa ya tabbata. Abu ne bayyananne cewa wannan ya faru ne yayin da nasara ta tabbata ga nassi a kan asasin shura, yayin da halifa na biyu ya ga wajabcin samuwar nassi a kan wanda zai maye gurbinsa. Sai wannan nassi ya zama ya hade da tsarin siyasa, duk da yana jefar da ka’idar shura gaba daya. Hada da cewa nassin hadisin Annabi mai daraja da daukaka yana cewa: “Shugabanni daga kuraishawa ne” yana mai rushe tunanin shura gaba daya! Sai ya zama wanda ya yi galaba a kan al’umma ya kuma kwace halifanci da takobinsa ya zama bakuraishe halifancinsa ya inganta domin bai fita daga nassin da ya gabata ba. Haka nan ba a la’akari da sharuddan wajibi da suke dole a same su ga halifa kamar ijtihadi, da adalci, da takawa, domin idan halifa ya zama bakuraishe to halifancin sa ya inganta koda kuwa ya zama mai rauni ko azzalumi. Ashe kenan al’amarin shura ya kamata ya zama ya fita daga wajen nassi, kuma ba zai yiwu a zabi wani ba sai bakuraishe na asali.

A takaice wannan mas’ala tana tabbatar mana da samuwar nassi ingantacce a wannan nazari ta wannan hadisi: “Shugabanni daga kuraishi ne” hakika Buhari da Muslim da ma’abota Sunnan da Siyar sun rawaito da lafazi mabanbanta, sai dai wannan nassi yana bukatar abin da zai kebance shi saboda wasu dalilai:

1-Nassin da ya gabata “Shugabanni daga kuraish ne”, shi kadai ba ya iya tabbatar da hadafin da ake nema na tabbatar da shugabanci, wannan ya kasance domin kare addini da al’umma, ta yadda sahabbai da kansu sun fahimci wannan al’amari tun karewar zamanin halifanci na gari. A cikin sahihul Buhari ya zo cewa: Yayin da aka yi jayayya tsakanin Marwan dan Hakam yana Sham, da Abdullahi dan Zubair yana Makka, sai wasu jama’a suka tafi wajen sahabi Abi barzatal aslami suka ce: Ya Aba barza! ba ka ganin abin da mutane suka fada cikinsa? Sai ya ce: Ina neman ladan Allah domin na wayi gari ina mai fushi da kuraishawa, domin wanda yake a Sham wallahi ba yana yaki ba ne sai domin duniya, wanda yake yaki a Makka ba yana yaki ba ne sai domin duniya[26].

2-Akwai wasu nassosi ingantattu da suka kebance hadisin da ya gabata, kamar haka: Hakika Annabi ya tsoratar a kan alfahari da nasaba ta kuraish, ya kuma yi gargadin cewa wannan al’umma zata halaka, kuma al’amarinta zai daidaice. Ya zo a cikin Sahilul Buhari, daga gare shi (S.A.W) ya ce: “Halakar wannan al’umma zata kasance a hannun wasu samari na kuraishawa ne”[27]. Yaya kenan za a iya hada wannan nassosi guda biyu mai cewa: “Shugabanni daga kuraish ne” da kuma “Halakar wannan al’umman zata kasance a hannun wasu samari na kuraishawa ne”. Ba makawa a kebance wannan hadisin da abin da ya zo na hadisai game da kuraishawa, wannan kuma kebancewar iri biyu ce:

A-Ta korewa: Akwai hadisai da suka toge wasu mutane daga kuraishawa kuma suka nisantar da su daga fagen girmamawa.

Ibn Hajar Alhaisami a wani hadisi mai sanadi ingantacce cewa Manzon Allah (S.A.W) ya ce: “Mafi sharrin kabilun larabawa: Banu Umayya, da Banu Hanifa, da Sakif”. Ya ce: A wani hadisi ingantace Hakim ya ce: A bisa sharadin shaihaini daga Abi Barzata ya ce: “Mafi kin jama’a ko mutane a wajan manzon Allah su ne Banu Umayya[28]”. Abin da ya zo game da sukan alayen Hakam baban Marwan yana da yawa kuma mash’huri ne, shin ya inganta shugabancin al’umma ya dogara da mafi sharrin kabilun larabawa wanda sune ma fi kin mutane a wajan manzon Allah (S.A.W)! Idan wadannan suka zama masu hukunci a sarari to dole mu shaida da cewa lallai al’umma ta halaka ta karkace ga barin gaskiya, kuma kamata ya yi al’umma ta dawo zuwa ga bin shiriyar manzon Allah (S.A.W) da nassin da ya kawo daga Allah na wasiyyarsa da Ahlin gidansa (A.S) maimakon ta koma tana neman samar wa abin da ya faru mafita da kuma tawilinsa da nassi.

B-Ta tabbatarwa:

Hadisin da yazo yana mai nuna fifikon kuraishawa da zabi a kan sauran kabilu bai tsaya ga nuna da’irai kuraishawa ba kawai, sai dai ya kebance wannan da cewa wasu jama’a daga cikinsu ake nufi sai ya ce: “Allah ya zabi Kinana daga ‘ya’yan Isma’il, ya zabi Kuraish daga Kinana, ya zabi Bani Hashim daga Kuraish, ya zabe ni daga Bani Hashim”[29]. Wannan fifita wa da daukaka ga Bani Hashim a kan sauran kuraish ne.

Ibn Taimiyya yana mai karin bayani game da wannan hadisi yana mai cewa: “Ya zo a cikin Sunna cewa; Abbas ya kai karar wasu kuraishawa da suke wulakanta shi, sai Manzo (S.A.W) ya ce: Na rantse da wanda raina take ga hannunsa! Ba wanda zai shiga aljanna sai ya so ku don Allah da kuma kusancina”. Idan sun kasance su ne mafifitan halitta to ba makawa ayyukansu su ne mafifita ayyuka, mafificinsu shi ne mafificin kowane mafifici na sauran kabilun kuraishawa da larabawa, har da Bani Isra’il da waninsu[30]. Matsayi a nan ba matsayi ne na fifita wa ba shi ke nan, sai dai abin nufi kuraish imaninta ba ya inganta sai ta so su Bani Hashim so biyu; Saboda Allah da kuma domin kusanci da Manzo (S.A.W).

Shin ya inganta kuraish gaba dayanta ta zama daidai a wajan gabtarwa a shugabanci da imamanci, kuma akwai Banu Hashim da nassi ya daukaka su zuwa mafi daukakar matsayi, da akwai kuma Banu Umayya da nassi ya kaskantar da su zuwa mafi kaskancin martaba?! Idan abin da ya wakana ya kai mu zuwa ga wannan halin, to shi kenan sai mu shaida da cewa abin da ya faru kauce wa daga hanya ta gari ne, ba mu yi kokarin gyara shi ba.

A takaice yana iya bayyana a fili cewa, a nan mu mun yi duba sosai don gane da abin da ya shafi bahasin maudu’in imamanci, sai muka ga cewa dalilin da ya sa aka samu wannan cece-kuce dangane da wadannan sabani da ake ta fama da su shi ne, bin wannan al’amari da ya faru, da kuma kokarin gyara shi da kuma sanya shi doka da madogara na asasi a tsarin siyasa da tafiyar da shugabancin al’umma har ya zama doka. Maganganu masu rusa juna da ake samu a lokuta daban-daban sun bayyana a zahiri a wadannan ra’ayoyi, abin da ya sa suka rasa kimarsu a matsayinsu na nazarin musulunci da zai iya warware daya daga manyan al’amuran musulunci masu girma.

Sai ga magana game da nassi na shari’a ba ta tsaya ga shi nassin ba, ba ta kuma lizimtu da aiwatar da sharuddansa ba da iyakokinsa. Shura kuma an nuna cewa abu ne rusasshe da aikin da halifa da ya gabata ya yi na nassi ga mai bi masa, da kuma ra’ayin shura da ra’ayin kwace da rinjaye da karfi da kuma sa karfin takobi. Amma mahangar tsarin shawarar manyan gari (shura) shi ya fi kowanne daga wadannan mahangai shiga duhu. Wani lokaci sai ta zama hannun mutum daya da zai kafa kansa halifa mutum biyu su bi shi kamar yadda ake daura aure, ko mutum hudu su bi shi, ko kuma su zama shida da halifa da ya rigaya zai ayyana ba tare da al’umma tana so ba, kai har abin ya wuce hakan, kai har malami kamar Ibn Khaldon ya sanya makusantan sarki da na gefensa -komai kuwa rashin takawarsu da iliminsu - a matsayin ma’abota kulla shugabanci da warwarewa wadanda irinsu ne suka sabawa halifa Ma’amun kan sanya halifanci zuwa ga Ali Arrida (A.S) bayansa[31].

Wannan al’amari ya faru a rabi na biyu na halifancin Usman, ta yadda ya zamana an samu shugaban masu bayar da shawara wani ne daga makusantansa na Banu Umayya a kebance, wanda ba su da wani fifiko, da daukaka, da kokari, da rigo na addini, tare da yawan wadanda suke da wadannan dabi’u a wannan lokaci! Sai manyan shura suka zama su ne Abdullahi dan Amir, da Abdullah dan Sa’ad dan Abi Sarh[32], da Sa’id dan Asi, da Mu’awiya dan Abi Sufyan, da Marwan dan Hakam.

Dabari ya rawaito cewa Usman ya aikawa Mu’awiya da Abdullahi dan Sa’ad dan Abi Sarh, da Sa’id dan Asi, da Amru dan Asi, da Abdullahi dan Amir, sai ya tara su domin ya yi shawara kan al’amrinsa, sai ya ce da su: Kowane mutum yana da wazirai da masu ba shi nasiha, kuma ku ne waziraina masu ba ni nasiha kuma aminaina, kuma kuna ganin abin da mutane suka gani na in kawar da gwamnonina, in kuma mayar da dukkan abin da da suke ki zuwa ga abin da suke so, ku yi kokarin dubawa ku ba ni shawara. Yayin da suka ba shi shawara sai ya yi aiki da duk shawararsu; ya kuma mayar da su a kan ayyukansu, ya kuma umarce su da tsanantawa ta fuskacinsu, da kuma korar mutane kan iyakoki[33] da kuma hana su komawa wajan iyalansu, ya kuma yi niyyar hana su albashinsu domin su bi shi su bukace shi[34].

Wannan irin al’amura masu karo da juna mustahili ne a same su a nazari daya, ta yadda zai zama nazari mai dacewa da al’amuran tafiyar da sha’anin al’umma da yake da doka da ake iya fahimta. Kuma daidai gwargwadon kokawanto game da ingancin wannan nazari daidai yadda yake kai wa ga rinjayar da dogaro da ingancin nassin shari’a da ya zo daga Annabi (S.A.W) wajan ayyana halifansa. Wannan ita ce irin natijar da Dr. Ahmad Mahmudu Subhi ya cimma yana mai duba nazarin imamanci yayin da ya ce: “Amma ta nahiyar tunani Ahlussunna ba su kawo wani nazari mai karfi ba game da siyasa da zai iyakance ma’anar bai’a da shura da ma’abota nada shugabanci da warwarewa daga manyan al’umma, balle a samu wani abu mai iya bambance mana tsakanin mahanga da abin da ya faru a aikace a zahiri, ko tsakanin abin da yake na shari’a da kuma abin da ya gudana a tarihi a aikace.

Sai ga nazarin Ahlussunna a siyasa ya bayyana a wannan zamanin karshe bayan daula ta tsayu a kan wanda ya fi karfi ya yi mulki kamar yadda ya zo a mafi yawancin wannan ra’ayoyi sun zo ne domin raddi ga nazarin Shi’a mabiya Ahlul Baiti (A.S), Kuma wasu daga wadannan ra’ayoyi aka sanya su a matsayin dalilai na hukuncin shari’a saboda dogaro da usulubin da halifofi uku na farko suka yi shugabanci. Wannan kuma ci baya da faduwa da rashin makama tsakanin shari’a da kuma abin da ya faru game da halifanci ne, balle kuma ga maganganu masu karo da juna na wadannan ra’ayoyi da abin takaici daga karshe suka sanya su a cikin dokokin fitar da hukuncin shari’a. Ba komai ne hadafinsu na yin haka ba sai samar da wani ra’ayi mai kishiyantar mahangar Ahlul Bait (A.S) na samun tabbatar nassi a game da halifanci[35].

Na uku: Muhimmancin da shari’a ta bayar ga abin da shawara ta zartar da kuma alakarsa da halifancin da yake da nassi. Zamu ga mafi muhimmanci madogarar shari’a da wannan nazari na shura ya dogara da shi ita ce wannan aya mai girma ta: “Ka yi shawara da su kan al’amari”. Wannan aya tana lizimta wa shugaba wajabcin shawara a kan wani ra’aryi gun wadanda suke ganin ana magana da Manzo ne da umartarsa da yin shawara, kuma umarni yana nuna wajabci, wannan kuwa yana nuna wajabcin shawara da musulmi, kuma tunda ba za a iya shawartar dukkan musulmi ba gaba daya to wannan yana nuna shawara da ma’abota ra’ayi da tunani na wannan al’umma ne[36]. Da wannan ma’anar zamu iya tambaya cewa; Shin shawara tana nufin ana neman yin ta a kan kanta, ko kuma ita hanya ce da za a cimma wasu hadafofi da ita? Suka ce: Ba makawa shawara ba a nemanta a kan kanta kuma ba tana zaman kanta ba ne, ita shawara hanya ce ta tabbatar da wasu abubuwan da mafi muhimmancinsu sanin ra’ayin wasu da kuma tunaninsu da tattaunawa, Domin idan tunani ya zo daga mahanga daban-daban aka tara shi waje daya sai ya sami kima mai girma wajan sanin makamar siyasa, da hukunci, da kuma tafiyar da al’amura, da tattalin arziki, da aminci, da yaki, a wannan kasa, wannan kuwa yana tabbata ba tare da ma’asumi ba daga ma’abota shugabanci.

A nan hadafin sanya shawara zai bayyana, sai dai menene matsayin shura a shari’a? Kuma shin natijar da za a samu ta hanyar shawara da ijma’i ra’ayin duka ake bukata ko kuma ra’ayin mafi yawa za a dauka? Kuma shin ya zama dole ga shugaba ya yi riko da wannan ko kuwa?. Malaman Ahlussunna suna bayar da amsa kala biyu ne a kan hakan:

Na farko: Masu ganin sakamakon shawara ya zama dole ne ga shugaba ya yi riko da shi. Daga cikin wadannan akwai Muhammad Abduh da yake fada a bayanin ma’anar Ulul’amri da yake cewa: Ulul’amri su ne masu shugabantar al’umma a hukunci, kuma wannan su ne aka yi nuni da su a fadin Allah madaukaki: “Al’amarinsu shawara ne tsakaninsu” ba kuma zai yiwu ba shawara ta samu tsakanin dukkan al’umma, don haka ya zama dole a samu wasu jam’a masu wakiltar al’umma, da ba kowa ne ba su sai ma’abota girma da daukaka na wannan al’umma da aka yawaita ambatonsu, yana mai karawa da cewa: Wajibi ne a kan shugabanni su yi hukunci da abin da manyan al’umma suka zartar”[37].

Na biyu: Ra’ayin da yake ganin shawara a matsayin fuskantarwa kawai, babu wani kima da take da shi na shari’a a wajan tilasta shugaba ya yi riko da ita wajan zartar da abin aka hadu a kansa, ko kuma abin da mafi yawa suka tafi a kai.

Daga cikin wadannan akwai Kurdabi, yayin da yake cewa a tafsirinsa “Shawara ta ginu ne a kan sabanin ra’ayoyi, mai shawara yana duba wadannan sabani ne, ya kuma duba wanda ya fi kusa da littafi da sunna in zai yiwu, idan Allah ya shiryar da shi zuwa ga abin da ya so sai ya yi niyyar aiki a kansa ya kuma zartar yana mai dogara gareshi”[38].

Amma malaman Shi'a sun tafi a kan ra’ayi na biyu a tafsirin ayar shura, Muhammad Jawad Balagi yana cewa: “Ka shawarce su a kan al’amari” ai ka nemi gyaransu, da kuma karkato zukatansu da shawara, ba wai domin zasu sanar da kai ilimin daidai ba ko sanar da kai ingantaccen ra’ayi ba, yaya kuwa zasu iya hakan alhali Allah (S.W.T) yana cewa: “Ba ya magana ta son rai, shi (al’amarin) ba komai ba ne face dai wahayi ne da aka yi” saboda haka idan ka yi niyya a kan abin da Allah ya umarce ka da hasken annabta ya kuma datar da kai a cikinsa sai ka aikata kana mai “ka dogara ga Allah”[39].

Shura a nazarin koyarwar Ahlul Baiti (A.S) tana nuna cewa ra’ayin musulmi ba ya lizimtar Annabi (S.A.W) yayin da madaukaki yake cewa: “Idan ka yi niyyar aiwatarwa sai ka dogara ga Allah”. Ashe kenan tsayuwa da aiki yana zama a bisa asasin niyyar Manzo (S.A.W) ba bisa abin da muminai suka yarda ba. Sannan shawararsa (S.A.W) ta kasance domin gane ra’ayin musulmi ne ga yadda za a zartar da hukunce-hukuncen musulunci, ita shawarar ba a matsayin fitar da hukuncin shari’a take ba, hada da cewa Ubangiji madaukaki ya ce: “Bai kamata ba ga mumini ko mimina idan Allah ya hukunta wani al’amari ya zama suna da zabi a al’amarinsu, duk wanda ya saba wa Allah da manzonsa hakika ya bace bata bayyananne”[40],

Ashe kenan rinjayar da shawara yana takaita da wajan da Allah da manzonsa ba su yi wani hukunci ba ne, amma abin da suka yi hukunci a ciki, shawara a nan sabo ce ga Allah da manzonsa da kuma bata bayyananne[41].

Saboda haka shura tana da kima ne idan ta amfana wajan daukar dokokin zartarwa na musulunci a dukkan fagagen rayuwa da makamancinta, kuma ba ta zama dole ga imami ma’asumi ba, domin ita ba ta iya shar’anta hukunci sabanin magana da zance da tabbatarwar ma’sumi, tana kebanta ne da wajan da Allah da manzonsa ba su da hukunci.

Amma ta bangaren tarihi kamar yadda muka ambata shura ba ta zama wani tsari na siyasa na shari’a na hukunci ba, domin an kirkiri ra’ayinta ne domin gyara barna da kuskure na tarihi da kuma sanya wannan a matsayin madogarar asasi ta tarihi a tsarin shugabanci na wannan lokaci, kuma mu sani halifanci ba ya tabbata sai da nassi daga Annabi ga halifan da zai zo bayansa.