• Farawa
  • Na Baya
  • 25 /
  • Na Gaba
  • Karewa
  •  
  • Gurzawa HTML
  • Gurzawa Word
  • Gurzawa PDF
  • Budawa: 4239 / Gurzawa: 2160
Girma Girma Girma
Imamanci Da Nassi

Imamanci Da Nassi

Mawallafi:
Hausa

Alaka Tsakanin Bai’a Da Nassi

Bai’a girmamawa ce ga mutum domin ya zabi makomarsa a cikin kira zuwa ga Allah da jihadi a tafarkinsa ko sha’anin hukunci da siyasa. A bisa dabi’a muslunci ba ya son rayuwar musulmi ta kasance ba tare da nufinsu ba da kuma yardarsu ba. Biyayya a nan ita ce mafi muhimmnaci a cikin zartar da ayyukan isar da sako da kira, da kuma ayyukan kasa, da jihadi, da karfafa wa ga bin imamai ma’asumai ta hanyar bai’a. Amma wannan ba yana nufin biyayya ga imami ma’asumi tana saraya ba ne idan ba a yi masa bai’a ba.

Idan bai’a ta kasance to tana karfafa imami da biyayya gareshi ne bayan an tabbatar da samuwarsa. Shin zai iya yiwuwa garemu mu ce: Bai’a sharadi ce ta inagancin biyayya ga imam, ko kuma sharadi ce ta wajabcin biyayya gareshi ta yadda zai zama idan babu bai’a ba shi da imamanci, ko kuma babu inganci ga binsa? Sai mu ce: Bai’a tana karfafa dankon wajabcin lizimtar wilayarsa da biyayya ga jagoracinsa ne, ba tana kafa ko samar da assassin asalin wilayar ba ne ko kuma ta zama sharadi na inagncin biyayya gareshi, domin biyayya da imamanci ba sun tsayu ba ne a kan bai’a ga wanda wilaya ta tabbata gareshi da nassi. Shi ya sa zamu samu cewa, Manzo (S.A.W) ya yi aiki da bai’a a lokacin rayuwarsa kamar yadda yake a fili a bai’ar Akaba ta farko, da bai’ar Akaba ta biyu, da bai’ar Gadir.

Wannan sura ta bai’a da ta faru ga Manzo (S.A.W) tare da cewa wilaya ta tabbata gareshi tun kafin wannan bai’a din. Bai’ar da musulmi sukan yi masa ko rashin bai’ar su gareshi (S.A.W) a game da amsa kiransa ko jihadi ko shugabanci, ba ya canza hakkin Manzo a kan al’umma na biyayya ga al’amarin kira da jihadi da jagoranci.

Haka nan shugabancin imam Ali (A.S) bayan Manzo (S.A.W) da ya tabbata a Gadir, Bai’ar da musulmi suka yi masa a rannan ba ita ce zata tabbatar masa da shugabanci ba ta fuskacin sharia’a duk da Manzo ne ya umarce su da su yi masa tun yana raye, ita wannan bai’ar ba ta kara kimar wilayarsa ta nahiyar shari’a a kan karfafa wilaya da biyayya, Kuma da dama daga malaman Ahlussunna sun tafi a kan kasancewar jagoranci yana samuwa ne ta hanyar wasiyya. Suka ce: Idan wani halifa ya yi wasiyya zuwa ga wani bayansa to bai’ar sa ta kullu domin yardar al’umma da ita ba a la’akari da ita, dalilin haka shi ne bai’ar Abubakar ga Umar ba ta tsayu a kan yardar sahabbai ba[42]. Wannan kenan, tare da cewa ba mu samu bai’a ba tsakanin Abubakar da Umar, abin da ya faru kawai ya yi wasiyya da halifanci ne kawai ba wani abu ba.

Idan haka ne wanda Annabi ya yi wasiyya gareshi shi ya fi cancanta a bi ba tare da wani dalili ba a kan sabawa hakan, kuma al’amarinsa zartacce ne, kuma da wannan ne halifanci ya tabbata ga Ali bayan Manzo kai tsaye, shin al’umma ta yi masa bai’a a kan biyayya ko ba ta yi ba. Bai’a tana kasancewa ne daga alkawarin biyayya da karbar tafiyar da hukunci da tafiyar da al’amuran al’umma, wannan kuwa ba ya yiwuwa sai da bai’a, kuma Abbas ya halartowa Ali da ita sai ya ki karba sai dai a fili a gaban mutane a masallacin Annabi. Sannan da aka zo yin bai’a a kan hakan ne mutane suka yi masa bai’a, haka nan al’amarin ya kasance game da Imam Hasan (A.S), shi ya sa yayin da sauran imamai da Allah ya zabe su ga jagorancin al’umma ya zama ba a yi musu bai’a ba sai aka kange su gabarin tafiyar da hukuma da al’amuran al’umma, amma kuma wannan ba ya cire musu hakkinsu na imamanci, sha’anin al’amarinsu yana daidai da na annabawa ne da al’ummarsu suka saba musu suka hana su tafiyar da jagoranci da shiryarwa da fuskantarwa, ba tare da wannan ya cire musu matsayinsu da Allah ya ba su ba[43].

Ashe kenan matsayin bai’a a lokacin halartar imami ma’asumi ba komai ba ne sai karfafawa ga wanda jagoranci ya tabbata gareshi ta hanyar nassi. Kamar yadda bai’a ba ta iya samar da wilaya ga mutum da aka yi nassin binsa kamar Manzo ko imami, nassi ga imami yana wajabta binsa da haramcin rashin yi masa bai’a.

Manzon Allah Ya Yi Kokarin Karfafa Lamarin Nassi

Idan muka kula da nazari ta fuskancin tarihi muka kuma lura da matakan da Annabi ya dauka wajan tarbiyyar al’umma da wayar da ita game da al’amarin Ubangiji wanda ya shafi halifanci sai mu samu cewa ya karfafa nazarin nassi a kwakwalenmu ne ba shura ba, kuma ba a samu wani waje da Manzo ya ambaci wayar da al’umma da tarbiyyantar da ita a kan nazarin shura ba tun daga saukar fadin Allah madaukaki “Ka gargadi jama’arka makusanta”. Har zuwa saukar fadinsa madaukaki: “Ya kai wannna Manzo ka isar da abin da aka saukar maka daga ubangijinka, idan ba ka aikata ba to ba ka isar da sakonsa ba kuma Allah yana kare ka daga mutane”.

Hakika ya zo daga dan Abbas daga imam Ali (A.S) cewa ya ce: “Yayin da wannan aya ta sauka; “Ka gargadi jama’arka makusanta” ga manzon Allah (S.A.W) sai ya kira ni ya ce: Ya Ali Allah ya umarce ni da in gargadi jama’ata makusanta, sai na samu kunci na san cewa idan na bayyana wannan al’amari to zan ga abin ki daga garesu, sai na kame gabarinsa sai Jibril ya zo mini, ya ce: Ya Muhammad idan ba ka yi abin da Allah ya umarce ka to zai azabtar da kai, saboda haka ka yi mana abinci sa’i daya, ka kuma sanya karfatar akuya, ka cika mana kwano na nono, sannan ka kira duk Bani Abdulmudallib domin in yi musu magana in isar musu da sakon da aka umarce ni da shi, sai na aikata abin da ya umarce ni da shi, sannan na kira su, a wannan lokaci mutum arba’in ne da daya ko ba daya, a cikinsu akwai ammominsa abu Dalib, da Hamza, da Abbas, da Abu Lahab, Ya ce: Sai manzon Allah (S.A.W) ya yi magana ya ce: Ya Bani Abdulmudallib ni wallahi ban san wani saurayi a larabawa da ya zo wa mutanensa da mafifici daga abin da na zo muku da shi ba, ku sani ni na zo muku da alherin duniya da lahira, kuma hakika Ubangiji ya umarce ni da in kira ku zuwa gareshi, wanene a cikinku zai karfafe ni a kan wannan al’amari a kan ya kasance dan’uwana wasiyyina kuma halifata a cikinku?, Imam Ali ya ce: Sai duk mutanen suka tage gaba daya, sai na ce alhalin ni ne na fi kowa karancin shekaru a cikinsu, ni ne ya Annabin Allah zan zama mai taimakon ka a kansa. Sai ya riki kafadata sannan ya ce: Wannan shi ne dan’uwana kuma wasiyyina halifata a cikinku ku ji ku bi daga gareshi, Ali (A.S) ya ce: Sai mutanen suka tashi suna dariya suna cewa da Abi Dalib, ya umarce ka ka ji daga danka kuma ka bi shi”[1].

Haka nan Manzo Allah (S.A.W) ya fara shirya wa al’umma tun daga farawa da makusantansa yana mai nuna wa al’umma halifancin Ali (A.S) bayansa, yana mai wasiyya a kan dan’uwansa da wasiyya da halifanci da kuma wajabta biyayya gareshi, Annabi ya kasance yana mai bayyyana ma’anar ayoyin Kur’ani da suke sauka a kansa game da hakkin Ali musamman ayoyin da suka shafi halifanci da imamanci.

Zamakhshari a tafsirinsa yana fada game da fadin Allah (S.W.T): “Kawai shugabanku Allah ne da manzonsa da wadanda suka yi imani wadannan da suke tsayar da salla suke bayar da zakka alhalin suna masu ruku’i”[2], Wannan aya ta sauka game da imam Ali (A.S) yayin da wani ya tambaye shi yana mai ruku’u a cikin salla sai ya jefa masa zobensa[3].

Domin kawar da rikitarwa da kuma yanke duk wani tawili game da abin da ake nufi da kalmar wali da kuma nuna ko waye a wannan waje sai Annabi (S.A.W) ya bayyana a wajaje da dama cewa: “Ali daga gareni ne, ni ma daga gareshi nake, kuma shi ne shugaban duk wani mumini bayana”[4].

Saboda karfafa shuganbacin imam Ali (A.S) da kuma matsayinsa mai muhimmanci a wajan bayyana sakon musulunci da kuma cimma hadafofin ta hanyar aiwatar da jagoranci domin aiwatar da hukunce-hukunce, da kuma kare su daga dukkan abin da zai iya karkatar da su da kuma canja su bayan Manzo, sai Annabi (S.A.W) ya ce: “Ali daga gareni yake ni ma daga Ali nake, kuma ba mai bayar wa daga gareni sai ni ko Ali”[5].

Kuma Manzo (S.A.W) ya karfafa wannan ma’ana a aikace, a bayyane, da rana, a kissar isar da sako a surar bara’a, kuma Ahmad dan Hanbal ya fitar da wannan ruwaya a Masnadinsa daga Abubakar yayin da ya ce: “Annabi ya aika ni da bara’a zuwa mutanen Makka, sai ya tafi kwana uku sannan sai ya ce da Ali: Ka yi maza ka riske shi, sai Abubakar ya mayar da ita gareni na isar da ita, yayin da Abubakar ya zo wajan Manzo (S.A.W) sai ya ce: Ya manzon Allah shin wani abu ne ya faru game da ni?! Sai Manzo (S.A.W) ya ce: Ba komai game da kai sai alheri, sai dai ni an umarce ni da kada wani ya isar da sako daga gareni sai ni ko wani mutum daga gareni[6].

A littafin Kusshaf: Abubakar ya rawaito cewa: Yayin da yake kan hanya domin isar da surar bara’a sai Jibril (A.S) ya sauka ya ce: “Ya Muhammad kada wani ya isar da sakonka sai wani mutum daga gareka, sai ya aika Ali”[7].

Daga karshe Kur’ani ya cika wannan maudu’i mai muhimmanci wanda ya shafi haifar da tunani da tarbiyyantarwa a kan yadda al’amarin shugabanci da halifanci zai kasance bayan Manzo (S.A.W) a karshen abin da ya sauka garshi a ayar tablig sannan da kuma ayar cika addini bayan kissar Gadir mash’huriya ta yadda babu wani uzuri ga mai kawo uzuri, Kissar Gadir kissa ce da dayawa sun rawaito ta da dan sabani kadan a wasu wurare Kamar yadda zai zo: Yayin da Manzo (S.A.W) ya dawo daga hajjin bankwana, sai wahayi ya sauka a kansa yana mai tsananta masa: “Ya kai wannan Manzo ka isar da abin da aka saukar maka daga ubangijinka idan ba ka aikata ba to ba ka isar da sakonsa ba kuma Allah ne yake kare ka daga mutane”[8], sai ya tsayar da jama’a gun Gadir khum, ya tara mutane a tsakiyar rana, ga zafi mai tsanani, ya yi musu huduba yana mai cewa: “An kusa kira na sai in amsa kuma ni mai bar muku sakalaini ne, daya ya fi daya girma, littafin Allah da zuriyata. a ruwayar Muslim[9] da Ahlin gidana ku duba yadda zaku maye mini a cikinsu, domin su ba zasu rabu ba har sai sun riske ni a tafki”. Sannan sai ya ce: “Hakika Allah shugabana ne kuma ni shugaban duk wani mumini ne”. Sannan sai ya kama hannun Ali ya ce: “Duk wanda nake shugabansa to wannan shugabansa ne[10] ya Ubangiji ka so wanda ya so shi ka ki wanda ya ki shi, ka tozarta wanda ya tozarta shi, ka taimaki wanda ya taimake shi[11], ka juya gaskiya tare da shi duk inda ya juya”[12].

Kuma hakika saukar wahayi da wannan aya ya biyo bayan faruwar wannan abu mai girma da fadin Allah (S.W.T): “A yau ne na kammala muku addininku na kuma cika ni’imata a gareku na yardar muku da musulunci shi ne addini”[13], Wasu hadisai da aka rawaito daga Manzo suna cewa, bayan saukar wannan aya a wannan rana abar halarta wacce ita ce ranar sha takwas ga watan zil-hajji[14] ranar Gadir sai ya ce: “Allah mai girma! Godiya ta tabbata ga Allah a kan kammala addini da cika ni’ima da yardar Ubangiji da manzancina da kuma shugabancin Ali bayana”[15].

A ruwayar Ahmad: “sai Umar dan khaddabi ya gamu da shi –imam Ali- bayan nan, sai ya ce da shi: Farin ciki ya tabbata gareka ya dan Abu Dalib, ka wayi gari ka maraita shugaban dukkan mumini da mumina”[16]. Ba mu samu wani abu ba a rayuwar Manzo (S.A.W) da yake ambaton wani abu da zai iya tabbatar da cewa Manzo ya nufi tabbatar da al’amarin halifanci bayansa in banda nazarin wasiyya a matsayinta na sakon shari’a, ba a matsayin jagoranci na siyasa ba kawai, shi al’amari ne da yake Ubangiji ne da yake aiwatar da zabar abin da ya so na sakon manzancin Annabi (S.A.W) yayin da Kur’ani ya yi nassi a kan Annabi da cewar, idan bai isar da wannan al’amari na sakon halifanci da shugabanci bayansa ba, da bai isar da komai na sakon da ya dauki shekara ishirin yana wahala a kan isar da shi ba[17].

Abin da Ake Tsammani Da Abin da Ya Faru A Tarihi

Shahid Sadar (K.S) ya yi muhawarar wannan mas’alar da ta faru a tarihi da bayanai kamar haka; Tsammanin cewa Manzo (S.A.W) ya riki wata hanya ta barin mutane ba magaji ba halifa, da ma’anar cewa Manzo bai taba tarbiyyantar da mutane a kan al’amarin halifanci ba da jagoranci bayansa, wannan kuwa batacce ne domin ya yi karo da matasyin Annabi wanda yake sane da dukkan makomar sakon da ya zo da shi, sannan ya ci karo da hadisai da suka yi Magana game da muhimmancin al’amarin al’umma bayansa a rayuwarsa da kuma kafin wafatinsa a karshen rayuwarsa[18]. Kamar yaddda shahid Sadar ya soke ra’ayi na biyu wanda yake ganin shura da fadinsa: Abin da aka samu daga Manzo da muhajirai da Ansar ya kore batun shura. Domin da Annabi ya dangana al’amari zuwa ga hannun Muhajirun da Ansar bai taskace shi da Ahlin gidansa (A.S) ba, da wannan al’amari ya zama daga mafi bayyanar al’amura da kuma ya wayar da kan al’mmma a kan tsarin shura da bayaninsa dalla-dalla domin mutane su san yadda tsarinta yake. Da Annabi (S.A.W) ya wayar da su a kan haka, to da kuma an samu bayyanar wannan a cikin hadisansa da suke rawaitowa daga gareshi da take dauke da bayani game da shura. Amma sai ya zama ba mu samu wani wanda yake dauke da wannan tunani ba, sai ya zama al’ummar Muhajirun da Ansar duka mun same su ne jama’a guda biyu mabanbanta.

Na daya: Jama’ar da Ahlul Baiti suke jagoranta mai dauke da tunanin wasiyya da Manzo (S.A.W) ya yi game da halifancinsu.

Na biyu: jama’ar mutanen Sakifa da suke bin halifanci da ya biyo bayan wafatin Manzo (S.A.W).

Kuma a dukkaninsu ba wanda yake dauke da tunanin shura kamar yadda tarihi ya nuna, yayin da Abubakar ya yi wasiyya da halifancin Umar bai nemi shawarar kowa ba sai ya dora shi kan halifanci a kan al’umma ba tare da shawarar musulmi ba, ko shugabanninsu, sai Umar shi ma ya tafi a kan wannan tafarki ya zabi wasu wadanda zasu zabi wani daga cikinsu, ya kasance yana cewa: “Da Salim ya kasance rayayye da ban sanya ta shura ba”, wannan kuwa bayani ne karara daga gareshi da rashin imaninsa da shura[19]. Da Annabi ya dauki matakin ya sanya ta shura a tsakanin mutane da ya sanya wannan a da’awarsa tun farko domin ya sanar da wannan al’umma al’amarin sakon Allah da zai iya ba ta damar fuskantar duk wata matsala ta tunani da fikira da wannan kira zai iya fuskanta, yayin da ake samun karuwar budi da shigowar al’ummu jama’a daban-daban.

Sai ya zama ba mu samu komai ba dangane da wannan, kuma abin da aka sani daga sahabbai sun kasance suna jin nauyin fara tambayar Manzo (S.A.W), kai har ma sun bar rubuta sunnar Manzo (S.A.W) duk da kuwa ita ce madogara ta biyu ta shari’a bayan Kur’ani, tare da cewa rubutawa ita kawai ce hanyar da ta rage domin kiyaye ta. Kuma tarihi ya tabbatar da cewa ‘ya’yan Muhajirun da Ansar ba su da komai a hannunsu na daga abin da ya shafi ilimi game da mas’aloli masu yawa, sai ga shi hatta da kasar da ake ci yaki halifa ba shi da wani hukumci na shari’a game da ita a hannunsa da ya sani; ko a raba ta tsakanin mayaka? ko ta zama wakafi ga dukkan musulmi? Kai har ma sun yi sabani a kan yawan kabbarorin sallar mamaci, wasu suna cewa Manzo ya yi biyar, wasu suna cewa ya yi hudu ne.

Haka nan ya bayyyana a fili cewa Manzo bai kawo shura ba, sai ya zama ba abin da ya rage sai hanya ta uku wacce take cewa Manzo (S.A.W) ya shirya imam Ali da umarinin Allah ya kuma sanya shi halifansa a kan sako da al’umma bayansa a matsayinsa na mai masaniya da zurfin abin da wannan sako ya kunsa da kuma iko a kan kula da tafiyar sakon da cigabansa bayan Manzo (S.A.W), kamar yadda ya tabbata a tarihi a shekaru talatin da ya yi bayan wafatin Manzo (S.A.W) da furucin masu tarihi. Kuma duk abin da da ya zo na hadisai mutawatirai game da Ahlul Baiti (A.S) ba komai ba ne sai karfafa wa ga wannan hanya ta uku, wato ayyana halifansa da umarnin Allah[20].

Nassin Wasiyya A Hadisan Imam Ali Da Ahlul Baiti

Abu ne a fili ga wanda ya karanta tarihi cewa imam Ali shi ne wanda ya bayyanar da hadisai da suke nuna halifancinsa bayan Manzo da sunansa (A.S). Kuma ingancin wannan wani abu ne da ma’abota ilimi na wannan al’umma da suka fitar da son rai daga zukatansu suka tabbatar da shi, kuma sama da malami hamsin daga masu sharhin hadisansa sun yi bayanin haka suka kuma kare wannan kariya mai cike da hujjoji da dalilai da suka bayar da nutsuwa a kan hakan[21]. Ali (A.S) shi ne wanda ya dawo wa kwakwalen mutane batun hadisan halifancinsa ba tare da wata jayayya ba, bayan an hana fadin wadannan hadisai a lokacin halifofi da suka gabace shi, yayin da suka hana fadin hadisan manzon Allah sai wanda ya shafi ibada kawai:

1- Ya tara sahabban manzon Allah lokacin halifancinsa sannan ya yi musu huduba yana mai hada su da Allah cewa waye ya ji Manzo (S.A.W) a Gadir khum yana cewa; “Duk wanda nake shugabansa Ali shugabansa ne”, sai ya tashi ya shaida[22].

2- Ali shi ne ya yada wannan hadisin da ya bujuro da shi ga Abubakar da Umar da Annabi yake cewa akwai wanda a cikinku zai yi yaki a kan tawilin Kur’ani kamar yadda na yi yaki a kan saukarsa wanda Abubakar ya yi burin a ce shi ne, haka ma Umar, amma Manzo ya amsa musu da: cewa ba su ba ne. Sannan daga baya Manzo ya gaya wa mutane cewa Ali ne[23].

Wannan ruwaya duk da waninsa sun rawaito ta amma ruwayarsa tana da wani hususiyya domin ya yi ta ne a huduba a gaban mutane, ba hadisi ba ne da ya gaya wa mutum daya ko wasu jama’a, wannan kuwa yana karfafa karfin hadisi game da hakkinsa da yake da yakini da shi, kuma yake da yakini da cewa sauran sahabbai suna da yakini da hakan ba su manta ba.

3- Kuma ya ambaci da yawa daga wadannan hadisai da suke nuna hakkinsa a ranar shura ko bayanta, sai dai an yi sabani kan dalla-dallar maganar da isnadinsa, duk da a dunkule sun tabbatar da hakkinsa, mafi karancin abin da ya hada su da Allah a kansa shi ne abin da Ibn Abdulbar ya fitar a littafinsa yana mai cewa: Ali ya fada wa wadanda suke cikin shura tare: “Ina hada ku da Allah shin akwai wanda Manzo (S.A.W) ya hada shi ‘yan’uwantaka da shi tsakaninsa da shi yayin da ya sanya ‘yan’uwantaka tsakanin musulmi in ba ni ba? A bayan wannan hadisi Ibn Abdulbar ya sake rawaito wani daga Ali yana mai cewa: Imam Ali (A.S) ya kasance yana cewa: “Ni bawan Allah ne kuma dan’uwan manzonsa, ba mai fadin haka a bayana sai makaryaci”[24].

An rawaito ta a littafin Kanzul Ummal a wani hadisi mai tsawo daga Abu Dufail ya ce: Ali (A.S) ranar shura yana fadin wannan hadisi…[25]. Wanda abin da shi Ibn Abdulbar ya fitar wani yanki ne daga gareshi, sai dai sanadin Kaznul ummal a kwai jahala[26] a cikinsa, shi ya sa ma aka samu jayayya game da shi, an ce Zafir ya rawaito shi wanda shi mutum ne da ba a san shi ba, wasu kuma sun yi musun sa saboda mataninsa amma ba a la’akari da wannan saboda ya ginu ne a kan fahimta ta cewa an yi bai’a ga Abubakar a kan cewa ijma’i ce ko kusa da hakan wacce ba ta da asasi.

Amma isnadi ya kasance saboda Zafir ne kamar yadda Ibn Abdulbar ya rawaito shi a littafin Isti’ab,[27] Ibn Hajar Askalani ya ce: Zafir ba a tuhumar sa da karya, kuma idan aka same shi a hadisi to hadisinsa yana da kyau[28]. A farkon wannan hadisin, Abu Dufail yana cewa: Na kasance a bakin kofa ranar shura sai aka daga sauti sama, sai na ji Ali (A.S) yana cewa: “Mutane sun yi bai’a ga Abubakar amma na rantse da Allah ni na fi shi cancanta, amma sai na ji na bi domin tsoron kada su koma kafirai wasu suna saran wasu da takobi, sannan sai Umar ya biyo bayansa alhalin na fi shi cancanta kan wannan al’amri, amma sai na ji na bi tsoron kada mutane su koma kafirai wasu suna saran wasu, sannan sai ga ku kuna son ku yi bai’a ga Usman! Ba komai zan ji in bi”, Sannan sai ya ambaci al’amrin shura ya fara bayyana musu falalarsa da fifikonsa da darajojinsa da ya fi su da ita, daya daga cikinsu ita ce wannan bangaren da shi Ibn Abdulbar ya rawaito game da ‘yan’uwantakarsa da Manzo (S.A.W)[29]. Wannan hadisi yana da wani mai karfafarsa da zai zo nan gaba.

4- Daga abin da yake nuna cancantarsa fiye da Abubakar musamman yayin da ya fadi karbar surar bara’a daga Abubakar! Nisa’i ya rawaito da sanadi sahihi daga Ali (A.S) cewa manzon Allah (S.A.W) ya aika shi da bara’a zuwa ga mutanen Makka tare da Abubakar, sannan sai ya sa Ali ya bi shi ya ce da shi: “Ka karbi littafin ka tafi zuwa Makka ya ce: Sai ya cim masa a hanya, sai Abubakar ya koma Madina yana mai bakin ciki, sai ya ce: An saukar da wani abu game da ni ne? Sai Manzo ya ce: A’a, sai dai ni an umarce ni da in isar da wannan ko ni ko wani mutum daga gidana”[30]. A dukkan wannan hadisai akwai raddi ga wanda yake cwa Ali bai ambaci wani abu ba da yake nuna shi ya fi cancanta da halifanci, wannan kenan balle mu shiga Nahajul Balaga.

5- Daga mafi shaharar maganarsa bayan labarin Sakifa ya zo masa da kuma mubaya’ar da mutane suka yi wa Abubakar:

ya ce: Me kuraishawa suka ce?

Suka ce: Sun kafa hujja da cewa su ne bishiyar Manzo.

Sai ya ce; Sun kafa hujja da bishiya amma sun tozarta ‘ya’yan itaciyar[31].

6- Kafa hujja da sakamakon Sakifa a fadinsa:

Idan ka shugabance su sakamakon shura

Yaya haka alhalin masu shawara ba sa nan

Idan kuma ka kafa hujja garesu da kusanci ne

To waninka shi ne ya fi cancanta, ya fi kusanci[32]

7- Hudubar shakshakiyya wacce take da karfafuwa daga malamai[33] daban-daban kuma take da ma’ana da take nuni ga hakan a fili dalla-dalla: “Amma wallahi! Hakika wane ya sanya ta (rigar halifanci) alhalin kuma ya san cewa misalin matsayina game da ita kamar matsayin kan inji ne na nika da dutsensa, kwararar ambaliyar ruwa daga gare ni yake gangarowa kuma tsuntsu ba ya iya kaiwa wajena (duk tashinsa), amma sai na sakaya tufafi na kau da kai[34] na kuma cije na kawar da kai, na zama ina mai kai-kawon ko in tafi da yankakken (shanyayyen) hannu ko kuma in yi hakuri cikin makahon duhu…! Sai na ga hakuri a kan wannan ya fi lizimtuwa, sai na yi hakuri amma a cikin idanu akwai kwantsa, akwai kuma shakewa (ala-ka-kai) a cikin makogaro, ina ganin gadona abin kwacewa! har sai da na farko ya wuce, sai ya mika ta zuwa ga wane bayansa…

Abin mamaki! Yayin da ya kasance yana neman ya sance ta daga wuyansa[35] a rayuwarsa sai ga shi ya kulla (mika) ta ga wani bayan wafatinsa, ya mamakin tsananin yadda suka yi kashe mu raba na abin da yake cikin hantsarta…![36] Sai na yi hakuri tsawon lokaci, da tsananin jarabawa, har sai da ya wuce shi ma sai ya sanya al’amarin halifanci a hannun wasu jama’a da ya raya cewa (wai) ni daya ne daga cikinsu, Kaicon al’amarin shura!, yaushe ne kokwanton fifikon al’amarina a kan na farkonsu ya faru har da zan zama ana sanya ni tsaran makamantan wadannan!…”[37].

Daga wannan magana ta imam Ali (A.S) zamu sani cewa; ashe kenan Abubakar ya san matsayin imam Ali na halifanci da daukakarsa kamar yadda kan dutsen markade da nika yake da daukaka a kan jikin dutsen ne.

Saoba haka ne yake a fili cewa matsayinsa ba boyayye ba ne sai dai mun ga tarihi yana neman ya farar da wani abu na jayayya domin ya yi daidai da abin da ya faru a tarihi, kamar yadda muka samu wasu suna neman musun maganarsa a game da halifanci, wanda da can sun yi musu ga hadisan Manzo (S.A.W). Amma gaskiya tana nan, sai dai abin takaici da tarihi bai karkata zuwa ga Ali ba! Tarihin da ya riga ya tabbatar da cewa imam Ali bai yi bai’a ga Abubakar sai bayan wata shida, sai ya nemi toshe kunnensa game da wannan jinkiri da imam Ali ya yi!

8- Maganarsa bayan shura, yayin da suka yi wa Usman bai’a yana mai cewa: “Wallahi kun sani ni na fi cancanta fiye da wanina, wallahi zan yi hakuri matukar al’amarin musulmi ya kubuta zalunci ya kasance a kaina ne ni kadai, domin neman ladan Allah da falalarsa, da kuma nisantar abin da yake kuna goggoriyonsa na kawa da adonsa”[38]. Ibn Abil Hadid ya samu wannan kalma cikin karshen abin da Ali ya fada a wannan lokaci a maganar da ya nakalto ta a nan bayan ya kawar da duk wani kokwanto game da ingancinta, sai ya ce: Mu muna ambaton wannan abu da ya zo na ruwayoyi masu yawa na imam Ali da ya hada ma’abota shura da Allah, kuma mutane da dama sun rawaito wannan da yawa, amma abin da ya inganta bai kasance da tsawo ba kamar yadda aka rawaito, sai dai bayan sun yi bai’a ga Usman shi ya ki bai’a ya ce: “Mu muna da hakki da in an ba mu sai mu karba, amma idan aka hana mu shi sai mu hau bayan rakuma komai nisan tafiya”. Sannan sai ya ce da su: “Ina hada ku da Allah shin a cikinku akwai wanda Manzo ya sanya shi dan’uwa tsakaninsa da shi in ba ni ba?

Suka ce: A’a.

Ya ce: A cikinku akwai wanda Manzo ya ce: Duk wanda nake shugabansa wannan shugabansa ne in ba ni ba?

Suka ce: A’a.

Ya ce: A cikinku akwai wanda Manzo (S.A.W) ya ce: Kai a wajena kamar matsayin Haruna ne gun Musa, in ba ni ba?

Suka ce: A’a.

Ya ce: Shin a cikinku akwai wanda aka amincewa ya isar da surar bara’a kuma Manzo ya ce: Kuma ba wanda zai isar daga gare ni sai ni ko wani mutum daga gareni, in ba ni ba?

Suka ce: A’a.

Ya ce: Shin ba ku sani ba cewa sahabban Manzo sun gudu sun bar shi a filin daga[39] ba wanda ya rage tare da shi in ba ni ba, ban taba guduwa ba?

Suka ce: E.

Ya ce: Shin kun sani cewa ni ne farkon musulunta?

Suka ce: E.

Sai ya ce: Waye ya fi kusanci da Manzo?

Suka ce: Kai ne.

Sai Abdurrahman dan Auf ya katse maganarsa ya ce: Ya Ali! mutane ne suka zabi Usman, kada ka dora wa kanka laifi (ka damu kanka).

Sannan sai Abdurrahman ya kalli Abu Dalha Al’ansari[40] ya ce da shi: Ya Aba Dalha da menene Umar ya umarce ka?

Sai ya ce: In kashe duk wanda ya saba wa al’umma!

Sai Abdurrahaman dan Auf ya ce da imam Ali: Ka yi bai’a tun da haka ne, in ba haka ba sai ka zama wanda bai bi tafarkin musulmi ba! Kuma mu zartar da umarnin da aka umarce mu da shi a kanka!!

Sai Ali (A.S) ya ce: “Kun sani ni ne mai wannan hakki ba wani ba, wallahi zan yi hakuri matukar al’amarin musulmi ya tafi daidai zalunci ya zamanto a kaina ne kawai…”[41]. Wannan kuma hadisi jama’a da yawa suka rawaito shi, ba ya cikin raunanansu ko wadanda ake kokwanto.

9- Wani ya taba cewa da imam Ali ya dan Abi Dalib kai ka kasance mai kwadayin wanna shugabanci, sai ya ce: Ku ne kuka fi ni kwadayinsa kuma ku ne mafi nisa, amma ni na fi kusanci, kuma ina neman hakkina ne, ku kuma kuna hana ni, kuna juyar da fuskata daga gareshi, yayin da ya kafa masa hujja a cikin mutane sai ya juya yana dimuwa bai san me zai amsa ba”[42].

Ahlussunna sun ce wanda ya fadi haka shi ne Sa’ad dan Abi Wakkas ranar shura, Shi’a kuma sun tafi a kan Abu ubaida ne bayan Sakifa, kowanne ne gaskiya dai muhimmin abu ne wanda ya shahara da kowa Sunna da Shi’a suke rawaito wa kamar yadda Ibn Abil Hadid wanda yake Sunna kuma Bamu’utazili yake rawaitowa[43].

10- Fadinsa: “Ya Ubangiji! ni ina hada ka da kuraishawa da wanda ya taimaka musu, sun yanke zumuncina sun karanta matsayina, sun hadu a kan kwace mini abin da yake nawa ne, sannan suka ce: Ka karba da gaskiya ko ka bari da gaskiya[44],

11- Fadinsa: “Amma bayan haka… Yayin da Allah ya karbi ran annabinsa (S.A.W) sai muka ce mu ne ahlinsa masu gadonsa zuriyarsa majibinta al’amarinsa ba wani ba, ba mai yi mana jayayya kan shugancin Muhammad, kuma kada wani ya yi kwadayin hakkinmu, sai mutanenmu suka mike suka kwace mana hakkinmu na shugabanci, sai ga shugabancin a hannun waninmu…”.

Wannan duk yana daga hudubobin da imam Ali ya yi a Madina a farkon shugabancinsa a lokacin bai fi watanni da karbar halifanci ba[45].

12- Fadinsa: “Amma kwace mana wannan matsayi wannan wani abu ne da kwadayin mutane ya jawo shi, wasu kuma suka yi bakin ciki kan matsayinmu, alhali hukunci na Allah ne, kuma makoma a ranar kiyama tana nan gareshi”. Ya fadi wannan a jawabin wanda ya tambaye shi: Yaya mutane suka ture ku daga wannan matsayi alhali ku kuka fi cancanta da shi.

Sannan sai imam Ali ya cigaba da magana kan wani abin da ya fi ban mamaki na wannan zamani da kamar Mu’awiya zai zo yana jayayya da shi, yana mai cewa “Zamani ya kai munzalin da yanzu ya ba shi dariya bayan ya sa shi kuka”[46].

Game Da Ahlul Baiti (A.S)

Kamar yadda ya bayyana a fili na karfafa wa ga hakkinsa musamman, matsayin Ahlul Baiti (A.S) yana iya bayyana garemu daga wadannan kalmomi da suka zo daga gareshi:

1- Fadinsa: “Haka yake, duniya ba za ta taba zama ba hujjar Allah ba a cikinta, ko zahiri mash’huri ko kuma boyayye, domin kada hujjar Allah da ayoyinsa su bace”[47]. Ibn Abil Hadid malamin sunna ne amma yana cewa: A nan Imam Ali (A.S) ya yi nuni da bin mazhabar Shi’a isna ashariyya ne[48].

2- Fadinsa: “Ba a kwatanta alayen Muhammad da wani daga wannan al’umma su ne asasin addini kuma madogarar yakini… su ne suke da hakkin wilaya da jagoranci, kuma wasiyya da gado nasu ne”[49].

Bayan ambaton hakkin jagoranci, wannan al’amari wani abu ne da imam Ali ya yi bayaninsa a fili ko ya yi nuni[50] da shi, amma sai ga shi irin su Dakta Ammara yana neman ya gafala daga wannan hudubobi na imam Ali (A.S) yana neman nuna rashin samun magana ta karara a kan hakan, Da kuma neman kare kagen da ya yi domin ya nuna kalmar “wasiyyi” da ta zo a hadisud dar, da cewa kage ne na Shi’a da suka sanya kalmar wasiyyi maimakon waziri[51] alhalin hadisin da ya zo daga ruwayar Ahlussunna bai zo da wata kalma ba in banda kalmar wasiyyina[52].

3- Hadisin “shugabanni daga kuraishawa ne, kuma suna cikin Bani Hashim, ba na waninsu ba ne, kuma shugabanci ba ya yiwuwa ga waninsu”[53]. Mun riga a baya mun yi nuni da wasu hadisai da suka nuna duk wani fifiko da cancantar Bani Hashim a kan sauran kuraishawa.

4- Fadinsa (A.S): “Ina zaku ne! Yaya kuke kirkirar karya! ga hujjoji a fili, ga ayoyi karara, ga manarori a kafe, yaya ake dimautar da ku?! Yaya kuka makance alhali a cikinku akwai zuriyar annabinku, su ne jagororin gaskiya, kuma alamomin addini, harsunan gaskiya?! Ku sanya su a matsayi mafi kyau na Kur’ani, ku kuma gangaro zuwa garesu irin gangarowar nan ta mai kishirwa. Ya ku mutane ku rike ta daga cikon annabawa (S.A.W) cewa: Duk wanda ya mutu daga cikinmu ba matacce ba ne, kuma duk wanda ya rididdige a cikinmu ba rididdigagge ba ne”[54]. A cikin wannan akwai abin takaici da imam (A.S) ya yi nuni da shi ga wadanda suka bar Alayen Annabi (A.S) bayan hujja da dalilai masu karfi, bayyanannu da suke wajabta bin su.

5- Fadinsa: “Mu kama ce ta tsatson ma’abota jirgin ruwa, kamar yadda wanda yake cikin can ya tsira haka ma wanda yake cikin wannan zai tsira, azaba ta tabbta ga wanda ya bar mu… kuma ni a cikinku kamar kogo ne na As’habul kahafi, kuma ni kamar kofar hidda ce, da wanda ya shige ta ya tsira wanda ya ki shiga ya halaka, ni hujja ce daga watan zilhijja a hajjin bankwana da fadin Annabi (S.A.W) cewa: “Ni na bar muku abin da idan kuka yi riko da shi ba za ku taba bata ba a bayana har abada; littafin Allah da kuma Ahlin gidana”[55].

6- Hudubarsa (A.S): “Ku duba Ahlin gidan Annabinku, ku lizimti tafarkinsu, ku bi sunnarsu, ba zasu taba fitar da ku daga shiriya ba ba kuma zasu taba dawo da ku cikin bata ba… idan suka yi kasa ku yi kasa idan suka tashi ku tashi… kada ku riga su sai ku bata, kada ku yi jinkirin binsu sai ku halaka”[56].

7- Fadinsa (A.S): “… shin ban yi aiki a cikinku da alkawari mafi girma ba, kuma na bar muku (na yi muku wasiyya da) alkawari mafi karanta”[57]. Alkawari mafi girma shi ne Kur’ani, alkawari mafi karanta su ne Ahlul Baiti (A.S) da su ne imam Ali (A.S) da Fadima (A.S) da imam Hasan (A.S) da imam Husain (A.S).

8- Fadinsa (S.A.W): “Mahadi daga cikinmu yake Ahlul Baiti, Allah zai tayar da shi a dare daya”, Ahmad da Suyudi sun rawaito shi daga Ali (A.S)[58]. Da fadinsa: “Mahadi daga garemu yake ‘ya’yan Fadima”, Suyudi ya karbo shi daga Ali (A.S)[59]. Haka nan wadannan ruwayoyi suka zo game da Mahadi daga hadisai masu yawa, da bayanai a fili, da ishara da siffa, da kuma bayanin tarihi tabbatacce.

A takaice muna iya cewa matakin imam Ali (A.S) da yakininsa na hakkinsa a game da halifanci ya kasance yakini ne wanda yake ya samu daga matsayinsa gun Annabi (S.A.W) da kuma rayuwarsa ta hidima ga musulunci, hakika ya kasance a rayuwar Manzo (S.A.W) yana cewa: Allah madaukaki yana cewa; “Idan ya mutu ko aka kashe shi sai kuka juya a kan dugaduganku[60] (kuka bar tafarkinsa)”, Imam Ali (A.S) yana cewa: “Wallahi ba zamu juya a kan dugaduganmu ba, bayan Allah ya shiryar da mu, wallahi idan ya mutu ko aka kashe shi, sai na yi yaki a kan abin da ya yi yaki a kai har in mutu, wallahi ni ne dan’uwansa kuma waliyyinsa dan amminsa mai gadon iliminsa, wanene ya fi cancanta da shi fiye da ni”[61].

A wani wajen Ali (A.S) yana cewa: “Yayin da ya rasu sai musulmi suka yi jayayya a kan mulkinsa bayansa, wallahi bai taba fado mini ba, ban kuma taba tunanin cewa larabawa zasu kawar da wannan jagoranci a bayansa daga Ahlin gidansa ba! ban taba tsammanin za a kawar da shi daga gareni ba bayansa! sai ga mutane sun yi dafifi ga wane suna yi masa bai’a…”[62]. Ashe kenan yana nufin hakkin da mutane suke nemansa, shi kuma ba ya rigonsu zuwa ga nemansa”[63].

Game Da Bai’ar Imam Ali (A.S) Ga Halifofi Uku

Sun kawo matsalar cewa imam Ali (A.S) ya yi wa halifofi uku bai’a, suka raya cewa wannan bai’ar kuma ba zai yiwu a ce domin maslaha ya yi ta ba, ko domin takiyya, ko tilastawa, domin wannan yana nuna tauye matsayi na imam Ali (A.S). Amsar da zamu bayar ita ce: Game da tilasta shi wannan abu ne a fili, da masu tarihi suka rawaito. Buhari yana cewa: “Ali (A.S) ya ki yin bai’a ga Abubakar tsawon wata shida har sai da Fadima (A.S) ta rasu”[64]. A hadubar imam Ali (A.S) ya fadi dalilin da ya sa ya yi bai’a, a hudubarsa da yake cewa:

A- “Na rantse da Allah ba domin tsoron rarraba ba, kafirci ya dawo, addini ya rushe, da mun kawar da wannan jagoranci, amma sai muka yi hakuri a kan wasu zogi da bakin ciki da yake damun mu”[65].

B- Yana fada a Nahajul Balaga: “Sai na duba, sai ga shi ba ni da wasu masu taimaka mini sai Ahlin gidana (A.S) sai na yi wa mutuwa rowarsu, na kuma runtse idanuna a kan wannan kwantsa, na yi himmar hadiyar bakin ciki, na yi hakuri a kan juriya da kuma hakurin dacin da ya fi na madaci”[66]. Shin zai yiwu a zo da wani bayani wanda ya fi wannan zama karara?! In ba haka ba menene ya sa duk wannan bayan irin wannan kokawa da kai kara? alhalin shi ne mafi sanin mutane da halin da ake ciki da sakamakon abin da ya faru.

Da a ce bai kafa musu hujja ba ya baro janazar Manzo (S.A.W) ya tafi Sakifa ya bar jikin masoyinsa (S.A.W) bai wanke shi ba, ya zo ya dora hannunsa a kan hannunsu ya yi bai’a da ba ma’ana ya zo da irin wannan kafa hujja. Idan ya tabbata ta hanya sahihiya Ali dan Abi Dalib (A.S) cewa ya soki nazarin shura ya kuma shelanta cewa ta saba wa shari’a… ya kuma fadi cewa an tilasta shi ne ya yi bai’a ga halifofi uku to bai’arsa ba ta da wani dalili na shari’a a kan halifancinsu kamar yadda wannan ya tabbata a fili daga maganganunsa.

Sannan ya bayyana cewa shi ne ya fi cancanta da halifanci, shin zai yiwu mu ce cancantarsa ga halifanci tana nufin shi ya fi, da ma’anar cewa duk da shi ne ya fi amma da waninsa zai karbi halifanci da ba komai? ko kuwa tana nufin shi ne kawai ya cancanta da halifanci?

Wannan ra’ayi na farko ba daidai ba ne saboda nassin hadisai da kuma maganganun imam Ali (A.S) yayin da yake cewa: “Mutane sun yi bai’a ga Abubakar alhalin ni ne na cancanci in sanya rigata wannan (wato in yi halifanci) daga garesu”. Wannan yana nufin cancantar da ta kebanta da shi, ba wai yana nufin fifikon cancanta ba ta yadda wani ma yana iya cancanta da ita, domin ba ma’anar ya ce rigarsa ce sannan ya zama ba ya nufin cancanta, domin mai riga shi ne mai ita mai cancanta da ita mai mallakarta.

Sannan ga fadinsa da yake cewa: “…Na zama ina mai kai-kawon ko ina tafi da yankakken (shanyayyen) hannu ko kuma in yi hakuri cikin makahon duhu, da babba yake tsufa a cikinsa yaro kuma yake girma a ciki, mumini yake shan bakar wahala a ciki har sai ya riski Ubangijinsa. Sai na ga hakuri a kan wannan ya fi lizimtuwa, sai nayi hakuri amma a cikin idanu akwai kwantsa, akwai kumashakewa (ala-ka-kai) a cikin makogaro, ina ganin gadona abin kwacewa”[67]. Ma’anarsa sai na samu kaina tsakanin ko in karba da karfin da bai isa ba kamar yadda ya zo a fadarsa (A.S): “Saina duba, sai gaba ni da wasu masu taimaka mini sai Ahlin gidana (A.S) saina yi wa mutuwa rowarsu”. Wato daya sami karfi isasshe da ya yaki ma’abota Sakifa kamar yadda yake a maganarsa da aka sani da yake cewa: “Da nasamu mutum arba’in masuniyya da gaskiya da na kawar da mutunen”.

Wannan mataki na imam Ali (A.S) bayadda za a fassara shi da ma’anar yafi cancanta da ma’anar wanima yana iya rikon jagoranci, wannan afili yake cewa ya yi daidai da ma’ana ceta cancantar kebantaka da shi. Hakanan fadinsa (A.S): “Ko kumain yi hakuri cikin makahon duhu…”. Ma’anarsa abin da ya faru ba kawai kwacen mulki ba ne, sai daiwannan yana zama farkon faruwar canji ne da zai iya kai al’umma gabata, Shi ya sa ya karfafa wa mutane bayan kashe Usman dan Affan yayin da suka zo domin yi masa bai’a: “Ku rabu da ni ku nemi wanina domin tafarki ya bice hujja kuma an yi musun ta”[68], da fadinsa garesu: “Ni inaji muku tsoro ne ku kasance cikin wani yanayi na lokaci, alhalin dacan wadansu al’amura sunfaru sun wuce da kuka karkata zuwa garesu karkatar da kuka zamo ba abin yabo ba ne ku a guna”[69].

Dalilan Tarihi A kan Ingancin Mahangar Nassi

Dalilan tarihi a rayuwar Annabi (S.A.W) da Ali a kan cewa Manzo (S.A.W) ya kasance yana yana shiryar da Ali da tarbiyya na daukar sako bayan wucewarsa, yana ba shi ilimi da tunani yana kuma kebewa da shi kowane dare da rana, yana wayar da shi a kan abin da sakon musulunci yake dauke da shi da matsalolin tafarkin har zuwa ranar karshe ta rayuwarsa.

Nisa’i[70] ya rawaito da sanadinsa zuwa ga Abi Ishak, ya ce: An tambayi Kusum dan Abbas cewa, yaya Ali ya zama mai gadon Annabi (S.A.W) banda ku? Sai ya ce: Domin shi ne na farkon haduwa da shi kuma mafi damfaruwa da shi”.

Haka nan ya rawaito[71] daga Ali (A.S) ya ce: “Na kasance idan na tambaya sai a ba ni, idan na yi shiru sai a fara –gaya- mini”.

Abu Na’im ya rawaito a littafin Hilyatul auliya daga dan Abbas ya ce: “Mun kasance muna magana a lokacin Annabi (S.A.W) cewa ya ba wa Ali wasiyya (ilimi) saba’in da bai ba wani shi ba”[72].

Nisa’i ya rawaito daga Ali (A.S) ya ce: “Ina da wani matsayi gun manzon Allah (S.A.W) da babu wani mahaluki da yake da shi, na kasance ina zo masa kowane karshen dare sai in ce: Assalamu alaika ya nabiyyallah, idan ya yi gyaran murya sai in koma zuwa ga Ahlina, in ba haka ba sai in shiga wajansa”[73]. Daga gareshi ya ce: “Ina da shiga guda biyu wajan manzon Allah, daya da dare, daya da rana”[74].

Wannan irin tarbiyyantarwa ga Ali da Manzo (S.A.W) ya yi masa ya yi tasirin da Ali ya zama shi ne madogarar kowa makoma ga warware duk wata matsala da aka kasa warware ta hatta da masu jagoranci a wannan lokaci, amma ba a taba samun wata matsala guda daya ba a tarihin imam Ali da ya koma zuwa ga wani mutum ko daya, yayin da a tarihi akwai mas’aloli da dama da dukkkan halifofi suka koma zuwa gareshi duk da kokarin boye wannan matsayi nasa da aka yi.

Amma tarihi ya riga ya tabbatar mana shelantawar da Annabi (S.A.W) ya yi game da hikimar da yake da ita wajan ba wa Ali tarbiyya da ilimi na musamman wanda suna da yawa da suka faru a lokuta daban-daban, kamar hadisuddar, da hadisin sakalaini, hadisin manzila, da hadisin Gadir, da gomomin hadisai[75].

Dalilin Tabbatar Wasiyya Daga Ruwayoyi

Idan nazarin samuwar nassi ya tabbata ita ce kawai hanyar shari’a da Annabi (S.A.W) ya tabbatar da ita a rayuwarsa a tarihi. Kuma imam Ali (A.S) ya ki dukkan wani abu da zai zama makoma ga jagoranci bayan Manzo in ba wasiyya ba, sai ya rage mana mu yi bincike game da dalili ta fuskacin shari’a da yake tabbatar da cewa Manzo (S.A.W) ya yi wasiyya da imam Ali (A.S) da halifanci bayansa, kamar yadda shi ma ya yi wasiyya da halifanci da imamai bayansa.

Shi’a suna da akidar cewa imamancin imam Ali da ‘ya’yansa Hasan da Husain da kuma tara daga zuriyar Husain (A.S) duk an samu nassi da ya zo game da hakan daga manzon Allah (S.A.W) wanda kuma kowanne daga cikinsu ya yi wasiyya da mai bi masa, nassosin hadisan sun kasu gida uku ne:

Nau’i na farko: Abin da yake wajabta komawa zuwa ga Ahlul Bait (A.S) ba tare ya fadi sunayensu ba; kamar hadisin sakalaini da hadisin safina wadanda mutawatirai ne daga Shi’a da Sunna.

Nau’i na biu: Abin da yake iyakance adadin halifofin Annabi da cewa sha biyu ne kuma daga kuraishawa daga Bani Hashim suke, Wannan kuwa adadi ba ya dabbakuwa sai a kan imamai na Ahlul Baiti (A.S), sabanin idan an dabbaka shi a kan wasunsu.

Nau’i na uku; Hadisan da suka zo da ambaton sunayensu (A.S) har guda goma sha biyu, ta hanyar Shi’a da Sunna.

Amma Abin da Ya Zo A Nau’i Na Farko

Tirmizi ya rawaito daga Jabir yana cewa: “Na ga manzon Allah (S.A.W) a hajjin bankwana yana kan taguwarsa da shi da Ali (A.S) sai na ji shi ya ce: “Ya ku mutane na bar muku abin da idan kun yi riko da su ba zaku taba bata ba, littafin Allah da Ahlin gidana”[76]. Tirmizi ya ce: A wannan babi kawai an karbo wannan hadisi daga Abi Sa’id da Zaidu dan Arkam da Huzaifa dan Asid.

A Sahih Muslim da Masnad Ahmad dan Hanbal da Sunan Darimi da Baihaki da wasunsu kuma lafazi ga na farko yake daga Zaid dan Arkam ya ce: “Manzon Allah ya tsaya yana mai huduba a wani ruwa da ake kira Khum da yake tsakanin Makka da Madina… Sannan ya ce: “Ya ku mutune ku sani ni mutum ne da dan sakon ubangijina ya kusa zuwa sai in amsa masa, na bar muku nauyaya biyu; Na farko littafin Allah da akwai shiriya a cikinsa, ku yi riko da littafin Allah da kuma Ahlin gidana”[77].

A cikin sunan Tirmizi da masnad Ahmad da lafazin Tirmizi: “Na bar muku abin da da idan kuka yi riko da shi ba zaku taba bata ba bayana, daya ya fi daya girma: littafin Allah igiya mikakkiya daga sama zuwa kasa, da kuma Ahlin gidana, ba zasu taba rabuwa ba har sai sun riske ni a tafki, ku duba ku gani yaya zaku maye mini a cikinsu”[78].

Daga irin hadisai da suka zo akwai hadisin safina, Manzo (S.A.W) yana cewa: “Ku sani misalin Ahlin gidana a cikinku kamar jirgin Nuhu ne, wanda ya hau ya tsira wanda kuma ya bar shi ya nutse”[79].

Wasu malamai da dama suna ganin Ahlin gidan Annabi (S.A.W) su ne mutum biyar masu girma da daraja da ya hada da annabin kansa (S.A.W) da kuma Ali da sayyida zahara da Hasan da Husain (A.S). Wannan kuwa ita ce mahangar da yawa daga sahabbai, wadanda suka tafi a kan hakan sun hada da, Abu Sa’idul Khuduri, da Anas dan Malik, da Wasila dan Aska’a, da Ummul muminin Ummu Salama, da A’isha, da Ibn Abi Salama -agolan Annabi- da Sa’ad dan Abi Wakkas, da sauransu.

Ma’abota tafsiri da ruwayar hadisai da dama sun tafi a kan hakan daga cikinsu akwai; Faharur razi a littafin Tafsirul kabir, da Zamakhshari a Kusshaf, da Kurdabi a Aljami’u li ahkamil kur’an, da Shaukani a Fatahul gadir, da Tabari a Jam’ul bayan an tawili ayil kur’an, da Suyudi a Durrul mansur, da Ibn Hajar Al’askalani a littafin Isaba, da Hakim a Mustadrak, da Zahabi a cikin Talkhis, da imam Ahmad dan Hanbal a littafin Masnad. Wannan kuwa shi ne ra’ayi da yafi zama daidai, shi ya sa ma zamu gani a ruwayar Muslim a sahihinsa da sanadinsa zuwa ga Amir dan Sa’ad dan Abi Wakkas, daga babansa ya ce: Mu’awiya dan Abi Sufyan ya umarci Sa’ad da ya tsinewa imam Ali (A.S) ya ce: Me ya hana ka ka zagi Aba turab? -Kinaya ce ta imam Ali- Sai Sa’ad ya ce: Amma matukar ina tuna uku da Manzo ya fada game da shi ba zan taba zaginsa ba, wallahi ya zama ina da daya daga cikinsu ya fi mini jajayen dabbobi”. Na ji Manzo (S.A.W) yana cewa da shi -yayin da ya bar shi a wani yaki- sai Ali ya ce: Ka bar ni tare da mata da yara? Sai Manzo (S.A.W) ya ce da shi: Ba ka yarda ba da cewa matsayinka a wajena kamar matsayin Haruna ne gun musa sai dai babu wani Annabi bayana. Na kuma ji shi (S.A.W) yana fada a ranar Haibar: Zan bayar da wannan tuta ga wani mutum da yake son Allah da manzonsa, Allah da manzonsa suke sonsa, ya ce: Sai duk muka yi burinta, sai ya ce: Ku kira mini Ali, sai aka zo da shi yana ciwon ido sai ya yi tofi a idanunsa sannan ya mika masa tutar da Allah ya bayar da nasara a hannunsa.

Yayin da ayar Mubahala: “Ka ce ku zo mu kira ‘ya’yanmu da ‘ya’yanku…” ta sauka sai Manzo (S.A.W) ya kira Ali da Fadima da Hasan da Husain ya ce: Ya Ubangiji wadannan su ne Ahlin gidana”[80]. Tirmizi ya rawaito a sahihinsa da sanadinsa daga Amir dan Sa’ad dan Wakkas ya ce: Yayin da wannan aya ta sauka “Mu kira ‘ya’yanmu da ‘ya’yanku” sai Manzo (S.A.W) ya kira Ali da Fadima da Hasan da Husain sannan ya ce: Ya Allah wadannan su ne Ahlin gidana”[81]. Haka nan Hakim[82] ya rawaito shi a littafin Mustadrak da Baihaki[83] shi ma a littafin sunna.

Mawallafi littafin Kusshaf yana cewa: Babu wani dalili mafi karfi ga falala da daukaka da ya kai wannan ga ma’abota bargo, wadanda su ne Ali da Fadima da Hasan da Husain. Domin su yayin da yayar mubahala[84] ta sauka ya kira su ya rungume Husain ya rike hannun Hasan, Fadima tana bayansa Ali kuma yana bayanta, da wannan ne aka san ma’anar ayar, kuma ‘ya’yan Fadima da zuriyarsu ana kiransu ‘ya’yansa, kuma ana danganta su ga Manzo dangantawa ingantacciya mai amfani a duniya da lahira[85]. Imam Ahmad ya rawaito a babin falala da sanadinsa daga Shaddad Abi Ammar, ya ce: Na shiga wajan Wasila dan Aska’a, a wajansa akwai wasu mutane sai suka rika maganar Ali (A.S) sai suka zage shi ni ma sai na zage shi tare da su, bayan sun tashi sai ya ce da ni: Ba na ba ka labari ba daga abin da na gani daga manzon Allah (S.A.W) ? Sai na ce: Na’am, Sai ya ce: Na zo wajan Fadima (A.S) ina tambayar ta Ali, sai ta ce ya tafi wajan manzon Allah (S.A.W), sai na zauna na saurare shi har sai da manzon Allah ya zo a tare da shi akwai Ali da Hasan da Husain (A.S), kowannensu yana rike da hannunsa, sai ya zaunar da Hasan da Husain kowanne a kan cinyarsa sannan sai ya lulluba masu tufafinsa -ko kuma bargo- sannan ya karanta wannan aya: “Kawai Allah yana son ya tafiyar da dauda daga gareku Ahlul Baiti ya tsarkake ku tsarkakewa”. Sannan sai ya ce: “Ya Ubangiji wadannan su ne Ahlin gidana, Ahlin gidana su suka fi cancanta”[86]. Tabari ya rawaito shi a cikin tafsirinsa[87] da Tirmizi[88] a cikikn sahihinsa, da Suyudi[89] a Durrul mansur, da Haisami a Majma’az zawa’id[90], da Hakim a Mustadrak[91] da Ahmad a Masnad[92].

Amma Abin Da Ya Zo Game Da Nau’i Na Biyu

Hadisin da Manzo (S.A.W) ya fadi adadin imamai a ciki kuma su sha biyu ne; Manzo ya bayar da labarin adadin imamai da zasu zo bayansa da imami kuma halifa bayansa kamar yadda ma’abota sihah (ingantattun littattafai) da ma’abota masanid suka rawaito kamar yadda zai zo:

1-Muslim ya raywaito daga Jabir daga Samura cewa ya ji Annabi (S.A.W) yana cewa: “Addini ba zai gushe ba yana mai tsayuwa har sai alkiyama ta tashi ko kuma an samu halifofi goma sha biyu a gareku dukkaninsu daga Kuraish”. A wata ruwaya sai Annabi ya fadi wata kalma da ban ji ba, sai na tambayi babana: menene manzon Allah ya ce: Sai ya ce: “Dukkaninsu daga Kuraishi suke”[93]. A wata ruwaya ya ce: “Dukkaninsu daga Bani Hashim”[94].

Ahmad da Hakim sun rawaito da lafazin Hakim daga Masruk ya ce: Mun kasance muna zaune a wani dare gun Abdullahi dan Mas’ud yana karanta mana Akur’ani sai wani mutum ya tambaye shi: ya Aba Abdurrahman shin kun tambayi Annabi (S.A.W) halifa nawa ne zai mallaki al’amarin wannan al’umma? Sai Abdullahi ya ce: Tun da na zo Iraki ba wanda ya tambaye ni wannan kafin kai! Sai ya ce: Mun tambaye shi sai ya ce: “Goma sha biyu ne, da adadin zababbun Bani Isra’il”[95].