• Farawa
  • Na Baya
  • 41 /
  • Na Gaba
  • Karewa
  •  
  • Gurzawa HTML
  • Gurzawa Word
  • Gurzawa PDF
  • Budawa: 4133 / Gurzawa: 1542
Girma Girma Girma
Fassarar Kur'ani

Fassarar Kur'ani

Mawallafi:
Hausa

Abin lura dangane da wannan littafin

Wanda ya tsara ya buga kuma ya yada

Muassasar Hasanain don yada al’adun Musulunci

Da fatan Allah Ta'ala ya datar da mu wajen kara gyara shi da fitar da shi bisa mafi kyawun sura

www.alhassanain.org/hausa

TARJAMAR KUR'ANI MAI DARAJA

Wallafar: Hafiz Muhammad Sa’id

hfazah@yahoo.com

Da Sunan Allah Ta'ala Mai Rahama Mai Jin Kai

KUR'ANI MADAUAKAKI:

"MU NE MUKA SAUKAR DA AMBATO KUMA MU MASU KARIYA NE GARESHI".

DAGA SURAR NABA'I ZUWA SURAR NASI

Surar Fatiha([1])

سورة الفاتحة

Ayoyinta 7 ne, Ana kiranta Uwar Littafi domin ta tara ilmin da yake a cikin Kur'ani a dunk'ule. Basmala a cikinta take ga k'ira'ar Asim, ruwayar Hafs, amma banda a k'ira'ar Warsh.

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ

1. Da Sunan Allah Mai Rahama Mai Jin k'ai.

الْحَمْدُ لِلّهِ رَبِّ الْعَالَمِينَ

2. Godiya ta tabbata ga Allah ubangijin talikai.

اَلرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ

3. Mai rahama mai jin k'ai.

مَالِكِ يَوْمِ الدِّينِ

4. Mai mallakar ranar sakamako.

إيَّاكَ نَعْبُدُ وإِيَّاكَ نَسْتَعِينُ

5. Kai kad'ai muke bautawa kuma kai kad'ai ne muke neman taimako.

اِهْدِنَا الصِّرَاطَ المُسْتَقِيمَ

6. Ka shiryar da mu tafarki madaidaici.

صِرَاطَ الَّذِينَ أَنعَمْتَ عَلَيهِمْ غَيرِ المَغضُوبِ عَلَيهِمْ وَلاَ الضَّالِّينَ

7. Tafarkin wad'anda ka yi wa ni'ima, ba wad'anda aka yi fushi da su ba, kuma ba b'atattu ba.

Ubangijin halittu ya tara ilmin Tafiyar da lamurran bayi da halitta su, kamar rayarwa, da matarwa, da ciyarwa, da shayarwa, da tufatarwa, Mai rahama Ya tara dukan rahamar duniya da dukkan ni'imomin samarwa gaba d'aya. Mai jin k'ai ya tara ni'imar duniya mai dogewa zuwa Lahira kamar ni'imar imani. Mai mallakar ranar sakamako, ya had'a dukan abin da ya shafi makoma. Kai muke bauta wa kuma Kai muke neman taimako, ya tara tauhidin bauta da ibada. Hanya madaidaiciya, ta had'a Littafin Allah da Ahlul Baiti (a.s) a matsayin wasiyyar Ma'aikin Allah. Wad'anda aka yi wa ni'ima, su ne Alayen Ibrahim da Alayen Muhammad (a.s). Wad'anda aka yi fushi da su, da kuma b'atattu, sun tara dukkan mutanen da suka kauce wa tafarki madaidaici.

Surar Labari([2])

سورة النبإ

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ

Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin K'ai

عَمَّ يَتَسَاءَلُونَ

1. A kan me suke tambayar juna?

عَنِ النَّبَإِ الْعَظِيمِ

2. A kan muhimmin labari mai girma?

الَّذِي هُمْ فِيهِ مُخْتَلِفُونَ

3. Wanda suke sab'a wa juna a cikinsa?

كَلَّا سَيَعْلَمُونَ

4. A'aha! Za su sani.

ثُمَّ كَلَّا سَيَعْلَمُونَ

5. Kuma, a'aha! Za su sani.

أَلَمْ نَجْعَلِ الْأَرْضَ مِهَادًا

6. Ashe, ba Mu sanya k'asa shimfida ba?

وَالْجِبَالَ أَوْتَادًا

7. Da duwatsu turaku (ga rik'e k'asa)?

وَخَلَقْنَاكُمْ أَزْوَاجًا

8. Kuma, Mun halitta ku maza da mata?

وَجَعَلْنَا نَوْمَكُمْ سُبَاتًا

9. Kuma, Muka sanya barcinku hutawa?

وَجَعَلْنَا اللَّيْلَ لِبَاسًا

10. Kuma, Muka sanya dare (ya zama) sutura?

وَجَعَلْنَا النَّهَارَ مَعَاشًا

11. Kuma, Muka sanya lokacin rana na neman abin rayuwa?

وَبَنَيْنَا فَوْقَكُمْ سَبْعًا شِدَادًا

12. Kuma, Muka gina sammai bakwai masu k'arfi, , a samanku?

وَجَعَلْنَا سِرَاجًا وَهَّاجًا

13. Kuma, Muka sanya fitila mai tsanin haske (rana).

وَأَنزَلْنَا مِنَ الْمُعْصِرَاتِ مَاءً ثَجَّاجًا

14. Kuma, Muka saukar ruwa mai yawan zuba daga cikakkun giragizai?

لِنُخْرِجَ بِهِ حَبًّا وَنَبَاتًا

15. Domin, Mu fitar da k'waya da tsiri da shi?

وَجَنَّاتٍ أَلْفَافًا

16. Da itacen lambuna masu lillibniya?

إِنَّ يَوْمَ الْفَصْلِ كَانَ مِيقَاتًا

17. Lalle ne, ranar rarrabewa ta kasance abin k'ayyade wa lokaci.

يَوْمَ يُنفَخُ فِي الصُّورِ فَتَأْتُونَ أَفْوَاجًا

18. Ranar da za a yi busa a cikin k'aho, sai ku zo, jama'a-jama'a.

وَفُتِحَتِ السَّمَاءُ فَكَانَتْ أَبْوَابًا

19. Kuma, aka bud'e sama, sai ta kasance k'ofofi.

وَسُيِّرَتِ الْجِبَالُ فَكَانَتْ سَرَابًا

20. Kuma, aka tafiyar da duwatsu, sai suka kasance k'ura.

إِنَّ جَهَنَّمَ كَانَتْ مِرْصَادًا

21. Lalle ne, Jahannama ta kasance madakata.

لِلْطَّاغِينَ مَآبًا

22. Makoma ce ga masu k'etare iyakoki.

لَابِثِينَ فِيهَا أَحْقَابًا

23. Suna, masu zama a cikinta, zamunna.

لَّا يَذُوقُونَ فِيهَا بَرْدًا وَلَا شَرَابًا

24. Ba su d'and'anar wani sanyi a cikinta, kuma ba su d'and'anar wani abin sha.

إِلَّا حَمِيمًا وَغَسَّاقًا

25. Sai dai tafasasshen ruwa da rub'ab'b'en jini.

جَزَاءً وِفَاقًا

26. Sakamako mai dacewa.

إِنَّهُمْ كَانُوا لَا يَرْجُونَ حِسَابًا

27. Lalle ne, su, sun kasance ba su fatar wani sauk'in hisabi.

وَكَذَّبُوا بِآيَاتِنَا كِذَّابًا

28. Kuma, suka k'aryata da ayoyinMu, k'aryatawa!

وَكُلَّ شَيْءٍ أَحْصَيْنَاهُ كِتَابًا

29. Kuma kowane abu Mun k'ididdige shi, a rubuce.

فَذُوقُوا فَلَن نَّزِيدَكُمْ إِلَّا عَذَابًا

30. Saboda haka ku d'and'ana, domin haka ba za Mu k'ara muku komai ba sai azaba.

إِنَّ لِلْمُتَّقِينَ مَفَازًا

31. Lalle ne, masu tak'awa na da wani wurin samun babban rabo.

حَدَائِقَ وَأَعْنَابًا

32. Lambuna da inabobi.

وَكَوَاعِبَ أَتْرَابًا

33. Da cikakkun 'yan mata, tsaran juna.

وَكَأْسًا دِهَاقًا

34. Da hinjalan giya cikakku.

لَّا يَسْمَعُونَ فِيهَا لَغْوًا وَلَا كِذَّابًا

35. Ba sa jin yasassar magana a cikinta, kuma ba sa jin k'aryatawa.

جَزَاءً مِّن رَّبِّكَ عَطَاءً حِسَابًا

36. Sakamako daga Ubangijinka, kyauta mai yawa.

رَبِّ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ وَمَا بَيْنَهُمَا الرحْمَنِ لَا يَمْلِكُونَ مِنْهُ خِطَابًا

37. Ubangijin sammai da k'asa da abin da yake a tsakaninsu, Mai rahama, ba su da ikon yin wata magana daga gare Shi.

يَوْمَ يَقُومُ الرُّوحُ وَالْمَلَائِكَةُ صَفًّا لَّا يَتَكَلَّمُونَ إِلَّا مَنْ أَذِنَ لَهُ الرحْمَنُ وَقَالَ صَوَابًا

38. Ranar da Ruhi da mala'iku zasu tsaya a cikin sahu, ba sa magana, sai wanda Allah Ya yi masa izini, kuma ya fad'i abin da yake daidai.

ذَلِكَ الْيَوْمُ الْحَقُّ فَمَن شَاءَ اتَّخَذَ إِلَى رَبِّهِ مَآبًا

39. Wancan shi ne yini na gaskiya, to wanda ya so, ya rik'i makoma zuwa ga Ubangijinsa.

إِنَّا أَنذَرْنَاكُمْ عَذَابًا قَرِيبًا يَوْمَ يَنظُرُ الْمَرْءُ مَا قَدَّمَتْ يَدَاهُ وَيَقُولُ الْكَافِرُ يَا لَيْتَنِي كُنتُ تُرَابًا

40. Lalle ne, Mu, Mun yi muku gargad'in azaba makusanciya, ranar da mutum ke dubi zuwa ga abin da hannayensa suka aikata, kuma kafiri ya ce; Kaicona, da dai na zama turb'aya!

Surar Masu Fizga([3])

سورة النازعات

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ

Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin K'ai

وَالنَّازِعَاتِ غَرْقًا

1. Ina rantsuwa da mala'iku masu fisgar rayuka da k'arfi.

وَالنَّاشِطَاتِ نَشْطًا

2. Da masu d'aukar rayuka da sauk'i a cikin nishad'i.

وَالسَّابِحَاتِ سَبْحاً

3. Da masu sauka daga sama da umurnin Allah kamar suna iyo.

فَالسَّابِقَاتِ سَبْقًا

4. Sa'an nan, su zama masu gaugawa (da umurnin Allah) kamar suna tsere.

فَالْمُدَبِّرَاتِ أَمْرًا

5. Sa,an nan, su kasance masu shirya gudanar da umurni.

يَوْمَ تَرْجُفُ الرَّاجِفَةُ

6. Ranar da mai girgiza abubuwa (busar farko) za ta kad'a.

تَتْبَعُهَا الرَّادِفَةُ

7. Mai biyar ta (busa ta biyu) na biye.

قُلُوبٌ يَوْمَئِذٍ وَاجِفَةٌ

8. Wasu zukata, a ranar nan, masu jin tsoro ne.

أَبْصَارُهَا خَاشِعَةٌ

9. Alhali idanunsu na k'ask'antattu.

يَقُولُونَ أَئِنَّا لَمَرْدُودُونَ فِي الْحَافِرَةِ

10. Suna cewa; Ashe lalle za a iya mayar da mu a kan sawunmu?

أَئِذَا كُنَّا عِظَامًا نَّخِرَةً

11. Ashe, idan muka zama k'asusuwa rududdugaggu?

قَالُوا تِلْكَ إِذًا كَرَّةٌ خَاسِرَةٌ

12. Suka ce; Waccan kam komawa ce, tab'ab'b'iya!

فَإِنَّمَا هِيَ زَجْرَةٌ وَاحِدَةٌ

13. To, ita kam, tsawa guda kawai ce.

فَإِذَا هُم بِالسَّاهِرَةِ

14. Sai kawai ga su a bayan k'asa.

هَلْ أتَاكَ حَدِيثُ مُوسَى

15. Shin, labarin Musa ya zo maka?

إِذْ نَادَاهُ رَبُّهُ بِالْوَادِ الْمُقَدَّسِ طُوًى

16. A lokacin da Ubangijinsa Ya kiraye shi, a cikin kwari mai tsarki, wato D'uwa?

اذْهَبْ إِلَى فِرْعَوْنَ إِنَّهُ طَغَى

17. Ka tafi zuwa ga Fir'auna, lalle ne shi ya k'etare haddi.

فَقُلْ هَل لَّكَ إِلَى أَن تَزَكَّى

18. Sai ka ce masa, Ko za ka so ka tsarkaka.

وَأَهْدِيَكَ إِلَى رَبِّكَ فَتَخْشَى

19. Kuma in shiryar da kai zuwa ga Ubangijinka domin ka ji tsoronSa?

فَأَرَاهُ الْآيَةَ الْكُبْرَى

20. Sai ya nuna masa ayar nan mafi girma.

فَكَذَّبَ وَعَصَى

21. Sai ya k'aryata, kuma ya sab'a.

ثُمَّ أَدْبَرَ يَسْعَى

22. Sa'an nan ya juya baya, yana tafiya da sauri.

فَحَشَرَ فَنَادَى

23. Sai ya yi gayya, sa'an nan ya yi kira.

فَقَالَ أَنَا رَبُّكُمُ الْأَعْلَى

24. Sai ya ce; Ni ne Ubangijinku mafi d'aukaka.

فَأَخَذَهُ اللَّهُ نَكَالَ الْآخِرَةِ وَالْأُولَى

25. Saboda haka Allah Ya kama shi, domin azabar maganar k'arshe da ta farko.

إِنَّ فِي ذَلِكَ لَعِبْرَةً لِّمَن يَخْشَى

26. Lalle ne, a cikin wannan hak'ik'a akwai abin kula ga wanda yake tsoron Allah.

أَأَنتُمْ أَشَدُّ خَلْقًا أَمِ السَّمَاءَ بَنَاهَا

27. Shin, ku ne mafi wuyar halitta ko sama? Allah Ya gina ta.

رَفَعَ سَمْكَهَا فَسَوَّاهَا

28. Ya d'aukaka rufinta, sa'an nan Ya daidaita ta.

وَأَغْطَشَ لَيْلَهَا وَأَخْرَجَ ضُحَاهَا

29. Kuma Ya duhuntar da darenta, kuma Ya fitar da hantsinta.

وَالْأَرْضَ بَعْدَ ذَلِكَ دَحَاهَا

30. Kuma, k'asa a bayan haka Ya mulmula ta.

أَخْرَجَ مِنْهَا مَاءَهَا وَمَرْعَاهَا

31. Ya fitar da ruwanta daga gare ta da makiyayarta.

وَالْجِبَالَ أَرْسَاهَا

32. Da duwatsu, Ya kafe su.

مَتَاعًا لَّكُمْ وَلِأَنْعَامِكُمْ

33. Domin jiyarwar dad'i a gare ku, kuma ga dabbobinku.

فَإِذَا جَاءَتِ الطَّامَّةُ الْكُبْرَى

34. To, idan uwar masifu mafi girma, ta zo.

يَوْمَ يَتَذَكَّرُ الْإِنسَانُ مَا سَعَى

35. Ranar da mutum zai yi tunanin abin da ya aikata.

وَبُرِّزَتِ الْجَحِيمُ لِمَن يَرَى

36. Kuma, a bayyana Jahim ga mai gani.

فَأَمَّا مَن طَغَى

37. To, amma wanda ya yi girman kai.

وَآثَرَ الْحَيَاةَ الدُّنْيَا

38. Kuma, ya zab'i rayuwar duniya.

فَإِنَّ الْجَحِيمَ هِيَ الْمَأْوَى

39. To, hak'ik'a Jahim ita ce makoma.

وَأَمَّا مَنْ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِ وَنَهَى النَّفْسَ عَنِ الْهَوَى

40. Kuma, amma wanda ya ji tsoron tsayi a gaban Ubangijinsa, kuma ya kange kansa daga son rai.

فَإِنَّ الْجَنَّةَ هِيَ الْمَأْوَى

41. To, lalle ne Aljanna ita ce makoma.

يَسْأَلُونَكَ عَنِ السَّاعَةِ أَيَّانَ مُرْسَاهَا

42. Suna tambayar ka game da alk'iyama, wai yaushe ne matabbatarta?

فِيمَ أَنتَ مِن ذِكْرَاهَا

43. Me ya had'a ka da ambatonta?

إِلَى رَبِّكَ مُنتَهَاهَا

44. Zuwa ga Ubangijinka k'arshen al'amarinta yake.

إِنَّمَا أَنتَ مُنذِرُ مَن يَخْشَاهَا

45. Kai mai gargad'i kawai ne ga mai tsoronta.

كَأَنَّهُمْ يَوْمَ يَرَوْنَهَا لَمْ يَلْبَثُوا إِلَّا عَشِيَّةً أَوْ ضُحَاهَا

46. Kamar su a ranar da za su gan ta, ba su zauna ba face a lokacin marece ko hantsinta.

Surar Murtuke Fuska([4])

سورة عبس

Tana karantar da rashin bambanci tsakanin musulmi, rik'on addini da gaskiya shi ne d'aukaka, An ce wannan sura ta sauka ne lokaci da Abdullahi bn Maktum ya zo wajen Usman sai ya d'aure fuskarsa saboda yana makaho kuma mabuk'aci

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ

Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.

عَبَسَ وَتَوَلَّى

1. Ya had'a fuska kuma ya juya baya.

أَن جَاءَهُ الْأَعْمَى

2. Saboda makaho ya zo masa.

وَمَا يُدْرِيكَ لَعَلَّهُ يَزَّكَّى

3. To, me ya sanar da kai cewa watak'ila shi ne zai tsarkaka.

أَوْ يَذَّكَّرُ فَتَنفَعَهُ الذِّكْرَى

4. Ko ya tuna, sai tunawar ta amfane shi?

أَمَّا مَنِ اسْتَغْنَى

5. Amma wanda ya wadatu da dukiya.

فَأَنتَ لَهُ تَصَدَّى

6. Sa'an nan kai kuma ka bijira zuwa gare shi!

وَمَا عَلَيْكَ أَلَّا يَزَّكَّى

7. To, me zai cuce ka idan bai tsarkaka ba?

وَأَمَّا مَن جَاءَكَ يَسْعَى

8. Kuma, amma wanda ya zomaka yana gaugawa.

وَهُوَ يَخْشَى

9. Alhali shi yana jin tsoron Allah.

فَأَنتَ عَنْهُ تَلَهَّى

10. Kai kuma ka shagala ga barinsa!

كَلَّا إِنَّهَا تَذْكِرَةٌ

11. A'aha! Lalle ne, wannan tunatarwa ce.

فَمَن شَاء ذَكَرَهُ

12. Saboda wanda ya so ya tuna Shi.

فِي صُحُفٍ مُّكَرَّمَةٍ

13. A cikin littattafai ababan girmamawa.

مَّرْفُوعَةٍ مُّطَهَّرَةٍ

14. Ababan d'aukakawa, ababan tsarkakewa.

بِأَيْدِي سَفَرَةٍ

15. A hannayen mala'iku marubuta.

كِرَامٍ بَرَرَةٍ

16. Masu daraja, masu d'a'a ga Allah.

قُتِلَ الْإِنسَانُ مَا أَكْفَرَهُ

17. An la'ani mutum (kafiri), mamakin yawan kafircinsa!

مِنْ أَيِّ شَيْءٍ خَلَقَهُ

18. Daga wane abu, (Allah) Ya halitta shi?

مِن نُّطْفَةٍ خَلَقَهُ فَقَدَّرَهُ

19. Daga d'igon maniyyi, Ya halitta shi sa'an nan Ya k'addara shi.

ثُمَّ السَّبِيلَ يَسَّرَهُ

20. Sa'an nan Ya saukake masa hanyarsa.

ثُمَّ أَمَاتَهُ فَأَقْبَرَهُ

21. Sa'an nan, Ya matar da shi sai Ya sanya shi a cikin kabari.

ثُمَّ إِذَا شَاءَ أَنشَرَهُ

22. Sa'an nan, idan Ya so lalle ne zai tayar da shi.

كَلَّا لَمَّا يَقْضِ مَا أَمَرَهُ

23. Hak'ik'a bai wada aikata abin da (Allah) Ya umurce shi ba.

فَلْيَنظُرِ الْإِنسَانُ إِلَى طَعَامِهِ

24. To, mutum ya duba zuwa ga abincinsa.

أَنَّا صَبَبْنَا الْمَاءَ صَبًّا

25. Lalle ne Mu, Mun zubo ruwa, zubowa.

ثُمَّ شَقَقْنَا الْأَرْضَ شَقًّا

26. Sa'an nan, Muka tsattsage kasa tsattsagewa.

فَأَنبَتْنَا فِيهَا حَبًّا

27. Sa'an nan, Muka tsirar da k'waya ,a cikinta.

وَعِنَبًا وَقَضْبًا

28. Da inabi da ciyawa.

وَزَيْتُونًا وَنَخْلًا

29. Da zaituni da itacen dabino.

وَحَدَائِقَ غُلْبًا

30. Da lambuna, masu yawan itace.

وَفَاكِهَةً وَأَبًّا

31. Da 'ya'yan itacen marmari, da makiyaya ta dabbobi.

مَّتَاعًا لَّكُمْ وَلِأَنْعَامِكُمْ

32. Domin jin dad'i a gareku, ku da dabbobinku.

فَإِذَا جَاءَتِ الصَّاخَّةُ

33. To, idan mai tsawa (busa ta biyu) ta zo.

يَوْمَ يَفِرُّ الْمَرْءُ مِنْ أَخِيهِ

34. Ranar da mutum yake gudu daga dan'uwansa.

وَأُمِّهِ وَأَبِيهِ

35. Da uwarsa da ubansa.

وَصَاحِبَتِهِ وَبَنِيهِ

36. Da matarsa da d'iyansa.

لِكُلِّ امْرِئٍ مِّنْهُمْ يَوْمَئِذٍ شَأْنٌ يُغْنِيهِ

37. Ga kowane mutum daga cikinsu, a ranar nan akwai wani sha'ani da ya ishe shi.

وُجُوهٌ يَوْمَئِذٍ مُّسْفِرَةٌ

38. Wasu fuskoki, a ranar nan, masu haske ne.

ضَاحِكَةٌ مُّسْتَبْشِرَةٌ

39. Masu dariya ne, masu bushara.

وَوُجُوهٌ يَوْمَئِذٍ عَلَيْهَا غَبَرَةٌ

40. Wasu fuskoki, a ranar nan, akwai k'ura a kansu.

تَرْهَقُهَا قَتَرَةٌ

41. Bak'i zai rufe su.

أُوْلَئِكَ هُمُ الْكَفَرَةُ الْفَجَرَةُ

42. Wad'annan su ne kafirai fajirai.

Surar Kisfewa([5])

سورة التكوير

Tana karantar da Tashin kiyama gaskiya ne, kuma Kur'ani gaskiya ne, daga Allah yake, babu ragi babu kari, ya taho ta hannun aminci daga Allah zuwa ga Annabi.

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ

Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin K'ai

إِذَا الشَّمْسُ كُوِّرَتْ

1. Idan aka kisfe rana.

وَإِذَا النُّجُومُ انكَدَرَتْ

2. Kuma idan taurari suka gurb'ace.

وَإِذَا الْجِبَالُ سُيِّرَتْ

3. Kuma idan duwatsu aka tafiyar da su.

وَإِذَا الْعِشَارُ عُطِّلَتْ

4. Kuma idan rak'uma masu cikkuna aka sake su wawai.

وَإِذَا الْوُحُوشُ حُشِرَتْ

5. Kuma idan dabbobin daji aka tattara su.

وَإِذَا الْبِحَارُ سُجِّرَتْ

6. Kuma idan tekuna aka mayar da su wuta.

وَإِذَا النُّفُوسُ زُوِّجَتْ

7. Kuma idan rayuka aka aurar da su (ga matattu).

وَإِذَا الْمَوْؤُودَةُ سُئِلَتْ

8. Kuma idan wadda aka turbud'e ta da rai aka tambaye ta.

بِأَيِّ ذَنبٍ قُتِلَتْ

9. Saboda wane laifi ne aka kashe ta?

وَإِذَا الصُّحُفُ نُشِرَتْ

10. Kuma idan takardun ayyuka aka watsa su.

وَإِذَا السَّمَاءُ كُشِطَتْ

11. Kuma idan sama aka fed'e ta.

وَإِذَا الْجَحِيمُ سُعِّرَتْ

12. Kuma idan Jahim aka hura ta.

وَإِذَا الْجَنَّةُ أُزْلِفَتْ

13. Kuma idan Aljanna aka kusantar da ita.

عَلِمَتْ نَفْسٌ مَّا أَحْضَرَتْ

14. Rai ya san abin da ya halartar.

فَلَا أُقْسِمُ بِالْخُنَّسِ

15. To, ba sai Na yi rantsuwa da taurari matafa ba.

الْجَوَارِ الْكُنَّسِ

16. Masu gudu suna b'uya.

وَاللَّيْلِ إِذَا عَسْعَسَ

17. Da dare idan ya bayar da baya.

وَالصُّبْحِ إِذَا تَنَفَّسَ

18. Da safiya idan ta yi lumfashi.

إِنَّهُ لَقَوْلُ رَسُولٍ كَرِيمٍ

19. Lalle ne shi (Kur'ani), maganar wani manzo ne mai girma.

ذِي قُوَّةٍ عِندَ ذِي الْعَرْشِ مَكِينٍ

20. Mai k'arfi, mai daraja a wurin Mai Al'arshi.

مُطَاعٍ ثَمَّ أَمِينٍ

21. Wanda ake yi wa d'a'a ne, amintacce a can.

وَمَا صَاحِبُكُم بِمَجْنُونٍ

22. Kuma abokinku ba mahaukaci ba ne.

وَلَقَدْ رَآهُ بِالْأُفُقِ الْمُبِينِ

23. Kuma lalle ne, ya gan shi a cikin sararin sama mabayyani.

وَمَا هُوَ عَلَى الْغَيْبِ بِضَنِينٍ

24. Kuma shi, ga gaibi ba mai rowa ba ne.

وَمَا هُوَ بِقَوْلِ شَيْطَانٍ رَجِيمٍ

25. Kuma shi ba maganar shed'ni abin la'ana, ba ce.

فَأَيْنَ تَذْهَبُونَ

26. Shin, to ina za ku tafi?

إِنْ هُوَ إِلَّا ذِكْرٌ لِّلْعَالَمِينَ

27. Lalle ne shi ba komai ba ne sai ambato ga talikai.

لِمَن شَاءَ مِنكُمْ أَن يَسْتَقِيمَ

28. Ga wanda ya so daga cikinku, ya shiryu.

وَمَا تَشَاؤُونَ إِلَّا أَن يَشَاء اللَّهُ رَبُّ الْعَالَمِينَ

29. Kuma ba zaku so ba sai idan Allah Ubangijin talikai ya yarda.

سورة الإنفطار

Surar Tsagewa ([6])

Tana karantar da gaskiyar Tashin Kiyama, kuma ayyukan mutum na duniya ana tsare da su domin hisabi da sakamako.

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ

Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin K'ai

إِذَا السَّمَاءُ انفَطَرَتْ

1. Idan sama ta tsage.

وَإِذَا الْكَوَاكِبُ انتَثَرَتْ

2. Kuma idan taurari suka watse.

وَإِذَا الْبِحَارُ فُجِّرَتْ

3. Kuma idan tekuna aka facce su.

وَإِذَا الْقُبُورُ بُعْثِرَتْ

4. Kuma idan kaburbura aka tone su.

عَلِمَتْ نَفْسٌ مَّا قَدَّمَتْ وَأَخَّرَتْ

5. Rai ya san abin da ya gabatar, da abin da ya jinkirtar.

يَا أَيُّهَا الْإِنسَانُ مَا غَرَّكَ بِرَبِّكَ الْكَرِيمِ

6. Ya kai mutum! Me ya ruء e ka game da Ubangijinka, Mai karimci.

الَّذِي خَلَقَكَ فَسَوَّاكَ فَعَدَلَكَ

7. Wanda Ya halitta ka sa'an nan ya daidaita ka, Ya kuma tsakaita ka.

فِي أَيِّ صُورَةٍ مَّا شَاءَ رَكَّبَكَ

8. Ya gina ka a kan kowace irin sura Ya so.

كَلَّا بَلْ تُكَذِّبُونَ بِالدِّينِ

9. A'aha, ba haka ba, kuna k'aryatawa game da sakamako!ٍ

وَإِنَّ عَلَيْكُمْ لَحَافِظِينَ

10. Lalle ne akwai matsara a kanku.

كِرَامًا كَاتِبِينَ

11. Masu daraja, marubuta.

يَعْلَمُونَ مَا تَفْعَلُونَ

12. Suna sanin abin da kuke aikatawa.

إِنَّ الْأَبْرَارَ لَفِي نَعِيمٍ

13. Lalle ne, masu d'a'a ga Allah suna cikin ni'ima.

وَإِنَّ الْفُجَّارَ لَفِي جَحِيمٍ

14. Kuma lalle ne, fajirai, suna cikin Jahim.

يَصْلَوْنَهَا يَوْمَ الدِّينِ

15. Za su shige ta a ranar sakamako.

وَمَا هُمْ عَنْهَا بِغَائِبِينَ

16. Ba za su faku daga gare ta ba.

وَمَا أَدْرَاكَ مَا يَوْمُ الدِّينِ

17. Kuma me ya sanar da kai abin da ake ce wa ranar sakamako?

ثُمَّ مَا أَدْرَاكَ مَا يَوْمُ الدِّينِ

18. Sa'an nan, me ya sanar da kai abin da ake ce wa ranar sakamako?

يَوْمَ لَا تَمْلِكُ نَفْسٌ لِّنَفْسٍ شَيْئًا وَالْأَمْرُ يَوْمَئِذٍ لِلَّهِ

19. Rana ce da wani rai ba ya iya mallakar komai domin wani rai, al'amari a ranar nan ga Allah yake.

Surar Masu Tauye Awo([7])

سورة المطففين

Tana karantar da wajabcin tsare hak'k'ok'in mutane tsakaninsu a ciniki da wasu mu'amalolin zamantakewa.

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ

Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin K'ai

وَيْلٌ لِّلْمُطَفِّفِينَ

1. Bone ya tabbata ga masu tauyewa.

الَّذِينَ إِذَا اكْتَالُواْ عَلَى النَّاسِ يَسْتَوْفُونَ

2. Wadanda suke idan suka auna daga mutane suna cika mudu.

وَإِذَا كَالُوهُمْ أَو وَّزَنُوهُمْ يُخْسِرُونَ

3. Kuma idan sun auna musu awon kwano ko awon sikeli, suna ragewa.

أَلَا يَظُنُّ أُولَئِكَ أَنَّهُم مَّبْعُوثُونَ

4. Ashe! Wad'ancan ba sa tsammanin cewa tabbas ana tayar da su ba?

لِيَوْمٍ عَظِيمٍ

5. Domin yini mai girma.

يَوْمَ يَقُومُ النَّاسُ لِرَبِّ الْعَالَمِينَ

6. Yinin da mutane ke tashi zuwa ga Ubangijin halitta?

كَلَّا إِنَّ كِتَابَ الفُجَّارِ لَفِي سِجِّينٍ

7. A'aha! Hak'ik'a littafin fajirai tabbas yana a cikin Sijjin.

وَمَا أَدْرَاكَ مَا سِجِّينٌ

8. Kuma, me ya sanar da kai abin da ake ce wa Sijjin?

كِتَابٌ مَّرْقُومٌ

9. Wani 1ittafi ne rubutacce.

وَيْلٌ يَوْمَئِذٍ لِّلْمُكَذِّبِينَ

10. Bone ya tabbata a ranar nan ga masu k'aryatawa.

الَّذِينَ يُكَذِّبُونَ بِيَوْمِ الدِّينِ

11. Wad'anda suke k'aryatawa game da ranar sakamako.

وَمَا يُكَذِّبُ بِهِ إِلَّا كُلُّ مُعْتَدٍ أَثِيمٍ

12. Babu mai k'aryatawa da ita sai dukkan mai k'etare haddi mai yawan zunubi.

إِذَا تُتْلَى عَلَيْهِ آيَاتُنَا قَالَ أَسَاطِيرُ الْأَوَّلِينَ

13. Idan ana karanta masa ayoyinmu, sai ya ce: Tatsuniyoyin mutanen farko ne.

كَلَّا بَلْ رَانَ عَلَى قُلُوبِهِم مَّا كَانُوا يَكْسِبُونَ

14. A'aha! Ba haka ba, abin da suka kasance suna aikatawa dai, ya yi tsatsa a cikin zukatansu.

كَلَّا إِنَّهُمْ عَن رَّبِّهِمْ يَوْمَئِذٍ لَّمَحْجُوبُونَ

15. A'aha! Hak'ik'a, su wad'anda ake shamakancewa daga Ubangijinsu ne a wannan ranar.

ثُمَّ إِنَّهُمْ لَصَالُوا الْجَحِيمِ

16. Sa'an nan, lalle ne, su masu shiga cikin Jahim ne.

ثُمَّ يُقَالُ هَذَا الَّذِي كُنتُم بِهِ تُكَذِّبُونَ

17. Sannan a ce; Wannan shi ne abin da kuka kasance kuna k'aryatawa da shi.

كَلَّا إِنَّ كِتَابَ الْأَبْرَارِ لَفِي عِلِّيِّينَ

18. A'aha! Hak'ik'a littafin masu d'a'a yana a cikin Illiyyina?

وَمَا أَدْرَاكَ مَا عِلِّيُّونَ

19. Kuma mene ne ya sanar da kai abin da ake cewa Illiyyuna?

كِتَابٌ مَّرْقُومٌ

20. Wani littafi ne rubutacce.

يَشْهَدُهُ الْمُقَرَّبُونَ

21. Mukarrabai ne suke halartar sa.

إِنَّ الْأَبْرَارَ لَفِي نَعِيمٍ

22. Hak'ik'a masu d'a'a suna cikin ni'ima.

عَلَى الْأَرَائِكِ يَنظُرُونَ

23. A kan karagu, suna ta kallo.

تَعْرِفُ فِي وُجُوهِهِمْ نَضْرَةَ النَّعِيمِ

24. Kana sanin walwalin ni'ima a fuskokinsu.

يُسْقَوْنَ مِن رَّحِيقٍ مَّخْتُومٍ

25. Ana shayar da su daga wata giya wadda aka yunk'e a kan rufinta.

خِتَامُهُ مِسْكٌ وَفِي ذَلِكَ فَلْيَتَنَافَسِ الْمُتَنَافِسُونَ

26. K'arshen kurb'inta al'miski ne. To, a cikin wannan, masu rige su yi ta rige.

وَمِزَاجُهُ مِن تَسْنِيمٍ

27. Kuma abin da ake gauraya ta da shi, daga tasnim yake.

عَيْنًا يَشْرَبُ بِهَا الْمُقَرَّبُونَ

28. Wani marmaro ne wanda muk'arrabai suke sha daga gare shi.

إِنَّ الَّذِينَ أَجْرَمُوا كَانُواْ مِنَ الَّذِينَ آمَنُوا يَضْحَكُونَ

29. Lalle ne, wad'anda suka kafirta sun kasance suna yi wa wad'anda suka yi imani dariya.

وَإِذَا مَرُّواْ بِهِمْ يَتَغَامَزُونَ

30. Kuma idan sun shud'e su sai su dinga yin zund'e.

وَإِذَا انقَلَبُواْ إِلَى أَهْلِهِمُ انقَلَبُواْ فَكِهِينَ

31. Kuma idan suka juya zuwa ga iyalansu, sai su tafi suna kakaci.

وَإِذَا رَأَوْهُمْ قَالُوا إِنَّ هَؤُلَاءِ لَضَالُّونَ

32. Kuma idan sun gan su sai su ce; Lalle wad'annan b'atattu ne.

وَمَا أُرْسِلُوا عَلَيْهِمْ حَافِظِينَ

33. Alhali kuwa, ba a aike su ba domin su zama masu lura da su.

فَالْيَوْمَ الَّذِينَ آمَنُواْ مِنَ الْكُفَّارِ يَضْحَكُونَ

34. To, yau fa wad'anda suka yi imani, su ne suke yi wa kafirai dariya.

عَلَى الْأَرَائِكِ يَنظُرُونَ

35. Suna masu kallo a kan karagu.

هَلْ ثُوِّبَ الْكُفَّارُ مَا كَانُوا يَفْعَلُونَ

36. Shin an saka wa kafirai abin da suka kasance suna aikatawa?

Surar Kecewa([8])

سورة الإنشقاق

Tana karantar da tabbatar Tashin K'iyama, kuma duka abin da ake aikatawa idan ba na tattalin K'iyamar ba ne, to, ya zama wahalar da kai, maras amfani, da b'ata lokaci.

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ

Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin K'ai

إِذَا السَّمَاءُ انشَقَّتْ

1. Idan sama ta kece.

وَأَذِنَتْ لِرَبِّهَا وَحُقَّتْ

2. Ta saurari Ubangijinta, kuma aka wajabta mata yin sauraron.

وَإِذَا الْأَرْضُ مُدَّتْ

3. Kuma idan k'asa aka mike ta.

وَأَلْقَتْ مَا فِيهَا وَتَخَلَّتْ

4. Kuma ta jefar da abin da yake a cikinta, ta wofinta daga kome.

وَأَذِنَتْ لِرَبِّهَا وَحُقَّتْ

5. Kuma ta saurari Ubangijinta, aka wajabta mata yin sauraren.

يَا أَيُّهَا الْإِنسَانُ إِنَّكَ كَادِحٌ إِلَى رَبِّكَ كَدْحًا فَمُلَاقِيهِ

6. Ya kai mutum! Lalle ne kai mai aikin wahalar da kai ne zuwa ga Ubangijinka, wahala mai tsanani, kuma kai mai had'uwa da Shi ne.

فَأَمَّا مَنْ أُوتِيَ كِتَابَهُ بِيَمِينِه

7. To, amma wanda aka bai wa littafinsa a damansa.

فَسَوْفَ يُحَاسَبُ حِسَابًا يَسِيرًا

8. To, za a yi masa hisabi, hisabi mai sauk'i.

وَيَنقَلِبُ إِلَى أَهْلِهِ مَسْرُورًا

9. Kuma ya juya zuwa ga iyalinsa yana mai raha.

وَأَمَّا مَنْ أُوتِيَ كِتَابَهُ وَرَاءَ ظَهْرِهِ

10. Kuma amma wanda aka bai wa littafinsa, daga wajen bayansa.

فَسَوْفَ يَدْعُو ثُبُورًا

11. To, zai dinga kiran halaka!

وَيَصْلَى سَعِيرًا

12. Kuma ya shiga sa'ir.

إِنَّهُ كَانَ فِي أَهْلِهِ مَسْرُورًا

13. Lal1e ne shi, ya kasance a cikin iyalinsa yana mai raha.

إِنَّهُ ظَنَّ أَن لَّن يَحُورَ

14. Lalle ne ya yi zaton ba zai komo ba.

بَلَى إِنَّ رَبَّهُ كَانَ بِهِ بَصِيرًا

15. Na'am! Hak'ik'a Ubangijinsa Ya kasance Mai gani gare shi.

فَلَا أُقْسِمُ بِالشَّفَقِ

16. To, ba sai Na rantse da shafak'i ba.

وَاللَّيْلِ وَمَا وَسَقَ

17. Da dare, da abin da ya k'unsa.

وَالْقَمَرِ إِذَا اتَّسَقَ

18. Da wata idan ya cika.

لَتَرْكَبُنَّ طَبَقًا عَن طَبَقٍ

19. Lalle ne kuna hawan wani hali daga wani halin.

فَمَا لَهُمْ لَا يُؤْمِنُونَ

20. To, me ya same su, ba sa yin imani?

وَإِذَا قُرِئَ عَلَيْهِمُ الْقُرْآنُ لَا يَسْجُدُونَ

21. Kuma idan an karanta Kur'ani garesu ba sa k'ask'an da kai?

بَلِ الَّذِينَ كَفَرُواْ يُكَذِّبُونَ

22. Ba haka ba! wad'anda suka kafirta, sai k'aryatawa suke yi.

وَاللَّهُ أَعْلَمُ بِمَا يُوعُونَ

23. Alhali Allah Shi ne Mafi sani ga abin a suke tarawa.

فَبَشِّرْهُم بِعَذَابٍ أَلِيمٍ

24. Saboda haka, ka yi musu bushara da azaba mai rad'ad'i.

إِلَّا الَّذِينَ آمَنُواْ وَعَمِلُواْ الصَّالِحَاتِ لَهُمْ أَجْرٌ غَيْرُ مَمْنُونٍ

25. Sai dai wad'anda suka yi imani, suka aikata ayyukan k'warai, suna da wani sakamako wanda ba ya yankewa.

Surar Taurari([9])

سورة البروج

Tana bayanin mugunyar ak'ibar masu wahalar da muminai a kan addininsu, ba da wata hujja ba ta shari'a

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ

Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin K'ai

وَالسَّمَاءِ ذَاتِ الْبُرُوجِ

1. Ina rantsuwa da sama mai taurarin lissafin shekara.

وَالْيَوْمِ الْمَوْعُودِ

2. Da yinin da aka yi alk'awarin zuwansa.

وَشَاهِدٍ وَمَشْهُودٍ

3. Da yini mai shaidu, da yini da ake halarta.

قُتِلَ أَصْحَابُ الْأُخْدُودِ

4. An la'ani mutanen rami.

النَّارِ ذَاتِ الْوَقُودِ

5. Wuta ce wacce aka hura.

إِذْ هُمْ عَلَيْهَا قُعُودٌ

6. A lokacin da suke a gefenta a zazzaune.

وَهُمْ عَلَى مَا يَفْعَلُونَ بِالْمُؤْمِنِينَ شُهُودٌ

7. Alhali su, bisa ga abin da suke aikatawa ga muminai, suna halarce.

وَمَا نَقَمُوا مِنْهُمْ إِلَّا أَن يُؤْمِنُوا بِاللَّهِ الْعَزِيزِ الْحَمِيدِ

8. Kuma ba su azabtar da su ba, sai kawai domin sun yi imani da Allah Mabuwayi, abin godewa.

الَّذِي لَهُ مُلْكُ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ وَاللَّهُ عَلَى كُلِّ شَيْءٍ شَهِيدٌ

9. Wanda Yake shi ne da mulkin sammai da k'asa, kuma Allah a kan kome halarce Yake.

إِنَّ الَّذِينَ فَتَنُوا الْمُؤْمِنِينَ وَالْمُؤْمِنَاتِ ثُمَّ لَمْ يَتُوبُوا فَلَهُمْ عَذَابُ جَهَنَّمَ وَلَهُمْ عَذَابُ الْحَرِيقِ

10. Lalle ne wad'anda suka fitini muminai maza da muminai mata, sa'an nan ba su tuba ba, to suna da azabar Jahannama, kuma suna da azabar gobara.

إِنَّ الَّذِينَ آمَنُوا وَعَمِلُوا الصَّالِحَاتِ لَهُمْ جَنَّاتٌ تَجْرِي مِن تَحْتِهَا الْأَنْهَارُ ذَلِكَ الْفَوْزُ الْكَبِيرُ

11. Lalle ne wad'anda suka yi imani, kuma suka aikata ayyukan k'warai suna da gidajen Aljanna, k'oramu suna gudana daga k'ark'ashinsu, wancan abu fa shi ne rabo babba.

إِنَّ بَطْشَ رَبِّكَ لَشَدِيدٌ

12. Hak'ik'a damk'ar Ubangijinka mai tsanani ce k'warai.

إِنَّهُ هُوَ يُبْدِئُ وَيُعِيدُ

13. Hak'ik'a shi ne Mai k'aga halitta, kuma Ya mayar da ita.

وَهُوَ الْغَفُورُ الْوَدُودُ

14. Kuma Shi ne Mai gafara, Mai bayyana soyayya.

ذُو الْعَرْشِ الْمَجِيدُ

15. Mai Al'arshi mai girma

فَعَّالٌ لِّمَا يُرِيدُ

16. Mai aikatawa ga abin da Yake nufi.

هَلْ أَتَاكَ حَدِيثُ الْجُنُودِ

17. Ko labarin rundanoni ya zo maka.

فِرْعَوْنَ وَثَمُودَ

18. Fir'auna da samudawa?

بَلِ الَّذِينَ كَفَرُوا فِي تَكْذِيبٍ

19. A'aha! wad'anda suka kafirta suna cikin k'aryatawa.

وَاللَّهُ مِن وَرَائِهِم مُّحِيطٌ

20. Alhali, Allah Mai kewaye daga bayansu ne.

بَلْ هُوَ قُرْآنٌ مَّجِيدٌ

21. A'aha! Shi Kur'ani ne mai girma.

فِي لَوْحٍ مَّحْفُوظٍ

22. A cikin Allo tsararre.

Ma'abota Rami: Ko kuma Mutanen Rami: Su ne mutanen Najiran da suka yi rami suka hura wuta a ciki, domin su k'one wanda ya yi imani da addinin Masih Isa domin su hana yad'uwarsa. Suka umurci kowane Musulmi ya jefa kansa a ciki, su kuma suna zazzaune suna kallo.