• Farawa
  • Na Baya
  • 41 /
  • Na Gaba
  • Karewa
  •  
  • Gurzawa HTML
  • Gurzawa Word
  • Gurzawa PDF
  • Budawa: 4158 / Gurzawa: 1589
Girma Girma Girma
Fassarar Kur'ani

Fassarar Kur'ani

Mawallafi:
Hausa

Surar Mai Aukowa([10])

سورة الطارق

Tana karantar da tsaron Al1ah ga kome bisa ga tsari, kuma kome asirinsa ne, sannan duk masu kaidi su sani cewa; Allah yana nan a madakata

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ

Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin K'ai

وَالسَّمَاءِ وَالطَّارِقِ

1. Ina rantsuwa da sama da mai aukowa da dare.

وَمَا أَدْرَاكَ مَا الطَّارِقُ

2. To, me ya sanar da kai abin da ake cewa mai aukowa da dare?

النَّجْمُ الثَّاقِبُ

3. Shi ne tauraron nan mai tsananin haske.

إِن كُلُّ نَفْسٍ لَّمَّا عَلَيْهَا حَافِظٌ

4. Babu wani rai face a kansa akwai wani mai tsaro.

فَلْيَنظُرِ الْإِنسَانُ مِمَّ خُلِقَ

5. To, mutum ya duba, daga me aka halitta shi?

خُلِقَ مِن مَّاء دَافِقٍ

6. An halitta shi daga wani ruwa mai tunkud'ar juna.

يَخْرُجُ مِن بَيْنِ الصُّلْبِ وَالتَّرَائِبِ

7. Yana fita daga tsakanin tsatso da karankarman k'irji.

إِنَّهُ عَلَى رَجْعِهِ لَقَادِرٌ

8. Lalle ne Shi (Allah), ga mayar da shi (mutum), tabbas Mai iyawa ne.

يَوْمَ تُبْلَى السَّرَائِرُ

9. Ranar da ake jarrabawar asirai.

فَمَا لَهُ مِن قُوَّةٍ وَلَا نَاصِرٍ

10. Saboda haka, ba shi da wani karfi, kuma ba shi da wani mai taimako.

وَالسَّمَاءِ ذَاتِ الرَّجْعِ

11. Ina rantsuwa da sama ma'abuciyar ruwa mai komawa yana yankewa.

وَالْأَرْضِ ذَاتِ الصَّدْعِ

12. Da k'asa ma'abuciyar tsagewa.

إِنَّهُ لَقَوْلٌ فَصْلٌ

13. Hak'ik'a shi magana ce dalla-dalla (daki-daki).

وَمَا هُوَ بِالْهَزْلِ

14. Kuma shi ba bananci (kakaci da raha) ba ne.

إِنَّهُمْ يَكِيدُونَ كَيْدًا

15. Lalle ne su, suna k'ulla kaidi na sosai.

وَأَكِيدُ كَيْدًا

16. Kuma Ni, Ina (mayar da) kaidi sosai.

فَمَهِّلِ الْكَافِرِينَ أَمْهِلْهُمْ رُوَيْدًا

17. Saboda haka, ka yi wa kafirai jinkiri, ka dakata musu, sannu-sannu.

Surar Mafi D'aukaka([11])

سورة الأعلى

Tana karantar da cewa rayarwa da matarwa a hannun Allah suke, su kuma nau'i-nau'i ne

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ

Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin K'ai

سَبِّحِ اسْمَ رَبِّكَ الْأَعْلَى

1. Ka tsarkake sunan Ubangijinka Mafi d'aukaka.

الَّذِي خَلَقَ فَسَوَّى

2. Wanda Ya yi halitta sa'an nan Ya daidaita abin halittar.

وَالَّذِي قَدَّرَ فَهَدَى

3. Kuma Wanda Ya k'addara (abin da ya so) sannan Ya shiryar.

وَالَّذِي أَخْرَجَ الْمَرْعَى

4. Kuma Wanda Ya fitar da makiyaya.

فَجَعَلَهُ غُثَاءً أَحْوَى

5. Sa'an nan Ya mayar da ita k'ek'asassa, bak'a.

سَنُقْرِؤُكَ فَلَا تَنسَى

6. Za mu karantar da kai, saboda haka ba za ka manta ba.

إِلَّا مَا شَاءَ اللَّهُ إِنَّهُ يَعْلَمُ الْجَهْرَ وَمَا يَخْفَى

7. Face abin da Allah Ya so, lalle ne Shi (Allah) Ya san bayyane da abin da yake b'oye.

وَنُيَسِّرُكَ لِلْيُسْرَى

8. Kuma za Mu sauk'ak'e maka zuwa ga mai sauk'i.

فَذَكِّرْ إِن نَّفَعَتِ الذِّكْرَى

9. Saboda baka, ka tunatar, idan tunatarwa za ta yi amfani.

سَيَذَّكَّرُ مَن يَخْشَى

10. Wanda yake tsoron (Allah) Zai tuna.

وَيَتَجَنَّبُهَا الْأَشْقَى

11. Kuma shak'iyyi, zai nisanceta.

الَّذِي يَصْلَى النَّارَ الْكُبْرَى

12. Wanda zai shiga wuta mafi girma.

ثُمَّ لَا يَمُوتُ فِيهَا وَلَا يَحْيَى

13. Sa'an nan ba zai mutu ba a cikinta, kuma ba zai rayu ba.

قَدْ أَفْلَحَ مَن تَزَكَّى

14. Lalle ne wanda ya tsarkaka ya samu babban rabo.

وَذَكَرَ اسْمَ رَبِّهِ فَصَلَّى

15. Kuma ya ambaci sunan Ubangijinsa, sa'an nan ya yi salla.

بَلْ تُؤْثِرُونَ الْحَيَاةَ الدُّنْيَا

16. Ba haka ba! Kuna dai zab'in rayuwar duniya ne.

وَالْآخِرَةُ خَيْرٌ وَأَبْقَى

17. Alhalin Lahira ita ce mafi alheri kuma mafi wanzuwa.

إِنَّ هَذَا لَفِي الصُّحُفِ الْأُولَى

18. Hak'ik'a wannan yana cikin littattafan farko.

صُحُفِ إِبْرَاهِيمَ وَمُوسَى

19. Littattafan Ibrahim da Musa.

Surar Mai Rufewa([12])

سورة الغاشية

Tana karantar da yin hujja da abin da ake iya gani da ido domin a fahimci abin da ake gani da hankali, gwargwadon tunanin abokin magana.

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ

Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin K'ai

هَلْ أَتَاكَ حَدِيثُ الْغَاشِيَةِ

1. Shin labarin (K'iyama) mai rufe (mutane da tsoronta) ya zo maka?

وُجُوهٌ يَوْمَئِذٍ خَاشِعَةٌ

2. Wasu fuskoki a ranar nan k'ask'antattu ne.

عَامِلَةٌ نَّاصِبَةٌ

3. Masu aikin wahala ne, masu gajiya.

تَصْلَى نَارًا حَامِيَةً

4. Za su shiga wata wuta mai zafi.

تُسْقَى مِنْ عَيْنٍ آنِيَةٍ

5. Ana shayar da su daga wani marmaro mai zafin ruwa.

لَّيْسَ لَهُمْ طَعَامٌ إِلَّا مِن ضَرِيعٍ

6. Ba su da wani abinci face dai daga danyi.

لَا يُسْمِنُ وَلَا يُغْنِي مِن جُوعٍ

7. Ba ya sanya k'iba, kuma ba ya wadatarwa daga yunwa.

وُجُوهٌ يَوْمَئِذٍ نَّاعِمَةٌ

8. Wasu fuskoki a ranar nan masu ni'ima ne.

لِسَعْيِهَا رَاضِيَةٌ

9. Masu yarda ne game da aikinsu.

فِي جَنَّةٍ عَالِيَةٍ

10. A cikin Aljanna mad'aukakiya.

لَّا تَسْمَعُ فِيهَا لَاغِيَةً

11. Ba za su ji yasassar magana ba, a cikinta.

فِيهَا عَيْنٌ جَارِيَةٌ

12. A cikinta akwai marmaro mai gudana.

فِيهَا سُرُرٌ مَّرْفُوعَةٌ

13. A cikinta akwai gadaje mad'aukaka.

وَأَكْوَابٌ مَّوْضُوعَةٌ

14. Da kofuna ar'aje.

وَنَمَارِقُ مَصْفُوفَةٌ

15. Da filoli (matasan kai) a jere.

وَزَرَابِيُّ مَبْثُوثَةٌ

16. Da katifu shimfid'e.

أَفَلَا يَنظُرُونَ إِلَى الْإِبِلِ كَيْفَ خُلِقَتْ

17. Ashe to ba zasu yi duba ga rakuma ba yadda aka halitta su?

وَإِلَى السَّمَاءِ كَيْفَ رُفِعَتْ

18. Da zuwa ga sama yadda aka daukaka ta?

وَإِلَى الْجِبَالِ كَيْفَ نُصِبَتْ

19. Da zuwa ga duwatsu yadda aka kafa su?

وَإِلَى الْأَرْضِ كَيْفَ سُطِحَتْ

20. Da zuwa ga k'asa yadda aka shimfid'a ta?

فَذَكِّرْ إِنَّمَا أَنتَ مُذَكِّرٌ

21. Saboda haka, ka yi wa'azi, kai mai yin wa'azi ne kawai.

لَّسْتَ عَلَيْهِم بِمُصَيْطِرٍ

22. Kai ba mai tankwasawa a kansu ba ne.

إِلَّا مَن تَوَلَّى وَكَفَرَ

23. Sai dai duk wanda ya juya baya, kuma ya kafirta.

فَيُعَذِّبُهُ اللَّهُ الْعَذَابَ الْأَكْبَرَ

24. To, Allah zai yi masa azaba, azabar nan da take mafi girma.

إِنَّ إِلَيْنَا إِيَابَهُمْ

25. Lalle ne, zuwa gare Mu komowarsu take.

ثُمَّ إِنَّ عَلَيْنَا حِسَابَهُمْ

26. Sa'an nan lalle ne aikinMu ne Mu yi musu hisabi.

Surar Alfijir([13])

سورة الفجر

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ

Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin K'ai

وَالْفَجْرِ

1. Ina rantsuwa da alfijiri.

وَلَيَالٍ عَشْرٍ

2. Da darare goma.

وَالشَّفْعِ وَالْوَتْرِ

3. Da (adadi na) cika da (na) mara.

وَاللَّيْلِ إِذَا يَسْرِ

4. Da dare idan yana shud'ewa.

هَلْ فِي ذَلِكَ قَسَمٌ لِّذِي حِجْرٍ

5. Ko a cikin wad'annan akwai abin rantsuwa ga mai hankali.

أَلَمْ تَرَ كَيْفَ فَعَلَ رَبُّكَ بِعَادٍ

6. Ba ka ga yadda Ubangijinka Ya aikata da Adawa ba?

إِرَمَ ذَاتِ الْعِمَادِ

7. Iramawa masu sakon k'irar jiki.

الَّتِي لَمْ يُخْلَقْ مِثْلُهَا فِي الْبِلَادِ

8. Wad'anda ba a halitta kwatankwacinsu ba a cikin garuruwa.

وَثَمُودَ الَّذِينَ جَابُوا الصَّخْرَ بِالْوَادِ

9. Da samudawa wad'anda suka fasa duwatsu a cikin Wadi.

وَفِرْعَوْنَ ذِي الْأَوْتَادِ

10. Da Fir'auna mai turaku.

الَّذِينَ طَغَوْا فِي الْبِلَادِ

11. Wad'anda suka k'etare iyakarsu, a cikin garuruwa.

فَأَكْثَرُوا فِيهَا الْفَسَادَ

12. Sai suka yawaita yin b'arna a cikinsu.

فَصَبَّ عَلَيْهِمْ رَبُّكَ سَوْطَ عَذَابٍ

13. Saboda haka Ubangijinka Ya zuba musu bulalar azaba.

إِنَّ رَبَّكَ لَبِالْمِرْصَادِ

14. Lalle ne, Ubangijinka Yana nan a mafaka.

فَأَمَّا الْإِنسَانُ إِذَا مَا ابْتَلَاهُ رَبُّهُ فَأَكْرَمَهُ وَنَعَّمَهُ فَيَقُولُ رَبِّي أَكْرَمَنِ

15. To, amma fa mutum idan Ubangijibsa Ya jarraba shi, wato Ya girmama shi kuma Ya yi masa ni'ima, sai ya ce; Ubangijina Ya girmama ni.

وَأَمَّا إِذَا مَا ابْتَلَاهُ فَقَدَرَ عَلَيْهِ رِزْقَهُ فَيَقُولُ رَبِّي أَهَانَنِ

16. Kuma idan Ya jarraba shi, wato Ya k'untata masa arzikinsa, sai ya ce; Ubangijina Ya wulak'anta ni.

كَلَّا بَل لَّا تُكْرِمُونَ الْيَتِيمَ

17. A'aha! Bari wannan, ai ba kwa girmama maraya!

وَلَا تَحَاضُّونَ عَلَى طَعَامِ الْمِسْكِينِ

18. Ba kwa kwad'aita wa junanku ga (tattalin) abincin matalauci!

وَتَأْكُلُونَ التُّرَاثَ أَكْلًا لَّمًّا

19. Kuma kuna cin dukiyar gado, ci na tarawa.

وَتُحِبُّونَ الْمَالَ حُبًّا جَمًّا

20. Kuma kuna son dukiya, so mai yawa.

كَلَّا إِذَا دُكَّتِ الْأَرْضُ دَكًّا دَكًّا

21. A'aha! Idan aka nik'e k'asa nik'ewa sosai.

وَجَاء رَبُّكَ وَالْمَلَكُ صَفًّا صَفًّا

22. Kuma Ubangijinka Ya zo, alhali mala'iku na jere, safu- safu.

وَجِيءَ يَوْمَئِذٍ بِجَهَنَّمَ يَوْمَئِذٍ يَتَذَكَّرُ الْإِنسَانُ وَأَنَّى لَهُ الذِّكْرَى

23. Kuma a ranar nan aka zo da Jahannama. A ranar nan mutum zai yi tunani. To, ina fa tunani yake a gare shi!

يَقُولُ يَا لَيْتَنِي قَدَّمْتُ لِحَيَاتِي

24. Yana dinga cewa, Kaicona, ina ma dai na gabatar (da aikin k'warai) domin rayuwata!

فَيَوْمَئِذٍ لَّا يُعَذِّبُ عَذَابَهُ أَحَدٌ

25. To, a ranar nan babu wani mai yin azaba irin azabar Allah.

وَلَا يُوثِقُ وَثَاقَهُ أَحَدٌ

26. Kuma babu wani mai d'auri irin d'aurinSa.

يَا أَيَّتُهَا النَّفْسُ الْمُطْمَئِنَّةُ

27. Ya kai rai mai natsuwa!

ارْجِعِي إِلَى رَبِّكِ رَاضِيَةً مَّرْضِيَّةً

28. Ka koma zuwa ga Ubangijinka, alhali kana mai yarda, abin yardarwa.

فَادْخُلِي فِي عِبَادِي

29. Sabobda haka, ka shiga cikin .

وَادْخُلِي جَنَّتِي

30. Kuma ka shiga Aljannata.

Wadi: Shi ne "Wadil-kura" sunan wuri ne a k'asar Siriya "Sham".

Surar Gari([14])

سورة البلد

Tana karantar da cewa mutum an halitta shi cikin wahala, komai amfaninsa idan ya bi umurnin Allah ko kuma cutarsa idan ya sab'a wa umurnin Allah

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ

Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin K'ai

لَا أُقْسِمُ بِهَذَا الْبَلَدِ

1. Ba sai Na yi rantsuwa da wannan gari ba.

وَأَنتَ حِلٌّ بِهَذَا الْبَلَدِ

2. Da kuma kai kana mai sauka a cikin wannan gari.

وَوَالِدٍ وَمَا وَلَدَ

3. Da mahaifi da abin da ya haifa.

لَقَدْ خَلَقْنَا الْإِنسَانَ فِي كَبَدٍ

4. Lalle ne, Mun halitta mutum cikin wahala.

أَيَحْسَبُ أَن لَّن يَقْدِرَ عَلَيْهِ أَحَدٌ

5. Shin ko yana zaton babu wani mai iya samun iko a kansa?

يَقُولُ أَهْلَكْتُ مَالًا لُّبَدًا

6. Yana cewa; Na kashe dukiya mai yawa.

أَيَحْسَبُ أَن لَّمْ يَرَهُ أَحَدٌ

7. Shin, ko yana zaton cewa wani bai gan shi ba?

أَلَمْ نَجْعَل لَّهُ عَيْنَيْنِ

8. Shin, ba Mu sanya masa idanu biyu ba?

وَلِسَانًا وَشَفَتَيْنِ

9. Da harshe, da leb'b'a biyu.

وَهَدَيْنَاهُ النَّجْدَيْنِ

10. Kuma muka shiryar da shi ga hanyoyi biyu?

فَلَا اقْتَحَمَ الْعَقَبَةَ

11. To, don mene ne bai shiga Ak'aba ba?

وَمَا أَدْرَاكَ مَا الْعَقَبَةُ

12. Kuma mene ne ya sanar da kai abin da ake ce wa Ak'aba?

فَكُّ رَقَبَةٍ

13. Ita ce fansar wuyan bawa.

أَوْ إِطْعَامٌ فِي يَوْمٍ ذِي مَسْغَبَةٍ

14. Ko kuma ciyar da ma'abucin yunwa, a cikin yini.

يَتِيمًا ذَا مَقْرَبَةٍ

15. Ga maraya ma'abucin zumunta.

أَوْ مِسْكِينًا ذَا مَتْرَبَةٍ

16. Ko kuwa wani matalauci ma'abucin turb'aya.

ثُمَّ كَانَ مِنَ الَّذِينَ آمَنُوا وَتَوَاصَوْا بِالصَّبْرِ وَتَوَاصَوْا بِالْمَرْحَمَةِ

17. Sa'an nan kuma ya kasance daga wad'anda suka yi imani, kuma suka yi wa juna wasiyya da yin hak'uri, kuma suka yi wa juna wasiyya da tausayi.

أُوْلَئِكَ أَصْحَابُ الْمَيْمَنَةِ

18. Wad'annan ne ma'abuta albarka.

وَالَّذِينَ كَفَرُوا بِآيَاتِنَا هُمْ أَصْحَابُ الْمَشْأَمَةِ

19. Kuma wad'anda suka kafirta da ayoyinmu, su ne ma'abuta shu'umci.

عَلَيْهِمْ نَارٌ مُّؤْصَدَةٌ

20. A kansu akwai wata wuta abar kullewa.

Surar Rana([15])

سورة الشمس

Tana karantar da cewa idan azaba ta sauka a kan mutane takan shafi mai laifi da wanda ba shi da laifi daga cikinsu, da kuma nuni zuwa ga had'arin k'aryata ayar Allah mad'aukaki.

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ

Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin K'ai.

وَالشَّمْسِ وَضُحَاهَا

1. Ina rantsuwa da rana da hantsinta.

وَالْقَمَرِ إِذَا تَلَاهَا

2. Kuma da wata idan ya bi ta.

وَالنَّهَارِ إِذَا جَلَّاهَا

3. Da yini a lokacin da ya bayyana ta.

وَاللَّيْلِ إِذَا يَغْشَاهَا

4. Da dare a lokacin da ya ke rufe ta.

وَالسَّمَاءِ وَمَا بَنَاهَا

5. Da sama da abin da ya gina ta.

وَالْأَرْضِ وَمَا طَحَاهَا

6. Da k'asa da abin da ya shimfid'a ta.

وَنَفْسٍ وَمَا سَوَّاهَا

7. Da rai da abin da ya daidaita shi.

فَأَلْهَمَهَا فُجُورَهَا وَتَقْوَاهَا

8. Sa'an nan ya sanar da shi fajircinsa da shiryuwarsa.

قَدْ أَفْلَحَ مَن زَكَّاهَا

9. Lalle ne wanda ya tsarkake shi (rai) ya sami babban rabo.

وَقَدْ خَابَ مَن دَسَّاهَا

10. Kuma lalle ne wanda ya turbud'e shi (da laifi) ya tab'e.

كَذَّبَتْ ثَمُودُ بِطَغْوَاهَا

11. Samudawa sun k'aryata domin girman kansu.

إِذِ انبَعَثَ أَشْقَاهَا

12. A lokacin da mafi shak'awarsu ya tafi.

فَقَالَ لَهُمْ رَسُولُ اللَّهِ نَاقَةَ اللَّهِ وَسُقْيَاهَا

13. Sai Manzon Allah ya gaya musu cewa: "Ina tsoratar da ku ga rakumar Allah da ruwan shanta!"

فَكَذَّبُوهُ فَعَقَرُوهَا فَدَمْدَمَ عَلَيْهِمْ رَبُّهُم بِذَنبِهِمْ فَسَوَّاهَا

14. Sai suka k'aryata shi, sa'an nan suka soke ta. Saboda haka Ubangijinsu Ya darkake su saboda zunubinsu kuma ya daidaita ta (azabar).

وَلَا يَخَافُ عُقْبَاهَا

15. Kuma ba ya tsoron ak'ibarta (ita halakawar).

Surar Dare([16])

سورة الليل

Tana karantar da dangantaka tsakanin d'abi'a da halitta da aK'ibar mutum bisa aikinsa, da kuma kasuwar abubuwa tsakanin alheri da sharri.

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ

Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin K'ai

وَاللَّيْلِ إِذَا يَغْشَى

1. Ina rantsuwa da dare a lokacin da yake rufewa.

وَالنَّهَارِ إِذَا تَجَلَّى

2. Da lokacin rana yayin da bayyana.

وَمَا خَلَقَ الذَّكَرَ وَالْأُنثَى

3. Da abin da ya halitta namiji da mace.

إِنَّ سَعْيَكُمْ لَشَتَّى

4. HaK'iK'a ayyukanku, mabambanta ne.

فَأَمَّا مَن أَعْطَى وَاتَّقَى

5. To, amma wanda ya yi kyauta, kuma ya yi taK'awa.

وَصَدَّقَ بِالْحُسْنَى

6. Kuma ya gaskata kalma mai kyawo.

فَسَنُيَسِّرُهُ لِلْيُسْرَى

7. To, za Mu sauK'aK'e masa har ya kai ga sauki.

وَأَمَّا مَن بَخِلَ وَاسْتَغْنَى

8. Kuma amma wanda ya yi rowa, kuma ya wadatu da kansa.

وَكَذَّبَ بِالْحُسْنَى

9. Kuma ya K'aryatar da kalma mai kyawo.

فَسَنُيَسِّرُهُ لِلْعُسْرَى

10. To, za Mu sauK'aK'e masa har ya kai ga tsanani.

وَمَا يُغْنِي عَنْهُ مَالُهُ إِذَا تَرَدَّى

11. Kuma dukiyarsa ba ta wadatar masa da komai idan ya gangara (wuta).

إِنَّ عَلَيْنَا لَلْهُدَى

12. Lalle aikinMu ne, Mu bayyana shiriya.

وَإِنَّ لَنَا لَلْآخِرَةَ وَالْأُولَى

13. Kuma lalle ne Lahira da duniya Namu ne.

فَأَنذَرْتُكُمْ نَارًا تَلَظَّى

14. Saboda haka, Na yi maku gargad'i da wuta mai babbaka.

لَا يَصْلَاهَا إِلَّا الْأَشْقَى

15. Babu mai shigarta sai mafi shaK'awa.

الَّذِي كَذَّبَ وَتَوَلَّى

16. Wanda ya K'aryata, kuma ya juya baya.

وَسَيُجَنَّبُهَا الْأَتْقَى

17. Kuma mafi taK'awa zai nisance ta.

الَّذِي يُؤْتِي مَالَهُ يَتَزَكَّى

18. Wanda yake bayar da dukiyarsa ,alhali yana tsarkaka.

وَمَا لِأَحَدٍ عِندَهُ مِن نِّعْمَةٍ تُجْزَى

19. Alhali babu wani mai wata ni'ima wurinsa wadda ake neman sakamakonta.

إِلَّا ابْتِغَاء وَجْهِ رَبِّهِ الْأَعْلَى

20. Face dai neman yardar Ubangijinsa Mafi d'aukaka.

وَلَسَوْفَ يَرْضَى

21. Kuma tabbas da sannu zai yarda.

Surar Hantsi([17])

سورة الضحى

Tana karantar da ni'imomin da Allah Ya yi wa Annabi, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, da neman ya yi godiya a kansu ta hanyar biyayya ga umarnin Allah.

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ

Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin K'ai

وَالضُّحَى

1. Ina rantsuwa da hantsi

وَاللَّيْلِ إِذَا سَجَى

2. Da dare a lokacin da ya rufe (da duhunsa)

مَا وَدَّعَكَ رَبُّكَ وَمَا قَلَى

3. Ubangijinka bai K'yale ka ba, kuma bai K'i kaba

وَلَلْآخِرَةُ خَيْرٌ لَّكَ مِنَ الْأُولَى

4. Kuma lalle K'arshe ce mafi alheri a gare ka daga farko

وَلَسَوْفَ يُعْطِيكَ رَبُّكَ فَتَرْضَى

5. Kuma lalle ne, Ubangijinka zai yi ta ba ka kyauta sai ka yarda.

أَلَمْ يَجِدْكَ يَتِيمًا فَآوَى

6. Ashe, bai same ka maraya ba, sa'an nan Ya yi maka mafaka?

وَوَجَدَكَ ضَالًّا فَهَدَى

7. Kuma Ya same ka ba ka da shari'a, sai Ya shiryar da kai?

وَوَجَدَكَ عَائِلًا فَأَغْنَى

8. Kuma Ya same ka matalauci, sai Ya wadata ka?

فَأَمَّا الْيَتِيمَ فَلَا تَقْهَرْ

9. Saboda haka, amma maraya, to, kada ka rinjaye shi.

وَأَمَّا السَّائِلَ فَلَا تَنْهَرْ

10. Kuma amma mai tambaya, kada ka yi masa kyara.

وَأَمَّا بِنِعْمَةِ رَبِّكَ فَحَدِّثْ

11. Kuma amma ni'imar Ubangijinka, sai ka fad'a.

Surar Yalwatawa([18])

سورة الشرح

Tana nuna ni'imomin da Allah Ya yi wa Annabi, (s.a.w) domin ya K'ara godiya ga Allah (s.w.t)

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ

Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin K'ai

أَلَمْ نَشْرَحْ لَكَ صَدْرَكَ

1. Shin ba Mu yalwata maka zuciyarka ba.

وَوَضَعْنَا عَنكَ وِزْرَكَ

2. Kuma Muka saryar maka da nauyinka.

الَّذِي أَنْقَضَ ظَهْرَكَ

3. Wanda ya nauyaya bayanka.

وَرَفَعْنَا لَكَ ذِكْرَكَ

4. Kuma Muka d'aukaka maka ambatonka.

فَإِنَّ مَعَ الْعُسْرِ يُسْرًا

5. To, lalle ne tare da tsanani akwai wani sauK'i.

إِنَّ مَعَ الْعُسْرِ يُسْرًا

6. Lalle ne tare da tsanani akwai wani sauK'in.

فَإِذَا فَرَغْتَ فَانصَبْ

7. Saboda haka idan ka K'are sai ka kafu.

وَإِلَى رَبِّكَ فَارْغَبْ

8. Kuma ka yi kwad'ayi zuwa ga Ubangijinka.

Surar B'aure([19])

سورة التين

Tana karantar da cewa dukkan abin da ya shafi imani da aiki na gari ba ya tab'ewa, amma sauran abubuwa suna halaka

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ

Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin K'ai

وَالتِّينِ وَالزَّيْتُونِ

Ina rantsuwa da B'aure da Zaitun.

وَطُورِ سِينِينَ

Da Dutsen Sina.

وَهَذَا الْبَلَدِ الْأَمِينِ

Da wannan gari amintacce.

لَقَدْ خَلَقْنَا الْإِنسَانَ فِي أَحْسَنِ تَقْوِيمٍ

Lalle ne, Mun halitta mutum a cikin mafi kyawon daidaito.

ثُمَّ رَدَدْنَاهُ أَسْفَلَ سَافِلِينَ

Sannan Muka mayar da shi mafi K'asK'antar K'asK'antattu.

إِلَّا الَّذِينَ آمَنُوا وَعَمِلُوا الصَّالِحَاتِ فَلَهُمْ أَجْرٌ غَيْرُ مَمْنُونٍ

Sai dai wad'anda suka yi imani, kuma suka yi ayyuka na K'warai, To wadannan suna da sakamako wanda ba ya yankewa.

فَمَا يُكَذِّبُكَ بَعْدُ بِالدِّينِ

To, bayan haka me ya sanya ka K'aryata sakamako.

أَلَيْسَ اللَّهُ بِأَحْكَمِ الْحَاكِمِينَ

Ashe Allah ba Shi ne Mafi iya hukuncin masu hukunci ba?

Surar Gudan Jini([20])

سورة العلق

Tana karantar da cewa karatu shi ne gaba da komai, amma a gama shi da sunan Allah, kuma duk wanda ya kauce wa hanyar Allah zai samu uK'uba

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ

Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin K'ai

اقْرَأْ بِاسْمِ رَبِّكَ الَّذِي خَلَقَ

1. Ka yi karatu da sunan Ubangijinka, wanda Ya yi halitta.

خَلَقَ الْإِنسَانَ مِنْ عَلَقٍ

2. Ya hahitta mutum daga gudan jini.

اقْرَأْ وَرَبُّكَ الْأَكْرَمُ

3. Ka yi karatu, kuma Ubangijinka shi ne Mafi karimci.

الَّذِي عَلَّمَ بِالْقَلَمِ

4. Shi ne wannan da ya koyar da alK'alami.

عَلَّمَ الْإِنسَانَ مَا لَمْ يَعْلَمْ

5. Ya sanar da mutum abin da bai sani ba.

كَلَّا إِنَّ الْإِنسَانَ لَيَطْغَى

6. A'aha! Lalle, ne mutum yana girman kai.

أَن رَّآهُ اسْتَغْنَى

7. Domin ya ga kansa, ya wadatu.

إِنَّ إِلَى رَبِّكَ الرُّجْعَى

8. HaK'iK'a zuwa ga Ubangijinka makoma take.

أَرَأَيْتَ الَّذِي يَنْهَى

9. Shin, ka ga wanda ke hana.

عَبْدًا إِذَا صَلَّى

10. Bawa idan ya yi salla?

أَرَأَيْتَ إِن كَانَ عَلَى الْهُدَى

11. Ashe, ka gani, idan ya kasance a kan shiriya?

أَوْ أَمَرَ بِالتَّقْوَى

12. Ko ya yi umurni da taK'awa?

أَرَأَيْتَ إِن كَذَّبَ وَتَوَلَّى

13. Ashe, ka gani, idan ya K'aryata, kuma ya juya baya?

أَلَمْ يَعْلَمْ بِأَنَّ اللَّهَ يَرَى

14. Ashe, bai sani ba cewa Allah Yana gani?

كَلَّا لَئِن لَّمْ يَنتَهِ لَنَسْفَعًا بِالنَّاصِيَةِ

15. A'aha! Lalle ne, idan bai hanu ba, tabbas zamu ja gashin maK'warK'wad'a.

نَاصِيَةٍ كَاذِبَةٍ خَاطِئَةٍ

16. MaK'warK'wad'a, maK'aryaciya, mai laifi.

فليدع نادية

17. To sai ya kira K'ungiyarsa.

سَنَدْعُ الزَّبَانِيَةَ

18. Zamu kira zabaniyawa.

كَلَّا لَا تُطِعْهُ وَاسْجُدْ وَاقْتَرِبْ

19. A'aha kada ka bi shi, kuma ka yi sujada, ka nemi kusanci.

Surar Daraja([21])

سورة القدر

Tana karantar da son Allah ga wannan al'umma ta Musulmi da Ya ba su Dare mai Daraja "Lailatul K'adr" domin Ya yawaita ladar ayyukansu ko da yake rayukansu ba su da tsawo kamar na al'ummomin farko, kamar yadda take nuna cewa; alaK'ar Allah (s.w.t) da bayinsa ba ta yankewa da yankewar Annabci.

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ

Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin K'ai.

إِنَّا أَنزَلْنَاهُ فِي لَيْلَةِ الْقَدْرِ

1. Lalle ne Mu, Mun saukar da shi a cikin Dare mai daraja.

وَمَا أَدْرَاكَ مَا لَيْلَةُ الْقَدْرِ

2. To, me ya sanar da kai abin da ake cewa Lailatul K'adari?

لَيْلَةُ الْقَدْرِ خَيْرٌ مِّنْ أَلْفِ شَهْرٍ

3. Lailatul K'adari mafi alheri ne daga watanni dubu.

تَنَزَّلُ الْمَلَائِكَةُ وَالرُّوحُ فِيهَا بِإِذْنِ رَبِّهِم مِّن كُلِّ أَمْرٍ

4. Mala'iku da Ruhi suna sauka a cikinsa da izinin Ubangijinsu daga kowane umurni.

سَلَامٌ هِيَ حَتَّى مَطْلَعِ الْفَجْرِ

5? Aminci ne shi har b'ollowar alfijiri.

Surar Hujja([22])

سورة البينة

Tana karantar da halayen kifirai da mutanen Littafi, wato Yahudu da Nasara game da Annabi (s.a.w), da Mushirikai tun gabanin da kuma bayan bayyanarsa.

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ

Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin K'ai

لَمْ يَكُنِ الَّذِينَ كَفَرُوا مِنْ أَهْلِ الْكِتَابِ وَالْمُشْرِكِينَ مُنفَكِّينَ حَتَّى تَأْتِيَهُمُ الْبَيِّنَةُ

1. Wad'anda suka kafirta daga mutanen Littafi, da mushirikai, ba su kasance masu gushewa daga gaskiya ba har sai da hujja ta zo musu.

رَسُولٌ مِّنَ اللَّهِ يَتْلُو صُحُفًا مُّطَهَّرَةً

2. Wani Manzo daga Allah yana karanta wasu takardu masu tsarki.

فِيهَا كُتُبٌ قَيِّمَةٌ

3. A cikinsu akwai wasu littattafai masu d'aukaka.

وَمَا تَفَرَّقَ الَّذِينَ أُوتُوا الْكِتَابَ إِلَّا مِن بَعْدِ مَا جَاءتْهُمُ الْبَيِّنَةُ

4. Kuma wad'anda aka bai wa Littafi ba su rarrabu ba sai bayan hujja ta zo musu.

وَمَا أُمِرُوا إِلَّا لِيَعْبُدُوا اللَّهَ مُخْلِصِينَ لَهُ الدِّينَ حُنَفَاء وَيُقِيمُوا الصَّلَاةَ وَيُؤْتُوا الزَّكَاةَ وَذَلِكَ دِينُ الْقَيِّمَةِ

5. Kuma ba a umarce su da komai ba sai su bauta wa Allah suna masu tsarkake addini gare Shi, masu daidaito, kuma su tsayar da salla, kuma su bayar da zakka, kuma wannan shi ne addinin nagarta.

إِنَّ الَّذِينَ كَفَرُوا مِنْ أَهْلِ الْكِتَابِ وَالْمُشْرِكِينَ فِي نَارِ جَهَنَّمَ خَالِدِينَ فِيهَا أُوْلَئِكَ هُمْ شَرُّ الْبَرِيَّةِ

6. HaK'iK'a ne wad'anda suka kafirta daga mutanen Littafi da mushirikai suna cikin wutar Jahannama suna madawwama a cikinta, wad'annan su ne mafi sharrin talikai.

إِنَّ الَّذِينَ آمَنُوا وَعَمِلُوا الصَّالِحَاتِ أُوْلَئِكَ هُمْ خَيْرُ الْبَرِيَّةِ

7. HaK'iK'a wad'annan nan da suka yi imani kuma suka yi ayyuka na gari, wad'annan su ne mafifitan talikai.

جَزَاؤُهُمْ عِندَ رَبِّهِمْ جَنَّاتُ عَدْنٍ تَجْرِي مِن تَحْتِهَا الْأَنْهَارُ خَالِدِينَ فِيهَا أَبَدًا رَّضِيَ اللَّهُ عَنْهُمْ وَرَضُوا عَنْهُ ذَلِكَ لِمَنْ خَشِيَ رَبَّهُ

8. Sakamakonsu, a wurin Ubangijinsu, shi ne gidajen Aljannar Adnu, K'oramu suna gudana daga K'arK'ashinsu suna madawwama a cikinta har abada, Allah Ya yarda da su, kuma su ma sun yarda da Shi, wannan (sakamako ne) ga wanda ya ji tsoron Ubangijinsa.

Surar Girgiza([23])

سورة الزلزلة

بسم الله الرحمن الرحيم

Da Sunan Allah Mai Rahama Mai Jin K'ai

إِذَا زُلْزِلَتِ الْأَرْضُ زِلْزَالَهَا

1. Idan aka girgiza k'asa girgizawarta.

وَأَخْرَجَتِ الْأَرْضُ أَثْقَالَهَا

2. Kuma k'asa ta fitar da kayan nauyin da suke cikinta.

وَقَالَ الْإِنسَانُ مَا لَهَا

3. Kuma mutum ya ce: Mene ne ya same ta?.

يَوْمَئِذٍ تُحَدِّثُ أَخْبَارَهَا

4. A ranar nan zata fad'i labaranta.

بِأَنَّ رَبَّكَ أَوْحَى لَهَا

5. Cewa Ubangijinka ne ya yi mata umarni.

يَوْمَئِذٍ يَصْدُرُ النَّاسُ أَشْتَاتاً لِّيُرَوْا أَعْمَالَهُمْ

6. A ranar nan mutane zasu zo jama'a-jama'a domin a nuna musu ayyukansu.

فَمَن يَعْمَلْ مِثْقَالَ ذَرَّةٍ خَيْراً يَرَهُ

7. To wanda ya aikta wani aiki gwargwadon nauyin zarra na alheri, zai gan shi.

وَمَن يَعْمَلْ مِثْقَالَ ذَرَّةٍ شَرّاً يَرَهُ

8. Kuma wanda ya aikata wani aiki gwargwadon nauyin zarra na sharri, zai gan shi.

Surar Dawakai([24])

سورة العاديات

بسم الله الرحمن الرحيم

Allah Sunan Allah Mai Rahama Mai Jin K'ai

وَالْعَادِيَاتِ ضَبْحاً

1. Ina rantsuwa da dawakai masu gudu, suna masu k'ugin ciki.

فَالْمُورِيَاتِ قَدْحاً

2. Da masu k'yasta wuta k'yastawa.

فَالْمُغِيرَاتِ صُبْحاً

3. Sannan da masu kai hari lokacin Asuba.

فَأَثَرْنَ بِهِ نَقْعاً

4. Sai su tayar da k'ura da shi (harin).

فَوَسَطْنَ بِهِ جَمْعاً

5. Sai su kutsa cikin jama'ar mayak'a da ita (k'urar).

إِنَّ الْإِنسَانَ لِرَبِّهِ لَكَنُودٌ

6. Hak'ik'a mutum mai tsananin butulci ne ga Ubangijinsa.

وَإِنَّهُ عَلَى ذَلِكَ لَشَهِيدٌ

7. Kuma lalle shi mai sheda ne a kan hakan.

وَإِنَّهُ لِحُبِّ الْخَيْرِ لَشَدِيدٌ

8. Kuma lalle shi mai tsananin so ne ga alheri.

أَفَلَا يَعْلَمُ إِذَا بُعْثِرَ مَا فِي الْقُبُورِ ‏

9. Shin ba ya sanin idan aka tone abin da yake cikin kaburbura.

وَحُصِّلَ مَا فِي الصُّدُورِ

10. Kuma aka bayyana abin da yake cikin zukata.

إِنَّ رَبَّهُم بِهِمْ يَوْمَئِذٍ لَّخَبِيرٌ

11. Lalle Ubangijinsu masani ne game da su a wannan ranar.

Surar Mai K'wank'wasa([25])

سورة القارعة

بسم الله الرحمن الرحيم

Da Sunan Allah Mai Rahama Mai Jin K'ai

الْقَارِعَةُ

1. Mai K'wank'wasa.

مَا الْقَارِعَةُ

2. Mece ce mai k'wank'wasa.

وَمَا أَدْرَاكَ مَا الْقَارِعَةُ

3. Kuma me ya sanar da kai mece ce mai k'wank'wasa.

يَوْمَ يَكُونُ النَّاسُ كَالْفَرَاشِ الْمَبْثُوثِ

4. Ranar da mutane zasu kasance kamar fari masu watsuwa.

وَتَكُونُ الْجِبَالُ كَالْعِهْنِ الْمَنفُوشِ

5. Kuma duwatus su kasance kamar gashin suf da aka sab'e.

فَأَمَّا مَن ثَقُلَتْ مَوَازِينُهُ

6. To amma wanda ma'aunansa suka yi nauyi.

فَهُوَ فِي عِيشَةٍ رَّاضِيَةٍ

7. To shi yana cikin wata rayuwa yardajjiya.

وَأَمَّا مَنْ خَفَّتْ مَوَازِينُهُ

8. To amma kuma wanda ma'aunansa suka yi sako-sako.

فَأُمُّهُ هَاوِيَةٌ

9. To uwarsa Hawiya ce.

وَمَا أَدْرَاكَ مَا هِيَهْ

10. Me ya sanar da kai mece ce ita?.

نَارٌ حَامِيَةٌ

11. Wata wuta ce mai zafi.

Surar Yawan Tara Arziki([26])

سورة التكاثر

بسم الله الرحمن الرحيم

Da Sunan Allah Mai Rahama Mai Jin K'ai

أَلْهَاكُمُ التَّكَاثُرُ

1. Rigen Yawan tara arziki ne ya shagaltar da ku.

حَتَّى زُرْتُمُ الْمَقَابِرَ

2. Har kuka ziyarci kaburbura.

كَلَّا سَوْفَ تَعْلَمُونَ

3. A'aha! Zaku sani.

ثُمَّ كَلَّا سَوْفَ تَعْلَمُونَ

4. Sannan tabbas zaku sani.

كَلَّا لَوْ تَعْلَمُونَ عِلْمَ الْيَقِينِ

5. Hak'ik'a da ku san sani na yak'ini.

لَتَرَوُنَّ الْجَحِيمَ

6. Da kun ga wutar Jahim.

ثُمَّ لَتَرَوُنَّهَا عَيْنَ الْيَقِينِ

7. Kuma tabbas zaku gan ta idanu k'uru-k'uru.

ثُمَّ لَتُسْأَلُنَّ يَوْمَئِذٍ عَنِ النَّعِيمِ

8. Sannan tabbas za a tambaye ku a wannan ranar game da ni'imar.

Surar Zamani([27])

سورة العصر

بسم الله الرحمن الرحيم

Allah Sunan Allah Mai Rahama Mai Jin K'ai

وَالْعَصْرِ

1. Ina rantsuwa da zamani

إِنَّ الْإِنسَانَ لَفِي خُسْرٍ

2. Hak'ik'a mutum yana cikin hasara.

إِلَّا الَّذِينَ آمَنُوا وَعَمِلُوا الصَّالِحَاتِ وَتَوَاصَوْا بِالْحَقِّ وَتَوَاصَوْا بِالصَّبْرِ

3. Sai dai wad'anda suka yi imani, kuma suka yi ayyukan k'warai, kuma suka yi wa juna wasici da bin gaskiya, kuma suka yi wa juna wasici da yin hak'uri.

Surar Mai Zumde([28])

سورة الهُمَزَة

بسم الله الرحمن الرحيم

Da Sunan Allah Mai Rahama Mai Jin K'ai

وَيْلٌ لِّكُلِّ هُمَزَةٍ لُّمَزَةٍ

1. Azaba ta tabbata ga dukkan wani, mai zumd'e, mai gatsine.

الَّذِي جَمَعَ مَالاً وَعَدَّدَهُ

2. Wanda ya tara dukiya ya yi tattalinta.

يَحْسَبُ أَنَّ مَالَهُ أَخْلَدَهُ

3. Yana tsammanin dukiyarsa zata dawwamar da shi.

كَلَّا لَيُنبَذَنَّ فِي الْحُطَمَةِ

4. A'aha! Lalle sai an jefa shi a cikin hud'ama.

وَمَا أَدْرَاكَ مَا الْحُطَمَةُ

5. Kuma me ya sanar da kai ko mece ce hud'ama.

نَارُ اللَّهِ الْمُوقَدَةُ

6. Wutar Allah ce abar hurawa.

الَّتِي تَطَّلِعُ عَلَى الْأَفْئِدَةِ

7. Wacce take lek'awa a kan zuciya.

إِنَّهَا عَلَيْهِم مُّؤْصَدَةٌ

8. Hak'ik'a ita abar kullewa ce a kansu.

فِي عَمَدٍ مُّمَدَّدَةٍ

9. A cikin wasu ginshik'ai mik'ak'k'u.