Makamin Ahlul-baiti

Makamin Ahlul-baiti0%

Makamin Ahlul-baiti Mawallafi:
: Mu'assasar Al-Balagh
: Muhummad Auwal Bauchi
Gungu: Kala-kala

  • Farawa
  • Na Baya
  • 36 /
  • Na Gaba
  • Karewa
  •  
  • Gurzawa HTML
  • Gurzawa Word
  • Gurzawa PDF
  • Budawa: 14016 / Gurzawa: 2653
Girma Girma Girma
Makamin Ahlul-baiti

Makamin Ahlul-baiti

Mawallafi:
Hausa

Adalcin Allah Da Sharhi Kan Halayyar Dan'adam

"Allah Ya shaida cewa: Lalle ne babu abin bautawa face Shi, kuma Mala'iku da ma'abuta ilmi sun shaida, Yana tsaye da adalci, babu abin bautawa face Shi, Mabuwayi, Mai Hikima". (Surar Aali Imrana, 3: 18)

Adalci siffa ce, cikin siffofin Allah (S.W.T.). Muna iya ganin gurabun adalcinSa a dukkan bangarorin samammu, kamar fagen halitta da samarwa da fagen dabi'a da halittar mutum da dabba da tsiro, haka kuma muna ganin wannan adalcin cikin shari'a da dokokin Ubangiji. "Lalle Allah Na yin umurni da adalci da kyautatawa". (Surar Nahli, 16: 90)

Haka ma adalcin Ubangiji ya bayyana cikin abin da Yake hukumtawa da kaddarawa kan halittunSa na hukumci da kaddara, da cikin abin da Ya shar'anta na shari'u da sakonni. Kamar yadda yake bayyana a fagen lahira, ranar hisabi da sakamako. Zai sakantawa mai kyautatawa da kyautatawar, mai mummunan aiki kuwa da irin aikinsa. "Kuma Ubangijinka ba Ya zaluntar kowa". (Surar Kahf, 18: 49) "Sa'an nan kuma a cika wa kowane rai abin da ya sana'anta". (Surar Bakara, 2: 281)

"Allah ba Ya kallafawa rai face ikon yinsa, yana da ladan abin da ya aikata, kuma a kansa akwai zunubin abin da ya yi ta aikatawa...". (Surar Bakara, 2: 286)

Bisa wannan tsarin ne musulmin farko suka tafi wajen fahimtar alakarsu da Allah (S.W.T.) da fahimtar halayyar 'yan Adam da ayyukansu. Daga bisani sai falsafa ta shigo ga kuma ra'ayoyin ilmin tauhidi dukkansu masu sassabawa juna. Hakika wadannan sun tsirar da ra'ayoyi uku kan fassarar ayyukan mutane da alakarsu da iradar (nufi) Allah Madaukakin Sarki. Wadannan ra'ayoyi kuwa su ne:

1. Jabru (Tilastawa).

2. Tafwidhu (Sakarwa).

3. Babu Jabru ballantana Tafwidhu.

Hakika wadansu kungiyoyi da mazhabobi sun yi mummunan fahimta wa zahirin wadansu ayoyin Alkur'ani, kamar fadinSa (S.W.T.) cewa: "Zahirinsu ya sanya irin wannan kungiya suka yarda da Jabru. Abin da wannan ra'ayi yake nufi shi ne dan'Adam ba ya mallakar nufi kuma ba shi da zabi, shi ba kome ba ne face bigire da gurin saukar kaddararrun abubuwa daga Allah (S.W.T.). A bisa wannan ra'ayi, mutum abin tilastawa ne, ba shi da wani zabi cikin al'amurransa. Masu irin wannan ra'ayi ana kiransu da sunan Mujabbira.

Ra'ayi na biyu kuwa shi ne mai cewa an sakar wa dan'Adam ikon zabi wajen ayyukansa, da kuma nufinsa babu nufin Allah a cikin ayyukansa. Kai suna ganin ma cewa Allah ba Ya iya hana mutum yin abin da ya yi nufin yi ko sabo ne kamar kisan kai, zalunci, shan giya, ko kuwa ayyukan biyayya ne kamar su adalci, kyautatawa, salla da dai sauransu. To da wannan, dan'Adam yana da 'yanci ga barin Allah (S.W.T.), wannan kuwa shi ne ra'ayin Mu'utalizawa.

To Imaman Ahlulbaiti (a.s) sun yi raddi wa wadannan ra'ayoyi guda biyu, sun nuna bacinsu gaba daya. Kowanne daga ra'ayoyin nan biyu sun saba da abin da Alkur'ani ya zo da shi, akidar tauhidi kuwa ta kafu kan tushensa ne. su Imamai (a.s.) sun fayyace mana cewa akwai bayyananniyar alaka tsakanin irin yadda ake fahimtar halayyar mutum da imani da adalcin Allah. Suka ce lallai abin da ra'ayin cewa mutum ba ya mallakar wani nufi ko zabi sai dai shi abin tilastawa ne kurum, yana janyo tuhumtar Mahalicci Mai girma da Daukaka da zalunci da kore adalci daga gare Shi, lallai kuwa Ya girmama daga hakan. Saboda ma'anar wannan shi ne Allah Ya tilastawa mutum aikata sharri sannan kuma Ya yi masa ukuba dominsa, haka nan Ya tilasta masa aikata alheri sannan kuma Ya hana shi ladansa. Domin haka ne Imamai (a.s.) suka kakkabe wannan mumunan fassara wanda da yawan musulmi suka fada ciki a dalilin gurguwar fahimtar da suka yi wa zahirin wadansu ayoyi kamar cewa: "Yana batar da wanda Ya so, Yana kuma shiryar da wanda Ya so".

Imaman Ahlulbaiti (a.s) sun yi wa matsalolin shiryarwa da batarwa tafsiri bayyananne mai dacewa da adalcin Allah (S.W.T.). Bayanin wannan yana tafe.

Haka nan kuma Imamai (a.s.) sun yi watsi da ra'ayin masu cewa an sakarwa mutum akala sai yadda ya ga dama zai yi, ba tare da Allah Yana iya hana shi ba. Sun bayyana cewa wannan ra'ayi karkatacce da cewa tuhumar Allah ne da rashin cikakken iko kan bayinSa da gajiyawarSa kan hakan. Alhali kuwa Allah (S.W.T.) Mai cikakken iko ne, kuma Mamallakin dukkan halittunSa.

Imamai (a.s.) suna da matsaya matsakaiciya dangane da al'amarin da ya shafi adalcin Ubangiji. Wannan matsaya tana kore Tilastawa da Sakarwa, tana cewa: (Nufin mutum baya iya rabuwa da nufin Allah). Sun bayyana wannan alakar da take tsakanin nufin mutum da nufin Ubangiji bayani cikakke a akidance. Nan gaba za mu kawo ruwayoyinsu masu nuna wannan ra'ayi.

Kafin mu kawo wadannan ruwayoyi, bari mu yi dan sharhi kan batutuwan da mazhabar Ahlulbaiti (a.s) suka bambanta da masu ra'ayoyi kan mas'alar adalcin Allah, bisa abubuwa guda uku na asasi:

Dan'Adam yana da nufi da ikon zabin duk aikin da zai yi, ko na alheri ko na sharri, haka kuma kin aikata shi. Mutum yana iya kisan kai ko sata ko zalunci ko karya, da wannan nufin da ikon da yake da shi. Haka kuma yana da daman tsai da adalci da aikata aikin kwarai da yin salla da barin haramtattun abubuwa, da wannan nufi nasa da iko.

Hakika Allah (S.W.T.) Yana da ikon hana mutum kowane aiki, kamar yadda yake da ikon sa mutum aikata kowane aiki ba tare da zabin mutum ya sami tasiri ba. Sai dai Allah ba Ya tilastawa kowa aikata alheri ko sharri.

Amma Shi Allah, domin tausayinSa da jin kanSa, Yana shiga tsakanin bawan da ya cancanci taimakonSa wajen aikata mummunan aiki, domin jin kai. Haka ma Yana taimaka masa wajen aikata alheri idan ya cancanci taimakon.

1. Wani abin da yake da dangantaka da adalcin Ubangiji kuma shi ne: Allah Yana sakantawa kowane mutum ranar kiyama da abin da ya aikata, alheri ko sharri. Sai dai kuma wata kungiyar ta musulmi tana ganin cewa mai yiyuwa ne Allah Ya shigar da mai kyautata aiki cikin wuta, mai mummunan aiki kuma aljanna, suna kuma dogara ne, bisa kuskure da mummunan fahimta, kan wannan aya mai girma: "Ba a tambayarSa ga abin da Yake aikatawa, alhali kuwa su ana tambayarsu". (Surar Anbiya, 21: 23)

Wasu jama'a daga cikin musulmi sun dogara da wannan ayar ne bisa tafsiri na kuskure, suka ce ba ya wajaba kan Allah (S.W.T.) Ya cika alkawarin sakayya da Ya yi a ranar kiyama. Imaman Ahlulbaiti (a.s) sun mai da martani kan wannan zance da cewa, wannan ya sabawa gaskiyar Allah Ta'ala da adalcinSa.

Wancan ra'ayin yana daidaita mai kyautatawa da mai mummunan aiki, hakan kuwa yana rusa kimar kallafawa bayi da kuma sanya shari'a. Ingantaccen zance dai shi ne babu wani aikin da ba shi da sakamako, ko kuma mai daukar laifin yinsa, kamar yadda aya ta ce:

"To wanda ya aikata (wani aiki) gwargwadon nauyin zarra, na alheri, zai ganshi. Kuma Wanda ya aikata gwargwadon nauyin zarra na sharri, zai gan shi". (Surar Zalzala, 99: 7-8)

2. Ra'ayoyin sashin musulmi sun tafi a kan cewar ya dace ga Allah (S.W.T.) Ya kallafawa bayi abin da yafi karfinsu, wannan kuwa sun fade shi ne domin dogara kan fahimta ta kuskure da suka yi wa wannan aya mai girma: "Ya Ubangijinmu Kada Ka sanya mu daukar abin da babu iko gare mu da shi". (Surar Bakara, 2: 286)

Imaman Ahlulbaiti (a.s) sun kore wannan fahimta suna masu bayanin cewa ta saba da adalcin Allah da kuma bayyanannen fadi na Alkur'ani mai girma, cewa: "Allah ba Ya kallafa wa rai face abin da zai iya dauka". (Surar Bakara, 2: 286)

To yanzu za mu kawo sashen ruwayoyi da tattauna-war Ahlulbaiti (a.s), masu mana sharhin wadannan ginshikai na asali da fassara halayyar mutum da alakar da ke akwai tsakanin nufin mutum da ta Allah (S.W.T.). Wadannan ruwayoyi suna kulla tafsiri da sharhin halay-yar mutum da tushen adalcin Allah domin su karfafa mana dayantaka (ta Ubangiji) fahimta da tunani da kuma i'itikadi cikin sakon Musulunci. A lokaci guda sun bata ra'ayin Jabru da Tafwidhu da ma dukkan sauran tunace-tunace da kirdado wadanda suka fice daga tafarkin Alkur'ani.

Imam Sadik (a.s.) ya ce: "Allah Ya halicci halittu Ya kuma san makomarsu. Ya umarce su (da ayyukan biyayya) Ya hane su (ayyukan sabo). Kuma bai umarce su da abu ba face Ya sanya musu hanyar barin abin. Ba su zamowa masu riko (da umarnin) ko masu bari face da izinin Allah Ta'ala([180]) ".

Yayin da Imam Ali bn Abi Dalib (a.s.) ya tafi kasar Sham (Syria), domin yakar Mu'awiyya a Siffin, wani daga sahabbansa ya tambaye shi cewa:

"Ya Amirul Muminina! Ka ba mu labarin wannan tafiya tamu, shin da hukumcin Allah ne ko da kaddararSa?" sai ya amsa masa da cewa: "Saurara dattijo, na rantse da Allah ba kwa hawan wani tudu ko ku gangara cikin wani kwari face bisa hukumcin Allah da kaddararSa".Sai Dattijon ya ce: 'Ga Allah nake neman ladar wahalata, Ya Amirul Muminina'. Sai Imam Ali (a.s.) ya ce da shi:"Kaiconka! Ta yiyu kana zaton hukumci lizimtacce da kaddara yankakkiya! Da haka al'amarin yake da sakamako da horo sun baci, kuma da alkawari da narko sun warware. Allah (S.W.T.) Ya umarci bayinSa bisa zabinsu, Ya hana su domin gargadi, Ya kallafa musu sassauka bai kallafa musu mai tsanani ba, Yana biyan kadan da mai yawa. Ba a saba masa domin rinjaya, ba a tilastawa don a yi maSa biyayya. Bai aiko Annabawa don wasa ba, kuma bai sauko da Littafi wa bayi haka a banza ba. Bai kuwa halicci sammai da kasa da abin da yake tsakaninsu a banza ba; "Wannan shi ne zaton wadanda suka kafirta. To, bone ya tabbata ga wadanda suka kafirta daga wuta([181]) ".

An ruwaito daga Imam Ali bn Musa al-Ridha (a.s.) cewa an ambaci Jabru da Tafwidhu a gabansa, sai ya ce: "Shin ba zan sanar da ku wata ka'idar da ba za ku sassaba a cikinta, kuma duk wanda ya yi jayayya da ku sai kun rinjaye shi ba?Sai muka ce: 'E, a sanar da mu', sai ya ce:"Allah Mai Girma da Daukaka ba a biyayya gare Shi domin tilastawa, ba a saba masa don rinjaya, ba ya sake da bayinSa cikin mulkinSa. Shi ne Mamallakin abin da Ya mallakar masu, Mai iko kan abin da Ya ba su ikonSa. Idan bayinSa sun yi biyayya gare Shi, ba zai tare ko Ya hana su ba. Idan kuwa suka zabi su saba masa, in Ya ga damar tare su sai Ya yi, idan kuwa bai tare su ba suka aikata sabon, to ba kuwa Shi Ya jefa su ciki ba". Daga nan sai ya ce: "Wanda duk ya kiyaye wannan maganar, to lallai zai rinjayi mai sabawa da shi([182]) ".

A cikin littafin Sharh al-Aka'id na Shaikh Mufid an ce: "An ruwaito daga Abul Hasan na Uku (a.s.) yayin da aka tambaye shi batun ayyukan bayi; shin halittattu ne daga Allah Ta'ala? Sai ya amsa da cewa: "Da Shi Ya halitta su da bai barranta da su ba, alhali Yana cewa: 'Lalle ne Allah Barrantacce ne daga masu shirka'. Barrantan nan ba ta shafar zatinsu, Ya dai barranta ne daga shirkarsu da munanan ayyukansu([183]) ".

A cikin littafin Kitabul Tauhid na Muhammad bn Ajlan, ya ce: "Na tambayi Abu Abdullah (a.s.) cewa: 'Shin Allah Ya sakar wa bayi al'amarinsu ne?', sai ya ce: "Karimcin Allah ya wuce gaban Ya saki al'amurransu gare su", sai nace: 'To kenan Allah Ya tilasta wa bayi aikata ayyukansu kenan?, sai ya ce: "Adalcin Allah Ya wuce gaban tilastawa bawa yin wani aiki sannan kuma Ya azabta shi a kan wannan aiki([184]) ".

A ruwaito cikin Uyunul Akhbar al-Ridha (a.s.) wajen fadar Allah Ta'ala cewa: "Kuma Ya (Allah) bar su a cikin duffai, ba su gani". (Surar Bakara, 2: 17)

Abu Abdullah (a.s.) ya ce: "Ba a siffanta Allah da bari kamar yadda ake siffanta halittunSa, sai dai yayin da Ya san cewa ba su dawowa ga barin kafirci da bata ba, sai Ya hana su taimako da ludufi (tausayi), Ya bar su da zabinsu([185]) ".

Har ila yau ya zo cikin wannan littafin wajen tafsirin Imam Ridha (a.s.) kan fadin Allah (S.W.T.) cewa: "Allah Ya sa rufi a kan zukatansu". Sai ya ce: "Abin da ake nufi da 'Khatam' shi ne 'al-Dab'u' watau rufi a kan zukatan kafirai domin yi musu ukuba kan kafircinsu, kamar yadda Allah (S.W.T.) ya ce:

"A'a Allah ne Ya rufe a kansu (zukatansu) saboda kafircinsu, saboda haka ba za su yi imani ba face kadan([186]) ". (Surar Nisa', 4: 155)

To haka ne tafarkin Ahlulbaiti (a.s) yake fayyace manufar shiriya da bata da kuma cewa Allah (S.W.T.) bai halicci mutane suna batattu ko shiryayyu ba. Sai dai Ya bar musu zabi, Ya ba su nufi, Ya kuma bayyana musu hanyar alheri tare da gargadi kan hanyar sharri da halaka, Allah Ta'ala Yana cewa: "Lalle ne Mu, Mun shiryar da shi (mutum) ga hanyar kwarai, ko ya zama mai godiya, ko kuma ya zama mai kafirci". (Surar Insan, 76: 3)

Kuma Yana cewa: "Kuma Muka shiryar da shi ga hanyoyi biyu". (Surar Balad, 90: 10) Watau Mun sanar da shi hanyar alheri da ta sharri, zabi kuma na gare shi.

Manzon Allah (s.a.w.a.) ya fassara ayar da cewa: "Su dai hanyoyi ne guda biyu, hanyar alheri da hanyar sharri. Kada hanyar sharri ta fi soyuwa gare ku bisa hanyar alheri([187]) ".

Tafarkin Ahlulbaiti (a.s) ya zabi ra'ayi tsarkakakke na bayani kan halayyar dan'Adam na alheri ko sharri, da wata ka'ida: "Babu Jabru ba tafwidhu, sai dai al'amari ne tsakanin al'amurra biyu, watau mataki tsakanin matakai biyu". Yayin da aka tambayi daya daga cikin Imaman Ahlulbaiti (a.s), shin akwai wani mataki tsakanin tilasta-wa (jabru) da sajarwa (tafwidh)? Sai ya amsa da cewa: "Abin da yake tsakaninsu ya kai fadin tsakanin sama da kasa".

Wannan shi ne takaitaccen bayanin tafarkin Ahlul-baiti (a.s) kan batun Jabru da Tafwidh, haka ne kuma akidar musulmin da suka yi koyi da tafarkinsu take.

Ra'ayin Ahlulbaiti (a.s) Dangane da Batattun Kungiyoyi

Babu shakka makiya Musulunci sun san cewa Ahlul-baiti (a.s) su ne mabubbuga ta asali da tsarkakar addini mai kwaranye wa musulmi dukkan wahalhalu da bala'u. Su masu daraja ne a zukatan musulmi bai daya.

Kowa yana ganin girman alkadarinsu, yana tsarkake duk abin da ya fito daga gare su ko ya karkare zuwa gare su. Don haka ne masu neman rushe addini da shuka masa dasisa suke fuskantar wannan tushe na Musulunci domin su sami damar shuka barna alhali suna karkashin inuwar Ahlulbaiti (a.s). Suna daukar tutar Ahlulbaiti (a.s) da sunan goyon bayansu domin su sami damar kaidi da rushe akidar tauhidi, alhali Ahlulbaiti (a.s) sun barranta daga gare su da kuma tsine musu albarka. Wadannan irin jama'a sun kirkiri akidun bata da karkatacciyar falsafa mai cewa Allah Yana hululi (wato Ya shiga jikin wata halitta daga cikin halittunSa) cikin Imamai - Allah Ya daukaka ga barin hakan- da cewa Allah Ya sakar wa Imamai (a.s.) al'amurran arzurtawa da tasiri cikin halittar aljanna da wuta.

Ba su tsaya nan ba sai da sashinsu ya dangantawa Imamai (a.s.) allantaka. Duk hakan kuwa sun yi shi ne domin kaidi wa Musulunci da musulmi da rusa akidar tauhidi. Hakika masu wannan aiki sun sami asali ne daga kungiyoyi irin na Majusawa, Manawiyya da Mazdakawa wadanda suka shiga Musulunci a munafurce, ba tare da sun yi imani ba. Haka nan, akwai tunanin kiristoci da yahudawa a cikin wannan yunkurin rusawa([188]) (*).

Wadannan mabarnata sun bi wancan hanyar suka rudar da hankula da shuka rikici da kirkirar ruwayoyi da ra'ayoyi fandararru, suka danganta su ga Ahlulbaiti (a.s) bisa karya. Saboda haka manyan malami suka rubuta littattafai kan masu ruwaya wato Ilmul Rijal domin tona asirin makaryata da masu kirkira da masu munanan akida tun zamanin Manzon Allah (s.a.w.a.) har ya zuwa karshen jerin Imamai (a.s.), amintattun maruwaita daga Manzon Allah (s.a.w.a.). Ta hanyar ne suka jefar da duk wata ruwaya ta karya da kuma duk wani maruwaici mai kirkira ake gane shi, kamar yadda Najashi ya yi cikin sanannen littafinsa nan na Rijalul Najashi da Shaikh Dusi cikin littattafansa na Al-Fihrist da kuma Rijalul Dusi da dai sauransu.

Tarihi yana sanar mana samuwar wasu kungiyoyi fandararru wadanda suka danganta kansu da Ahlulbaiti (a.s) kamar 'yan Gullatu da 'yan Mufawwidha, alhali kuwa Ahlulbaiti (a.s) sun barranta da su, sun la'ane su da kuma koransu. Baya ga haka ma, malaman mazhabar Imamiyya (Shi'a) suna hukumta su da cewa su najasa ne.

Al-Nawbakhti([189]) (*) cikin littafinsa mai suna Firakush Shi'a ya ambato kungiyoyi daban-daban na 'yan Gullatu da 'yan Mufawwidha, da kuma ambaton matsayar Imaman Ahlulbaiti (a.s) dangane da su, ga kadan daga cikin abin da yake cewa:

"Amma batun sahabban Abul Khaddab Muhammad bn Abi Zainab al-Ajda al-Asadi da duk wanda yake da ra'ayi irin nasa, to lallai sun watse lokacin da suka ji cewa Imam Sadik (a.s.) ya la'anci Abul Khaddab, ya kuma barranta daga gare shi da sahabbansa". Har zuwa inda yake cewa: "Wata kungiya daga cikinsu ta ce Abu Abdullah Ja'afar bn Muhammad Sadik shi ne Allah - Allah Ya daukaka ga barin haka daukaka mai girma - sannan Abul Khaddab kuma Annabi ne mursali.

Wata kungiyar kuwa cewa ta yi: "Ja'afar bn Muhammad shi ne Allah - Wal iyazu billah- kuma Shi Allah (S.W.T.) wani haske ne mai shiga jikkunan wasiyyai ya kuma zauna a cikinsu. Wannan haske sai ya kasance shi ne Ja'afar bn Muhammad Sadik, sannan ya fita daga jikinsa ya shiga jikin Abul Khaddab([190]) ". Bayan al-Nawbakhti ya bijiro da wadannan batattun akidu sai ya ce:

"Wadannan kungiyoyin 'yan Gullatu masu da'awar Shi'a, sun sami asali ne daga addinan Kharmadaniyya(**) da Mazdakiyya([191]) (*)da Zindikiyya([192]) (**) da Dahriyya([193]) (***) duk madaurinsu guda ne, Allah Ya la'ancesu. Dukkansu sun tafi a kan kore rububiyyar Allah Mahalicci (Allah Ya daukaka ga barin hakan), sun kuma tabbatar da ita wa jikkuna ababen halitta da nufin wai jikkunan su ne bigiren da Allah Yake zama, sannan kuma shi Allah Ta'ala wani haske ne da ruhi mai ciratuwa daga wannan jikin zuwa wani. Face dai su sun sassaba ne kurum wajen shugabannin da suke bi, sashinsu yana barranta daga sashi yana kuma la'antarsa([194]) .

Al-Nawbakhti ya kara da nakalto fandararrun kungiyoyin da suka riga suka mace, masu fakewa da jingina kansu ga Ahlulbaiti (a.s) kamar haka:

"Wata kungiya ta ce wai Muhammad bn Hanafiyya dan Imam Ali (a.s.) 'shi ne Mahdi, Imam Ali ya kira shi da Mahdi, bai mutu ba kuma ba zai mutu ba, wannan ba ya halatta, sai dai kawai shi ya faku ne, ba a kuma san inda yake ba. Zai dawo ya mallaki kasa, babu wani Imami bayan fakuwarsa har zuwa dawowarsa wajen sahabbansa, su ne kuma sahabban Ibn Karb([195]) ". Sannan ya ce:

"Hamza bn Ammara al-Barbari cikinsu yake kuma shi mutumin Madina ne, sai ya rabu da su ya yi ikirarin cewa shi Annabi ne, shi kuma Muhammad bn Hanafiyya shi ne Allah - wal iyazu billahi -. Ya kuma ce shi ne Imam sannan kuma wasu abubuwa guda bakwai za su sauko masa daga sama, da su ne zai cinye dukkan kasa ya mallake ta. Ya kuma sami mutane daga Madina da Kufa da suka bi shi kan hakan. Imam Bakir (a.s.) ya tsine masa ya barranta daga gare shi, ya karyata shi, a sanadiyyar hakan ne kuma ya sa 'yan Shi'a suka barranta daga gare shi([196]) ".

Haka nan ma Imam Sadik (a.s.) ya la'anci Sa'id al-Nahdi wanda wadannan fandararrun kungiyoyin nan suke bi. Imam din ya kira shi shaidan, wanda ya yi wa Imam karya([197]) ".

Ga wasu ruwayoyin malaman Shi'a kan matsayin da Imam Sadik (a.s.) ya dauka dangane da wadannan 'yan Gullatu da kuma fandararrun ra'ayoyinsu. Misalin hakan shi ne abin da Imam din ya ce kan Abul Jarud da mabiyansa kamar yadda Ibnu Nadim ya nakalto cikin Alfihrist. "Imam Sadik (a.s.) ya la'ance shi ya ce: 'shi makahon zuciya ne da idanu([198]) '.

Kamar yadda kuma Imam din ya la'anci Abu Mansur al-Ajli, daya daga cikin 'yan Gullatu, an ruwaito cewa: 'Al-Kishshi ya kawo cikin Rijal dinsa shafi na 300 cewa Imam Sadik ya la'ance shi sau uku. Sannan kuma Yusuf bn Umar al-Thakafi, gwamnan Iraki, ya tsire shi a zamanin Hisham bn Abdul Malik([199]) '.

Hakika Imam Sadik (a.s.) ya bayyana matsaya kan wadannan 'yan gullatu, daga nan ya ambaci wasu daga cikinsu, su ne: Mughira bn Sa'id, Bazi, Sirri, Abul Khaddab Muhammad bn Abi Zainab al-Ajda', Mu'ammar, Bashshar Sha'iri, Hamza Barbari da Sa'id Nahadi, sai ya ce: "Allah Ya la'ance su, mu dai ba mu rabuwa da makaryata msu yi mana karya ko kuma wani mai gurgun tunani. Allah Ya isar mana ga dukkan makaryaci, Ya kuma dandana musu zafin karfe([200]) ".

A wani hadisin kuma Imam Sadik (a.s.) ya barranta daga 'yan Gullatu, inda yake cewa: "Ya ku jama'ar Shi'a - shi'ar Alu Muhammadu- ku kasance matsakaita, wadanda suka wuce gona da iri (masu guluwi) su dawo gare ku, wadanda kuwa suka yi nawa su risko ku". Sai wani mai suna Sa'id ya ce: 'Allah Ya sanya ni fansarka! Wane ne mai guluwi? Sai Imam ya ce masa:"Wasu mutane ne masu fadi game da mu, abin da mu ba mu fada ba, wadannan ba su daga gare mu, mu ma ba mu daga gare su". Sai mutumin ya ce: 'To wane ne mai nawa? Sai ya amsa masa da cewa: "Shi ne mai bidar (gaskiya) yana nufin alheri, alherin zai same shi kuma za a sakanta masa da shi([201]) ".

Daya daga cikin sahabban Imam Sadik (a.s.) ya ruwaito cewa yayin da Imam din ya sami labarin cewa Abul Khaddab na wuce gona da iri sai idanunsa suka cika da hawaye yana cewa:

"Ya Ubangiji, na barranta ya zuwa gareKa, daga abin da Al-Ajda yake ikirari a kaina, gashina da fatar jikina sun ji tsoronKa. Ni bawa ne a gare Ka dan bawanKa, makaskanci mai tawali'u".Daga nan sai ya sunku'i da kai na dan lokaci kamar yana ganawa da wani abu, sai ya daga kansa yana cewa:"Haka yake, haka yake! Bawa mai tsoro, makaskanci gaba ga Ubangijinsa, kankani, mai tsananin tsoro. Wallahi ina da Ubangijin da nake bautarSa, bana yi masa tarayya da kome. Me ya same shi (Abul Khaddab)? Allah ya kunyata shi, Ya zuba masa tsoro. Kada kuma Ya ba shi aminta daga firgici a ranar kiyama…..ba haka amsawar Annabawa take ba, ko ta mursalai, ba kuma amsawa ta ba. Amsawa ta kam ita ce fadar cewa: Ya Allah na amsa maKa, na amsa maKa Ya Allah ba Ka da abokin tarayya([202]) ".

Sadir ya ce: 'Na ce da Abu Abdullah (a.s.) cewa wasu mutane suna ikirarin cewa ku alloli ne, suna kuma kafa hujja da fadar Allah (S.W.T.) cewa:"Kuma Shi ne Wanda ke abin bautawa a sama, kuma bautawa a kasa"", (Surar Zukhruf aya ta 84),sai ya ce:"Ya kai Sadir! (Ka sani) jina da ganina da fatata da namana da gashina duk sun barranta daga wadannan mutane, Allah ma Ya barranta da ga gare su. Ba kan addinina wadannan suke ba, ba kuma kan na iyayena ba. Na rantse da Allah ba zai tara ni da su ba ranar lahira, kuma ba su zo a wannan rana ba face Allah Na fushi da su([203]) ".

Kamar yadda suka yi wa Imam Bakir da Sadik (a.s.) karairayi kuma suka barranta daga gare su, haka nan ma suka yi wa Imam Musa Kazim (a.s.) bayan shahadarsa. Suka ce bai mutu ba, sai dai kawai an daukake shi ne kamar yadda aka daukaki Annabi Isa (a.s.) kuma nan gaba zai dawo. Imam Ridha (a.s.) dan Imam Kazim (a.s.) sai ya barranta daga gare su, ya kuma la'ance su.

Kamar yadda Imam Sadik (a.s.) ya ce ba za a rabu da masu yi wa Ahlulbaiti (a.s) karya ba, domin su rikita tafarkinsu, domin kaidi ga Musulunci, haka nan Ahlulbaiti (a.s) suka bayyana matsayinsu dangane da wadannan masu niyyar ruguza Musulunci.

Yana daga ni'imomin Allah ga Musulunci da musulmi cewa wadannan kungiyoyi sun gushe, babu abin da ya rage sai ambatonsu cikin littattafan tarihi. Sai dai abin ban mamaki da takaici shi ne wasu masu mugun nufi suna danganta tafarkin Ahlulbaiti (a.s) da tatsuniyo-yi da barnace-barnace domin bakanta tafarkin Ahlulbaiti (a.s). Duk wani mai nufin alheri ba zai yarda da wannan ba bayan kuwa su Ahlulbaiti (a.s) da kansu sun barranta daga duk abin da ya saba wa tafarki madaidaici, kamar yadda muka ambata a baya. Babu shakka babu abin da masu sukar mabiya tafarkin Ahlulbaiti (a.s) suke yi face barazana ga hadin kan musulmi.

A daya gefen kuma, duk masu bincike suna iya ganin abubuwan da ake danganta su da sauran mazhabobin musulmi na akida, kamar su jabru da cewa Allah jiki ne kuma Yana zama a bisa kujera da cewa fadin kujerarSa taki bakwai ne, da cewa Allah zai shigar da kafarSa cikin wuta a ranar lahira sai Ya bice zafinta, da cewa Shi Yana saukowa nan duniya bisa wani farin jaki da dai sauransu.

Hakika a sarari yake cewa duk wadannan zantuttuka, kamar tatsuniyoyin Gulatu, suna warware akidar tauhidi, addinin Musulunci kuwa yana barranta daga gare su.

Tafarkin Ahlulbaiti (a.s) Wajen Tarbiyyar Mabiyansu

Imam Ja'afar Sadik (a.s.) ya ce: "Ni ina kin a ce mutum ya mutu alhali akwai wata ta'adar Manzon Allah (s.a.w.a.) da ta rage bai aikata ba([204])".

Babu shakka Ahlulbaiti (a.s) sun ba da muhimmanci kwarai wajen ilmantarwa da tarbiyyar mabiya da sahab-bansu da kuma shiryar da su zuwa hanya sahihiya ta tabbatar da rayuwa irin ta mai akida da halayen kwarai da biyayya ga hukumce-hukumcen Musulunci. Sun karfafa kan gina tarbiyyar musulmi bisa dacewa da Littafin Allah da Sunnar Manzon Allah (s.a.w.a.) domin samar da gwarzaye masu daukar hasken Musulunci da kira zuwa gare shi ta yadda hasken zai watsu kan sauran jama'a su amfana da ilmi da kuma aiki. Ahlulbaiti (a.s) sun yi hakan ne saboda tabbatar da haraka ta Musulunci cikin al'ummar duniya bayan da muggan manufofin masu neman ruguza addini suka bayyana ko ina. Muna iya ganin wannan kokarin nasu a fili cikin halayensu da wasiyyoyinsu da tarbiyyarsu ga mabiyansu. Daga cikin maganganun Imam Bakir (a.s.) akwai raddi kan masu cewa duk wanda ya kaunaci Ahlulbaiti (a.s) ba ya bukatar lizimtar farilloli Musulunci. Imam ya bayyana musu tafarkin Musulunci na gaskiya wanda Ahlulbaiti (a.s) suke kai, kuma suke kaunar dukkan musulmi ya yi riko da shi. Idan ba ka san shi ba, to shi ne tafarkin ilmi da akida ta gaskiya da aiki da duk abin da Alkur'ani ya zo da shi, Annabi (s.a.w.a) kuma ya iyar da shi ya kuma rayu a kansa. Imam din ya ce:

"Wallahi ba mu da wata kubuta daga Allah, babu wata dangantaka tsakaninmu da Allah, ba mu da wata hujja a kan Allah, kuma ba a kusantar Allah sai da biyayya. Wanda ya zama mai biyayya daga cikinku to jibintarmu za ta amfane shi, wanda kuwa yake mai sabo daga cikinku, jibintarmu ba za ta amfane shi ba([205]) ".

Amru bn Sa'id bn Hilal ya ce da Abu Ja'afar (a.s.): 'Allah Ya sanya ni fansar ka! Ni da kyar nake saduwa da kai, sai dai bayan shekaru, to ka yi mini wasicci da wani abin da zan rika', sai ya ce masa:"Ina maka wasicci da tsoron Allah da tsantsaini da kokari, ka sani cewa tsantseni ba ya amfani sai tare da kokari([206]) ".

Daga cikin abin da Imam Sadik (a.s.) ya yi wasicci da shi ga wani mabiyinsa, Abu Usama ya kuma umurce shi da ya isar da shi ga sauran mabiyansa, shi ne cewa:

"Ku ji tsoron Allah ku kasance ado a gare mu, kada ku zamo abin kyama. Ku janyo mana dukkan soyayya, ku ije mana duk wani mugun abu, domin mu ba kamar yadda aka fada dangane da mu muke ba. Muna da hakki cikin Littafin Allah da dangantaka da Manzon Allah (s.a.w.a.) da tsarkakewa daga Allah, da haifayya tsarkakakkiya, ba mai ikirarin hakan, koma bayanmu, face makaryaci*. Ku yawaita ambaton Allah da tuna mutuwa da karatun Alkur'ani da salatin Annabi (s.a.w.a) domin akwai (ladan) kyawawan aiki goma ga ko wane salati a gare shi([207]) ".

Imam Sadik (a.s.) ya yi wasicci wa Isma'il bn Ammar, daya daga cikin sahabbansa, da cewa: "Ina ma wasicci da tsoron Allah da tsantseni da gaskiya cikin magana da mai da amana da kyautatawa makwabta da yawan sujada, don da wannan ne Annabi (s.a.w.a) ya umurcemu([208]) ".

Hisham bn Salim ya ce: 'Na ji Abu Abdullah (a.s.) yana fada wa Hamran cewa: "Ka dubi wanda ya kasa ka, kada ka dubi wanda ya fi ka, domin haka ya fi (tabbatar da) wadar zuci ga abin da aka yanka maka, kuma za ka fi cancantar kari daga Allah. Ka sani cewa kadan na dawwamammen aiki wanda aka yi yakini, a wajen Allah, ya fi mai yawa dawwamamme amma babu yakini a cikinsa. Ka sani cewa babu tsantsenin da ya fi nisantar ababen da Allah Ya haramta, da kuma kamewa ga barin cutar da musulmai da yi da su. Babu kuma abin da ya fi kyan hali faranta rai. Kuma babu dukiyar da tafi amfani daga wadatuwa da kadan mai biyan bukata. Babu jahilcin da ya fi jiji da kai daci([209]) ".

Imam Sadik (a.s.) ya ruwaito daga Manzon Allah (s.a.w.a.) kan siffofin muminai cewa: "Wanda ya yi bakin cikin mummunan aikinsa, ya yi farin ciki da kyakkyawan aikinsa, to mumini ne([210]) ".

Wadannan bayanai suna nuna siffar mumini mai riko da addini irin wanda Ahlulbaiti (a.s) suka yi kokarin samarwa kuma wannan shi ne tafarkinsu na tarbiyyar al'ummar musulmi. Shi ne kuma kiran da suka yi wa al'ummar Annabi (s.a.w.a) na lizimtar Littafin Allah da Sunnar Ma'aiki (s.a.w.a.) da gina rayuwa bisa wannan shiriya da tafarki mai karfi. Babu abin da ya fi dacewa ga musulmi sai bin shiryarwarsu da wasiccinsu da kuma wa'azinsu.

Gudummawar Ahlulbaiti (a.s) A Fagen Siyasa

Babu shakka al'ummar musulmi ta san matsayin Ahlulbaiti (a.s) da hakkinsu a kan wannan al'umma na shugabantarta. Domin haka ne za a iya ganin cewa Ahlulbaiti (a.s) suna matakin kololuwa a fagen siyasa da shugabancin Musulunci, domin su shiryar da al'umma, su tabbatar da gyara da aiwatar da hukumce-hukumcen addini da tsayar da adalci.

Duk wanda ya karanci tarihin Musulunci zai gani a sarari cewa shugabantar al'umma bayan zamanin Khulafa'u al-Rashiduna ta koma mulukiyya mai dora kanta bisa bayin Allah da jan hankulansu da dukiya da mukamai da kuma dankwafe hukumce-hukumcen shari'a da wasa da su. Wannan wasa da shari'a da makomar al'umma ya janyo sassabawa da juyin-juya-hali da jayayya mai tsanani da zubar da jinin kungiyoyi masu sabanin ra'ayoyi da tunace-tunace masu warware juna sun zama sakamakon wannan. Wasunsu suna goya wa sarakuna baya kan zaluncinsu da kuma horar da mutane su mika wuya da hana su bijirewa da warware mubaya'arsu ga azzalumai. Wasu kuma sun yi amfani da wannan damar (ta jayayya tsakanin musulmi) wajen tabbatar da mugun nufinsu na ruguza addini yayin da suka dora kira da halalta dukkan haram da dukiyoyi da mata da rusa wajibai, kungiyoyi irinsu 'yan Karamida, Mazdakiyya da Kharmiyya da dai sauransu. Wasu kuma suka dora kira zuwa ga rudani da rusa dukiyar hukuma da zubar da jini da kafirta kowa da kowa kamar su Khawarijawa.

Da wannan fantsamar ra'ayoyin siyasa masu sassabawa da fitinu da yake-yake na cikin gida, al'umma ta fuskanci hadari mai munin gaske. Ahlulbaiti (a.s), a matsayinsu na jagororin al'umma, sun kasance mafus-kanta da tushen sakon Musulunci wanda duk wata mishkila ta akida da tunani wacce ta kalubalanci musulmi ana iya warware ta a hannunsu. Domin wannan matsayi nasu na matabbacin tafarkin gaskiya, musulmi suna bin ra'ayinsu da riko da matsayin da suka dauka kan al'amurra. Face wadanda suka damfaru da masu iko, masu kare ayyukansu domin biyan bukatar kansa. A nan za mu yi dubi cikin tafarkin Ahlulbaiti (a.s) akan abubuwan da suka shafi ayyukan siyasa.