Ziyarar Kabari

Ziyarar Kabari0%

Ziyarar Kabari Mawallafi:
: Shekh Hafiz Muhammad Sa'id
: Shekh Hafiz Muhammad Sa'id
Gungu: Raddin Shubuhohi

Ziyarar Kabari

Mawallafi: Ayatul-Lahi Subhani
: Shekh Hafiz Muhammad Sa'id
: Shekh Hafiz Muhammad Sa'id
Gungu:

Budawa: 7055
Gurzawa: 2186

Bayanai:

Bincike Cikin Littafi
  • Farawa
  • Na Baya
  • 30 /
  • Na Gaba
  • Karewa
  •  
  • Gurzawa HTML
  • Gurzawa Word
  • Gurzawa PDF
  • Budawa: 7055 / Gurzawa: 2186
Girma Girma Girma
Ziyarar Kabari

Ziyarar Kabari

Mawallafi:
Hausa

Tafiya Domin Ziyarar Kabarin Manzo (S.A.W)

Ziyarar Kabarin dukkan musulmi da musamman ziyarar kabarin Manzo wani abu ne wanda yake mustahabbi mai karfi a cikin musulunci. Sannan malaman hadisi daga Sunna da Shi’a sun ruwaito hadisai da dama a kan mustahabbancin ziyarar kabarin Manzo wadanda wasu daga cikinsu sun gabata a cikin bahasin da ya gabata ta yadda babu wani malami daga cikin malaman musuluncin da ya ba kansa damar yin shakku a kan mustahabbancin ziyarar Manzo. Wannan kuwa ya hada har da Muhammad bn Abduh wanda yake da wasu masatlolin dangane da abin da ya shafi annabawa, a nan ba kawai ya yi shiru ba ne, sai dai ya yi magana a kan mustahabbcin ziyarar Manzo (S.A.W). Sannan mun kawo abin da yake cewa dangane da hakan a bahasimmu na baya. Tare da la’akari da kasantuwar mustahabbicn ziyarar Manzo, amma msulmi sun kasu a kan wannan kyauta ta ubangiji:

1-Mazauna Madina

Mazauna Madina sakamakon makwautaka da suke da ita da Manzo (S.A.W). Suna iya ziyartarsa ba tare wata wahala ba don aiwatar da wannan mustahabbi.

2-Mazauna sauran wurare a cikin duniya

Mazauna sauran sassan duniya dole ne su yi tafiya domin su damar yin sallama ga kabarin Manzo Su ce: "Amincin Allah ya tabbata a gareka ya manzon Allah".

A nan tambaya ita ce; menene hukuncin wannan tafiya a shari’a?

Jawabain wannan tambaya kuwa a fili yake domin wannan amsa tana matsayin gabatarwa ce domin aiwatar da aikin mustahabbi, saboda haka a akidar wasu malamai tana matsayin mustahabbi, wasu kuwa suna cewa tana hukuncin halal "Mubah" ne.

Duk yadda ta kama kasantuwar wannan tafiya domin aiwatar da mustahabbanci ce ba zata taba zama haramun ba. Domin kuwa ba zai inganta ba a hankali Allah madaukaki ya umurce mu da aikin mustahabbi na ziyartar Manzo sannan ya haramta abin da yake matsayin gabatarwa ne domin aiwatar da wannan aikin. Saboda haka daga nan muna iya gane cewa hukuncin wannan tafiya domin aiwatar da wannan aiki ta halitta. [48]

Kamar yadda yake a tarihi shi ne musulman da suke rayuwa a sauran sassan duniya wato ba wadanda suke rayuwa ba a garin Madina sukan daure kayansu domin tafiya zuwa ziyarar kabarin Manzo mai girma a nan ga wasu misalai a kan hakan:

Bilal wanda yake mai kiran salla ne na Manzo kuma Manzo ya kasance yana kaunarsa. Bayan tafiyar Manzo ya zabi ya tafi wani wuri yiwa musulunci hidima, sakamakon haka ne ya yi hijara daga garin Madina. Wani dare sai ya ga Manzo a cikin mafarki yana ce masa: Wannan wane irin rashin kulawa ne Bilal? Yanzu lokaci bai yi ba da zaka ziyarce ne?

Lokacin da Bilal ya tashi daga barci yana cikin bakin cikin da ya mamaye masa zuciya, sai kawai ya tanaji abubuwan bukata domin yin tafiya kuma ya tafi zuwa Madina. Lokacin da Bilal ya shiga a cikin Raudar Manzo yana kuka da murya mai karfi a wannan hali ya dinga goga fusakarsa a kan kabarin Manzo (S.A.W). A nan haka sai kwatsam abin kaunar? Manzo wato Hasan da Husain (A.S) sai suka yi wajensa sai ya kama su ya runguma, sai suka ce masa, Muna tsananin son mu ji muryar kiran sallarka, kiran sallar da kake yi wa kakanmu manzon Allah (S.A.W).

A lokacin sallar Asubahi sai Bilal ya hau wurin da ya kasance yana kiran salla a zamanin Manzo (S.A.W) ya kira salla. A lokacin da kiran sallarsa ya mamaye Madina Ya girgiza garin Madina a wannan lokaci, a lokacin da ya yi kalmar shahada a cikin kiran sallarsa sai duk mutane suka daga murya suna kuka, a lokacin da kuwa ya yi shahada a kan manzancin Manzo (Ashhahadu anna Muhammadar Rasulullah) ai sai duk mutanen Madina suka yi waje suna kuka. Kamar yadda ake rubutawa: Bayan ranar da Manzo ya yi wafati madina ba ta taba ganin irin kukan da ta gani ba a wannan lokaci.[49]

2-Umar bn Abdul Aziz ya kasance yana hayar mutane domin su zo daga Sham zuwa madina domin su yi masa sallama ga Manzo. Subki a cikin Futuhus Sham yana rubuta cewa: Lokacin Umar bn Abdul Aziz ya yi Sulhu da mutanen Kudus sai Ka’abul Akhbar ya shigo wajen kuma ya musulunta, a wannan lokaci Umar ya ji dadi kwarai da musuluntarsa. Sai Umar ya ce masa: Kana iya bi na mu tafi madina mu ziyarci kabarin Manzo ta yadda zamu fa’idantu da ziyararsa? Sai Ka’ab ya amsa wa khalifa abin da ya nema daga gareshi, ya yi shirin tafiya tare da khalifa. A lokacin da Umar ya shiga garin madina, farkon abin da ya fara yi shi ne ya shiga masallacin Manzo ne domin ya yi wa Manzo sallama.[50]

Duk da yake ba mu da bukatar mu kafa sheda a nan da irin wadannan misalai, domin kuwa al’ummar musulmi duk tsawon karnoni? sha hudu sun dauki wannan al’amari na ziyara Manzo a matsayin mustahabbi kuma suna tafiya Madina domin su aiwatar da wannan mustahabbi.

Subki dangane da tafiyar ayari-ayari zuwa ziyarar Manzo ya yi maganganu da dama a kan hakan, ya kara da cewa masu ziyara bayan sun gama aikin hajji sukan kama hanyar Madina ne domin su kai wa Manzo ziyara, ya kara da cewa: wata sa’a sakamakon fahimtar ladar da yake cikin yin hakan sukan dauki hanyar da tafi nisa zuwa Madina, domin su samu lada mai yawa a kan haka. Sannan ya cigaba da cewa, wadanda suke tunanin cewa dalilin da ya sa mutane suke tafiya madina shi ne domin su ziyarci masallacin Manzo kuma su yi salla a ciki wannan kuskure ne, domin kuwa abin masu ziyarar suke fada ya saba wa wannan tunanin. Domin manufarsu a kan wannan ziyara shi ne su ziyarci kabari Manzo, sannan wannan shi ne gurinsu na ziyarar Madina. Domin kuwa idan manufarsu a kan wannan tafiya shi ne ziyartar masallaci, me ya sa ba su tafiya Kudus domin su ziyarci masallacin baitil mukaddas wanda yin salla a cikinsa bai gaza wa yin salla a masallacin Manzo ba?

Kamar yadda yake haduwar malamai a kan wani hukunci yana nuna ingancin wannan hukunci a shari’a haka nan haduwar dukkan musulmi a kan wani aiki yana nuna mafi daukaka kasantuwan wannan abin a cikin shari’a.[51]

Masu Haramta Tafiya Don Ziyarar Manzo

Har zuwa karshen karni na bakwai malamai sun hadu a kan wannan al’amari cewa tafiya domin aiwatar da wani aiki na mustahabbi koda ba ta zama mustahabbi ba to alal akalla ta halasta. Amma a farkon karni na takwas, Sai Ibn Taimiyya ya yi riko da hadisin Manzo wanda Abu Huraira ya ruwaito ta yadda ya saba wa dukkan malamai da suka hadu a kan wannan al’amari. Wannan ruwaya kuwa da Ibn taimiyya ya yi mafani da ita, an ruwaito ta ne ta fuska guda uku, amma abin da yake iya tabbatar wa Ibn taimiyya da manufarsa ya zo da fuska biyu ne kamar haka:

1- Kada a yi nufin tafiya sai zuwa masallatai guda uku: Wannan masallaci nawa, masallacin ka’aba da Masallacin Kudus.[52]

2- Ana yin tafiya ne kawai zuwa ga masallatai guda uku[53], Ibn taimiyya ya yi riko ne da zahirin wannan hadisi domin tabbatar da manufarsa, ta yadda ya yi da’awar cewa domin aiwatar da ayyukan ibada masallatai uku ne kawai mutum zai iya zuwa domin yin hakan. Saboda haka ziyarar Manzo wanda yake matsayin ibada ba ya daya daga cikin wadannan abubuwa guda uku. Wannan kafa hujja ta Ibn Taimiyya kuwa idan muka lura da kyau zamu iya gane rashin ingancinsa, domin kuwa ba shi da kafafu masu karfi.

Domin kuwa mun san cewa jumlar da take kebewa tana ginuwa daga sassa guda biyu kamar haka:

1-Jumlar da ake kebewa daga gareta: "Ba wanda ya zo wurina".

2- Jumlar da a ka kebance "Sai Ali"

Hadisin da ya gabata ya ginu ne ta hanyar jumloli biyu ne:

1-jumla ta farko jumlar da aka kebance daga gare ta "Kada ku yi tafiya. "

2-Jumla ta biyu kuwa, wadda aka kebance: "Sai masallatai uku".

A jumlar ta farko abin da aka kebance bai fito ba a fili, bisa la’akari da ka’idar larabci a nan dole mu kaddara wata jumla, wadda zata iya zama daya daga cikin wadannan jumloli guda biyu kamar haka:

1-Mai yiwuwa ka iya cewa "masallaci" ne. (wato kada ka yi tafiya zuwa kowane masallaci sai masallatai guda uku)

2-Mai yiwuwa ana nufin "wuri" ne (kada ka yi tafiya zuwa wani wuri sai masallatai guda uku) Saboda haka bisa ga tsammani na farko, zai zama ma’anar jumla zai zama haka, wato kada ka yi tafiya zuwa kowane masallaci sai masallatai guda uku da aka ambata.

Saboda haka idan muka dauki wannan ma’ana zai zama cewa Manzo yana magana ne a kan masallatai, wato don mutum ya yi salla kada ya yi wahala don tafiya kowane masallaci sai masallatai guda uku da aka ambata. Saboda haka a nan ziyarar Manzo ba ta cikin abin da aka hana a cikin wannan hadisi domin ba a kansa ake Magana ba. Sannan dalilin da ya sa aka yi hani tafiya wani masallaci domin yin salla domin sauran masallatai hukunci guda garesu babu wani wanda ya fi wani daraja daga cikinsu, saboda haka yayin da mutum yake da damar yin salla a daya daga cikin masallatai me zai sanya ya sha wahala domin ya tafi waninsa.

Misali kamar idan akwai masallacin jumma’a a wani gari me zai sanya mutum ya tafi wani gari domin ya yi sallar jumma’a a can, domin kuwa ladar da zai samu a wancan masallacin ba ta dara wadda zai samu ba a wannan na garinsu.

Amma dangane da wadancan masallatai uku abin ba haka yake ba, domin salla a cikin daya daga cikinsu ya fi salla a cikin sauran masallatai, saboda haka tare da kula da cewa a cikin wannan hadisi an yi magana ne kawai a kana masallatai, don haka tafiya zuwa wasu wurare bai shafi wannan hani na hadisi ba, saboda haka ba ya magana a kan halasci ko haramcin yin hakan.

Amma idan muka dauki ma’ana ta biyu ma’anar wannan hadisi zata kasance kamar haka: kada ka yi tafiya sai zuwa wurare guda uku (masallatai guda uku da muka ambata).

Idan muka dauki wannan ma’ana dogaron Ibn Taimiyya yana iya zama dai-dai. Amma tare da lura da yadda tarihin musulmai ya tafi a kan mustahabbacin tafiya zuwa kabarin Manzo (S.A.W), domin ziyara tana nuna mana rashin ingancin wannan hadisi.

Na farko kamar yadda muka gani a cikin hadisin da ya gabata, ana iya tsammanin wata ma’ana daban, sakamakon wannan ma’ana kuwa ba za a samu wani fito na fito ba a hadisai da ayoyi da kuma tarihin musulmi da suke nuni a kan halascin ziyarar Manzo. Kuma tare da daukar ma’anar farko musamman kasantuwar mu dauki cewa kalmar da zamu iya kaddarawa ita ce masallaci, domin kasantuwar dacewarta da abin da ya zo a cikin jumlar, kuma shi ne abin da ya fi dacewa ya kuma fi karfi. Saboda haka wannan hukunci wanda Ibn Taimiyya ya dauka zai zama sam ba shi da ma’ana a nan.

Haka nan idan muka dauki ma’ana ta biyu wato muka dauka cewa ai a nan ana nufin "wuri" wato bai halitta ba mutum ya tafi wani wuri sai wadannan wurare guda uku, wannann kuwa zai bayar da ma’anar da ba ta dace ba, sannan fitowar wannan kalma daga mai hikima musamman Manzo ba zai yiwu ba. Wato ya zama an hana zuwa kowane wuri sai wadannan wurare guda uku (Masallacin ka’aba, Kudus da Masallacin Manzo). alhalin musulunci ya halatta wasu tafiye-tafiye da dama a cikin musulunci wasu daga cikinsu ma mustahabbi ne. Misali kamar tafiya domin neman ilimi, ko tafiya domin kasuwanci ko tafiya don sada zumunci, tafiya don yawon bude ido, tafiya domin jihadi da dai sauran tafiye-tafiye da suke halas wadansu ma mustahabbi a musulunci.

Saboda haka a nan dole ne mu dauki ma’ana ta farko wato masallaci, cewa kada mutum ya yi tafiya domin ya je wani masallaci sai masallatai guda uku, domin kuwa su ne su kafi sauran masallatai matsayi. Da wannan ne zamu fitar da batun tafiya domin ziyarar Manzo domin ba ita ake magana ba a cikin wannan hadisi.

Bayan dangane da ingancin wannan hadisi koda an dauki ma’ana ta farko, akwai shakku a cikinsa. Domin kuwa yana nufin wannan magana ta fito daga bakin Manzo inda take nuni da cewa tafiya zuwa kowane masallaci ba ta inganta sai masallatai guda uku. Alhali kuwa ruwayoyi sun zo a kan cewa Manzo (S.A.W). Wasu ranakun Asabar yakan tafi kasa, wata sa’a bisa abin hawa domin ya je masallacin "Kuba?" domin ya yi salla raka’a biyu a wajen. Wannan masallaci a zamanin da Manzo yake a raye yana da tazarar kilo mita 12 tsakaninsa da Madina.[54]

Ziyarar Masallatai Guda Bakwai

A sassa daban-daban na garin Madina akwai wasu masallatai guda bakwai wadanda mahajjata sukan ziyarta yayin da suka je Madina, Idan ma muka kara da (masallacin Raddi shams, da na Bilal da na Ijaba) Yawansu zai wuce bakwai. Mahajjata suka yi salla raka’a biyu a wadannan masallatai musamman sukan fi ba da muhimmanci a kan masallacin Imam Ali (A.S) Yanzu tambaya zata iya zuwa cewa: Idan har yin salla a wadannan masallatai ba shi da wani fifiko a kan sauran masallatai, to me ya sa mahajjata suke zuwa ziyarar wadannan masallatai sannan su yi salla a cikinsu? alhali kuwa wannan bai zo ba a cikin shari’a, saboda haka wannan zai zama "Bidi’a" kenan a cikin addini.

Amsar wannan tambaya kuwa a fili take:

Tafiya domin ziyarar wadannan msallatai ba wai don yazo a cikin shari’a ba ne, ko kuma yin salla a cikin wadannan masallatai yana da wani fifiko na musamman, sam ba haka ba ne manufar tafiya zuwa wadannan wurare sai daya daga cikin biyu ne kamar haka:

1-Tunawa da musulman farko wadanda suka kasance cikin mawuyacin halin yakin Khandak amma a cikin wannan hali ne suka gina wadannan masallatai don su yi salla kuma suka cigaba da yakinsu. Domin kuwa wasu daga cikin wadannan masallatai suna wuraren da aka gwabza tsakanin sojojin tauhidi da na shirka yayin da aka kashe gwarzon shirka (Amru bn Abdu wud) kuma sakmakon haka ne gwamnatin dagutu ta kawo karshe.

Halartar musulmi a wadannan wurare tana tuna musu da wadannan abubuwa da suka faru a wannan wuri, sannan yana kara karfafa alakarsu da wadancan musulman farko.

2-Amma ma’ana ta biyu kuwa da zata iya zama dalilin da ya sa musulmai suke zuwa wadannan masallatai ita ce, domin neman tabarraki daga wadannan wurare, domin jinanan shahidai a kan hanyar tauhidi a wadannan wurare ne ya zube, Saboda haka wannan wurare sun sheda kai da kawon shahidan musulunci, sannan kuma wuri na kai-da-kawon manyan musulmai.

Wadannan manufofi su ne suke sanya musulmi suna tafiya zuwa wadannan wurare da makamantansu, kamar wurin da aka yi yakin khaibar da Fadak, duk sun samo asali ne daga wadannan manufofi guda biyu.

Amma yin salla a wadannan wurare bayan musulmi sun shiga wadannan masallatai domin aiwatar da umarnin ubangiji cewa duk yayin da mutum ya shiga wani masallaci to ya gabatar da salla raka’a biyu a matsayin gaisuwa ga shi masallacin. Saboda haka ba wannan ba ne hadafinsu na zuwa wadannan masallatai ba domin su gabatar da salla a wajen. Wannan niyya tana zuwa ne bayan sun shiga masallatan.

Girmama Kaburbura Masu Tsarki

Al’ummun da suke raye a kasashen da suka cigaba a duniya zaka ga suna kokari wajen kare kayan tarihi kuma suna nuna soyayyarsu ga wadannan abubuwa na tarihi. Sannan suna iya kokarinsu da su kare wadannan kayan tarihi don kada su bata ko su lalace. Domin kiyaye wadannan kayan tarihi kuwa wadanda suke nuna cigabn su a tsawon tarihi har ma’aikatu na musamman suka samar da ma’aikata kwararru domin kawai wannan aiki. Sakamakon haka ne ba su ba da wata dama da zata sanya wani guntun abu daga cikin wadannan kayan tarihi da suka hada da wani allo wanda aka yi wani rubutu a kai ko guntun jirgin ruwa da ya bata. Domin sun yi imani da cewa wadannan kayan tarihi suna ba da wata sheda ce ta musamman ta su wadannan al’umma. Mutanen da suka yanke daga al’ummarsu da manyan tarihinsu da suka gabata suna da hukuncin yaro ne wanda ya bata daga hannun iyayensa. Cigaban musulunci wani cigaba ne wanda yake mai girman gaske wanda a karnonin tsakiya shi ne kawai cigaban da babu kamarsa.

Sakamakon koyarwar da Musulmai suka samu daga littafinsu na sama, sun kafa cigaban da ba a taba yinsa ba a tarihi. Wanda ya kai kololuwarsa a cikin karni na hudu, ta yadda gabas da yammacin duniya suka shaida haka, kamar yadda ya gina Tajmahal na kasar Indiya da Kasar (Spain) sauran gine-gine masu ban al’ajabi, wanda ta hanyar kaitsaye ko kuma ba kaitsaye ba. Kamar yadda masana na yamacin duniya suka tabbatar da cewa cigaban yammacin duniya ya samu asali ne ta hanyar Andulus ko kuma ta hanyar yakin da ya auku tsakanin musulmi da kiristocin yammacin duniya.

Cigaban musulunci ya fara ne da aiko manzon Musulunci (S.A.W) ko kuma da wata ma’ana ya fara ne da haihuwar shi manzon, Sannan da taimakon mabiyansa ya cigaba ta kafuwa da yaduwa a sauran sassan duniya. Gine-ginen da suke dangane da Manzo ko kuwa wasu daga cikin sahabbansa suna daga cikin wannan cigaba na musulunci. Sannan kuma wannan ba mallakin wani ba ne ta yadda zai yi abin da ya ga dama da su, wannan na dukkan al’ummar musulmi ne. Saboda haka babu wata hukuma ko wasu mutane da zasu yi abin da suka dama da wannan kayan tarihi da cigaban musulunci ba tare da izinin sauran musulmi ba. Ta yadda ta hanyar yaki da bidi’a da tsayar da tauhidi su kawar da wadannan kayan tarihi.

Tarihin musulunci yana gaya mana cewa: An haifi manzon musulunci ne a shekara ta 570 bayan haihuwar Annabi Isa (A.S) Sannan bayan ya kai shekara 40 da haihuwa aka aiko shi a manzanci. Bayan aiko shi da manzanci ya yi shekara 13 a garin Makka yana isar da wannan sako. Bayan wannan ne tare da umarnin ubangiji ya bar inda aka haife shi zuwa garin Madina, Inda a can ne ya yi shekara 10 yana isar da wannan sako na musulunci kuma ya yi fito na fito da mushrikai makiya musulunci, sakamkon bayar da shahidai da ya yi a wannan hanyar ya samu damar daga tutar musulunci a dukkan yankin kasashen Makka da kewayenta (yanki mai girma daga cikin Jaziratul Arab) A shekara ta 11 bayan hijara ne ya koma zuwa ga rahamar Ubangijinsa. Sannan bayan wafatinsa Sahabbansa suka cigaba da wannan aiki na yada musulunci a sassan duniya daban-daban.

Wannan kuwa ya shafi rayuwar da kokarin Manzo da iyalansa da da mabiyansa ne (kamar yadda muka fadi cewa shi ne tushen wannan cigaba) Saboda haka dole mu yi kokari wajen kare wannan asali.

Kaburburan Shugabannin Addinin Musulunci Suna Nuna Tarihin Musulunci

Dole ne mu kula da cewa duk wani abu da zai faru a wani zamani yana kore duk wani shakku ga wadanda suke rayuwa a wannan zamani. Amma tare da gushewar zamani sakamkon ko-in-kula na mutane zai sanya wannan yakini da tabbas da yake ga mutane ya ragu. Ta yadda a hankali zai zama ana shakku da tararrabi a kan faruwar wannan abin, ta yadda wani lokaci ma zai koma kamar wata tatsunniya. Abubuwan da suka faru ga addinan da suka gabata a lokacin da suka faru babu wani shakku ko taraddudi a kan faruwarsu, amma sakamakon rashin kulawa a yau sun zama kamar tatsunniya.

Maimaita wannan mummunan al’amari dangane da musulunci yana da matsala fiye da yadda ya faru a sauran addinan da suka gabata. Domin kuwa addinin musulunci addini ne wanda har zuwa ranar tashin kiyama dukkan mutane dole ne su yi biyya a gare shi, ta yadda zasu sadu da haske ta hanyar hakan. Mutanen da zasu zo nan gaba kuwa zasu iya biyayya ga wannan addini yayin da suka kasance sun samu yakini dangane da hakikaninsa.

Babu shakka daya daga cikin hanyar kiyaye wannan tabbaci na hakikanin addinin musulunci kuwa shi ne kiyaye abubuwan da suka shafi rayuwar Manzo da sauran shugabannin addinan musulunci.

Magabatanmu Allah ya rahamshe su, sun yi hidima mai yawa dangane da al’ummar yanzu, ta yadda suka kiyaye mana abubuwan da suka zo tun farkon zuwan musulunci. Sakamakon haka ne kai tsaye muke kiran sauran al’umma zuwa ga wannan addini wanda yake hakikaninsa bai samu wani canji ba, ta yadda muke cewa: Karni goma sha hudu ne da suka gabata shugaban Bani Hashim ya ta shi da manzanci daga Allah ya kuma kira mutane zuwa ga Tauhidi da kaurace wa bautar gumaka da kafirci, bayan Mu’ujizozin da ya zo da su. Sannan ya zo da littafi mai girma wanda ya karya makiyansa da shi. Sannan har zuwa yanzu wannan Mu’ujizata har abada tana nan ba tare da wani canji ba.

Wanda kafin ya fara bayyana kiransa ya kasance yana tafiya kogon hira domin yin ibada ga Allah madaukaki. Bayan cika shekara arba’in da rayuwarsa ya fara kiransa. Wasu mtane daga cikin mutanen Makka suka yi imani da shi, yayin da wasu mafi yawa suka kaurace masa, har ma suka yi nufin su hallaka shi, amma Allah da ikonsa ya boye shi a wani kogo da ake kira (Thaur) wanda yake kudancin garin Makka, ta yadda ya tsira da makiya. Bayan nan kuma ya yi hijira zuwa garin Madina, a wannan gari ne mutane Aus da Khazraj (wadanda ake kira da Ansar) suka amsa kiransa suka taimake shi. Manzo a tsawon zamansa a garin Madina ya gwabza yaki mai tsanani tsakaninsa da mushrikai da Yahudawa, Ta wannan hanyar ne ya gabatar da shahidai da dama a tafarkin Allah ta yadda suka ba da jinansu a yakin Uhud, Khaibar da Hunain. Manzo (S.A.W). Ta hanyar aika mabiyansa zuwa sassa daban-daban na wannan nahiya ta kasashen larabawa ya samu damar isar da sakonsa zuwa ko’ina a wannan lokaci. A shekara ta 11 ne bayan hijira ya koma zuwa ga ubangijinsa kuma ya yi umarni da rufe shi a cikin dakinsa. Bayan wafatinsa mabiyansa suka cigaba da hanyar da ya bari, ta yadda ba tare da bata lokaci ba, ya yada wannan addini tare da al’adun da Kur’ani ya zo da su a dukkan sassan duniya.

Wannan shi ne wani yanki na tarihimmu wanda bayan wucewar karni 14 ake maimaita shi. Saboda haka dole mu yi kokarin wajen kare wannan tarihi na mu da duk abin da ya shafi hakan, ba wai ta hanyar wasu dalilai ba marasa tushe mu ruguza wannan tarihi namu!.

Kamar yadda ya kasance mu shagala game da kiyaye wadannan kayan tarihi, ta yadda babu bambanci a wurin dangane da samuwarsa da rashinsa duk daya yake, (abin da ma ya fi muni shi ne yadda ake ganin cewa rusa wadannan abubuwa yaki ne da yaduwar shirka) Ta yadda a cikin kankanin lokaci an manta da wasu abubuwa na tarihin musulunci, don ha ka bayan wani lokaci zai yiwu a fara shakku dangane da wasu abubuwa na hakikanin wannan kira da Manzo ya zo da shi. Ta yadda kamar su Salman Rushudi maimakon canza addini sai ya yi kokarin inkarin addinin da tarihinsa baki daya.

Daukar Darasi Daga Tarihi

Mutum kodayaushe yana kokari ne ya kalli kowane al’amari ta hanyar idanu ko makamancinsu, domin kuwa ilimin da yake samuwa ta wannan hanya mutum ya fi dogara a kansa. Cikinsa a babban hanyar da ake bi domin tabbatar da wani abu dangane da abin da ya shafi rayuwar zamantakewa, kuma wanda aka fi dogara da shi domin yana ba da sakamakon da ake samun yakini, shi ne tarihi, Kur’ani mai girma yana ba da tarihin magabata ne domin daukar darasi. [55] Dangane da shari’un da suka zo daga sama muna iya daukar shari’ar Annabi Isa (A.S) a matsayin misali. A akidar musulmi Annabi Isa matsayin annabin Allah yake, wanda yake mai albishiri ne ga zuwan Manzo Muhammad (S.A.W), sannan ya zo da littafi mai suna "Injil" wanda yake dauke da haske a cikinsa, amma muna samun tabbas a hakan ne ta hanyar Kur’ani mai girma.

Amma sakamakon matashin da yake yammacin duniya ba shi da imani da Kur’ani ta yadda zai kalli Annabi Isa ta wannan fuskar, a yau dangane da zuwan Annabi Isa da littafinsa yana da shakku a kansu. Domin kuwa ba shi da wata alama ta wannan kira a hannunsa ta yadda zata taimaka masa ya samu yakini a kan hakan. Domin kuwa Masih ba shi da kabari ko mahaifiyarsa da sahabbansa da zasu tabbatar da zuwansa. Sannan littafinsa an hakaito shi ta hanyoyi daban-daban ta yadda zai yi wahala mutum ya gane gaskiyar al’amarin. A takaice babu wani abu wanda zai tabbatar wa matashin yammacin duniya gaskiyar zuwan Annabi Isa da littafinsa. Saboda haka sabanin magabatansa yana shakku a kan hakikanin wannan al’amari.

Saboda haka mu musulmi dole mu dauki darasi daga wannan abin da yake faruwa daga kiristanci. Ta yadda zamu kiyaye duk wani abu wanda yake ya zo daga Manzo kuma yana matsayin sheda ne ga da’awar da shi Manzo ya zo da ita, (duk yadda ya kasance abu dan karami ne) Ta yadda zamu kare duk wani abu wanda zai sanya wadanda zasu zo bayammu su yi shakku a kan gaskiyar addinin musulunci, kamar yadda matashin yammacin duniya yake shakkun gaskiyar Annabi Isa da Injila.

Muna iya amfana daga ayoyin Kur’ani da suke nuni da cewa: Al’ummun da suka gabata sun kasance suna kiyaye duk wani abin da manzonsu ya zo da shi, ta yadda suke tafiya da shi yayin wani kwami mai zafi da yake a gabansu. Ta yadda ta hanyar neman albarkaci da wannan abin daga annabawansu don neman samu cin nasara daga mushrikai abokan gabarsu. A matsayin misali Bani Isra’il sun kasance suna tsaron wani akwati wanda duk abin da musa da iyalansa suka bari yana cikinsa, sannan suna neman tabarruki daga gare shi kuma yayin karo da makiya suna daukar shi domin neman cin nasara.[56]

Kasantuwar albarkar da muhimmancin wannan akwati ya zamana mala’iku suke daukarsa. Idan har ya kasance kiyaye wasu abubuwa na magabata (kamar wannan akwatin) wani abu ne marar kyau, to me ya sa Kur’ani mai girma yake ambaton wannan al’amari da harshe na yabo, kuma me ya sa mala’iku suke daukarsa, sannan me ya sa bayan dauke wannan akwati daga "Amalika" a cikin wannan aya ya zama wata alama ce da take nuna wanda zai jagoranci wannan runduna ta yaki?! Yara wadanda ba su balaga ba, su ne suke wasa da kayan da iyayensu suka bar musu, ta yadda cikin sauki suna iya batar da su. Amma magadan da suke da hankali kuma sukan amfani da matsayin wannan abin da iyayensu suka bar musu, suna rike wadannnan kaya ne iya karfinsu. Al’ummar musulmi ma sakamakon cigaban da suka samu bayan wafatin Manzo (S.A.W), su kiyaye duk wani abu da ya bari, wannan kuwa har da kwarar gashinsa sun kasance sun sanya ta wani wuri na musamman suka ajiye ta.

Matsayin Gidajen Annabawa A Cikin Kur’ani

Gidajen annabawa da manyan bayin Allah suna da wani matsayi na musamman, wannan kuwa a fili yake matsayin da suke da shi bai shafi wani abu na duniya ba ne, domin idan da haka ne, gidajensu ba su da wani bambanci da sauran gidajen mutane domin an gina su ne da yumbu da tubali kamar na kowa. Wadannan gidaje suna da wannan matsayi ne sakamakon mutane masu matsayi da suka zauna a cikinsu.

Kur’ani mai girma[57] yana siffanta hasken ubangiji da fitila mai haske ta yadda yake haske kamar tauraruwa. A ayar da take biye ma wannan aya kuwa ya nuna cewa wurin wannan haske yana gidajen wasu mutane masu girma wadanda suke ambaton Allah a ciki safiya da yamma.[58]

A cikin wannan aya jimlar da take cewa "Ana tasbihinsa safiya da yamma, tana nuna dalilin da ya sa aka daukaka wadannan gidajen wadanda aka ambata a cikin ayar da ta gabata. A ayar da take biye mata kuwa an siffanta masu yin ibada a cikin wadannan gidaje ne, inda yake cewa: "mutane ne wadanda kasuwanci ba ya shagaltar da su daga ambaton Allah da tsayar da salla, domin suna jin tsoron ranar da zukata da idanu suke jujjuyawa suna tsorata.[59]

Wannan aya tana bayani ne a kan girma da daukakar gidajen da ake zikirin Allah ake kuma tsarkake shi a cikinsu. A nan dole ne mu yi bayani a kan abubuwa guda biyu kamar haka:

1-Me ake nufi da gidaje a cikin wannan aya?

Masu tafsiri sun yi sabani a kan ma’anar wannan ayar ta yadda kowane ya dauki daya daga cikin ma’anonin kansa:

A-Ana nufin gidaje a cikin wannan aya da masallatai guda hudu

B-Ana nufin dukkan masallatai ne a cikin wannan aya

C-Ana nufin gidajen Manzo ne

D-Masallatai da gidajen Manzo

A cikinwadannan ma’anoni da aka ambata a kasa ma’ana ta uku ce kawai zata iya dai-dai kamar yadda zamu kawo dalilai da suke karfafa hakan.

1-Ta fuskar lugga kalmar Buyut jam’i ne na bait wato gidan kwana. Ibn manzur ya tafi a kan cewa bait yana nufin gidan mutum. Ragib kuwa yana cewa bait shi ne inda mutum yake fakewa da dare. Amma mawallafin "almunjid kuwa cewa ya yi, ma’anar bait tana nufin wurin zama wanda ya hada da hema da gidan da aka gina kasa da tubali.

Saboda haka fassara kalmar bait da masallaci wanda yake wurin ibada na kowa da kowa bai inganta ba, domin kuwa ba wurin da mutum yake fake wa ba ne da daddare. Saboda haka idan ma har ya inganta, amma abin zai zo ga kwakwalwar mutum shi ne gidan kwana, don haka idan har yana nufin masallaci ne ana bukatar abin zai nuna hakan. Ba tare da hakan ba, ba za a karbi wannan ma’ana ba.

Da wani kalamin ma Bait ya samu asali ne daga baituta wato mutum ya tsaya wani wuri har zuwa safe. Idan har ana mabata gidan mutum da bait saboda mutum yana kwana a cikin wannan gida ne har zuwa safe. Tare da kula da wannan ma’ana ta kalamar bait, fassara ta da ma’anar masallaci yana bukatar abin da yake nuna hakan, ba tare da wannan ba ba za a karbi wannan fassara ba.

2-Kur’ani duk lokacin da zai yi magana a kan wurin da al’umma suke bauta yana amfani ne da kalmar "masjid" ko "Masajid" ne. Sakamakon haka ne wannan kalma an yi amfani da ita sau 28 acikin Kur’ani mai girma. Amma duk lokacin da za a yi nagana a kan wurin da mutane suke kwana a kan yi amfani da kalmar "Maskan, Ma’awa" ne. Sannan an yi amfani da kalmar bait ta fuskar jam’i ko tilo. Saboda haka wannan kalma ta zo sau 66 a cikin Kur’ani da wannan manufa, sakamakon haka muna iya fahimata cewa a cikin Kur’ani kalmar "Masjid" da "bait" ba suna nufin ma’ana guda ba ne. saboda haka idan aka nemi fassara su da ma’ana guda zai zama da’awa ba tare da dalili ba.

Idan Kur’ani ya kira masallacin Ka’aba da "baitullahi"[60] ba don yana wurin bautar Allah ba ne, domin kuwa mun san cewa Ka’aba alkibla ce ta masu bautar Allah ba wurin da ake ibada ba. Saboda haka hada sunan Allah da wannan wurin kawai yana nuna girmamawa ne, kai ka ce wannan gida na Allah ta yadda za a girmama shi girmamawa ta musamman.

3-Akwai muhimmin bambanci tsakanin masallaci da gida, Bait ana nufin bangaye guda hudu da aka yi wa rufi, amma masjid kawai bangaye guda hudu ne, wato rufi ba sharadi ba ne kafin ya zama masallaci. Da yawan akan gina masallatai a wuraren da suke da zafi ba tare da rufi ba, wanda daya daga cikinsu shi ne masallacin ka’aba, alhalin kuwa gidan da mutum yake kwana yana bukatar rufi.

Wannan aya da zata zo a kasa tana bayar da sheda a kan bukatar gida daga rufi:

"Ba don hikimar Allah ta yi rigaye ba akan cewa komai zai kasance bai daya, da mun sanya gidajen wadanda suka kafirce wa Ubangiji mai rahama masu rufi da azurfa da tsanin da suke amfani zuwa sama".[61]

Wannan aya tana bayyana cewa "bait" sabanin "Masjid" yana da rufi, sannan ba don wata maslaha ba da Allah madaukaki ya bambanta gidajen kafirai da na muminai ta yadda zai sanya gidajen Kafirai rufinsu ya zama na azurfa, amma sai bai yi hakan ba.

4-Jalaluddin Suyudi ya ruwaito daga Anas bn Malik Yana cewa: Yayin wannan aya wadda take cewa "A cikin gidajen da Allah ya yi Umarni da a daukaka….". Sai ya karanta a cikin masallaci, sai wani daga cikin sahabban Manzo ya mike ya tambayi Manzo me ake nufi da wadannan gidaje?

Sai Manzo ya amsa masa da cewa: Ana nufin gidajen Annabawa, a wannan lokaci sai Abubakar ya mike ya ce: Ya nuna gidan Ali da Fatima (A.S) ya ce wadannan gidajen suna cikin wadanda Allah ya yi izini da daukaka su?. Sai Manzo (S.A.W). ya amsa masa da cewa: E, suna ma daga cikin mafi daukakarsu.[62]

Imam Bakir (A.S) yana cewa: Abin da ake nufi da gidaje a cikin wannan aya shi ne, gidajen Annabawa da gidan Ali (A.S)[63]

Bisa dogaro da wadannan dalilai muna iya fahimtar cewa abin da ake nufi da gidaje a cikin wannan aya ta cikin Suratun Nur shi ne gidajen annabawa da waliyyan Allah, sakamakon tasbihi da tsarkake Allah da ake yi a cikinsu yake da wani matsayi na musamman, kuma Allah ya yi izini da yin kokari wajen a daukaka su.

5-Sannan dalili wanda yake a fili a kan cewa abin da ake nufi da gidaje a cikin wannan aya su ne, ayoyi guda biyu da suka zo kamar haka: Allah madaukaki yana yi wa Annnabi Ibrahim da matarsa magana kamar haka:

A-"Rahmar Allah da albarkarsa ta tabbata a gare ku ya ku ma’abota gida[64];

B-Allah Kawai ya yi nufi ya tafiyar muku da kazanta yaku Ahlul Bait, ya kuma tsarkake ku tsarkakewa[65]; Kai ka ce wadannan gidaje su ne cibiyar hasken ubangiji.

Tare da kula da wadannan dalilai guda biyar da muka kawo muna iya cewa: Masati da daukakar wadannan gidaje sakamakon wadanda suke zaune a cikinsu ne, suna tasbihin ubangiji suna tsarkake shi. A hakikanin gaskiya wannan aya tana magana ne dangane da gidaje irin gidajen Annabi Ibrahim da Manzo (S.A.W). Wannan kuwa sakamakon tasbihi da tsarkake ubangiji da ake yi a cikinsu. Shi ne ya sanya Allah madaukaki ya daga martaba da darajarsu.

Mai yiwuwa a ce: Karkashin wannan aya ana cewa: "Yana tasbihinsa a cikinsu safiya da yamma": wato abin da ake nufi da "Buyut" Masallatai, domin kuwa musulmin farkon zuwan musulunci sun kasance suna halarta sallar jam’i baki dayansu. saboda haka tasbihi da tsarkake ubangiji ana yin sa ne a cikin masallaci.

Amma wannan fahimta ba daidai ba ce, domin kuwa ana aiwatar da sallar wajibi ne kawai a cikin masallatai, sannan mustahabbi ne a gabatar da sauran sallolin mustahabbi a cikin gidaje. Sannan ya kamata ma mutum ya kasa ibadarsa zuwa gida biyu, wato wani bangare na farilla ya aiwatar da su a cikin masallaci, sannan bangaren nafiloli ya gabatar da su a cikin gida.

Mai yiwuwa wasu suga wannan bai inganta ba, amma hakikanin al’amarin haka yake domin kuwa ruwayoyi da dama sun karfafa hakan. Muslim a cikin sahih dinsa, ya kawo babi mai zaman kansa wanda yake nuna mustahabbancin sallar nafila a cikin gida. A kan haka ya ruwaito ruwayoyi da dama, amma a nan kawai zamu kawo wasu a matsayin misali:

Manzo mai tsira da aminci yana cewa: "Fiyayyar sallar mutum a cikin gidansa, sai dai sallolin wajibi"[66].

Wannan ruwaya tana nuna mana cewa Manzo (S.A.W) da sauran sahabbansa suna yin sallolinsu na nafila a cikin gidajensu, sakamakon haka ne gidajen annabawa da na salihan bayi suka zama wurin zikirin Allah da tsarkake shi. Sannan kuma dalilin wannan ne Allah ya ba da izini a kan daukaka su.

A yanzu dole ne mu ga me ake nufi daga matsayin wadannan gidaje! me ake nufi da daukaka wadannan gidaje?

A baya mun yi bayanin cewa, kafa hujja da wannan aya yana bayyanar da abubuwa guda biyu ne. Abu na farko kuwa shi ne, bayyanar da ma’anar "buyut" wanda muka yi cikakken bayaninsa a baya, yanzu lokaci ya yi da zamu yi bayani a kan abu na biyu wanda shi ne daukaka wadannan gidaje da Allah yake horo da shi.

Hakika kalmar "Rafa’a" cikin Kur’ani tana zuwa ne da ma’anar daga gini kamar yadda ta zo a cikin wannan ayar: "Shin halittar su ita ce tafi wahala ko kuwa sama wadda ya gina ta?! Sannan ya daga rufinta ya kuma daidaita ta?![67]

Amma kalmar "rafa’a" a cikin wannan aya ba yana nufi yin gini ba, domin kuwa an dauka cewa akwai gida ne, Kur’ani yana magana a kan siffofin wannan gida ne. saboda haka abin da ake nufi da wannan kalma a cikin wannan aya shi ne daga matsayinsu da girmama su, mafi yawan masu tafisiri sun dauki wannan ma’ana duk da cewa wasu daga ciki sun tafi a kan ma’anar da muka ambata a baya. [68]

A bayyane zamu iya cewa: Wuraren da Allah yake ambatar "Buyut" yana nufin gidajen da bayin Allah suke kwana suna yin tasbihin ubangiji kuma suna tsarkake shi. Saboda haka daukaka wadannan gidaje ba ya nufin daga gininsu ko rufinsu ba ne, abin da ake nufi shi ne daga matsayi da martabarsu. Daya daga cikin wannan girmamawa da daga matsayinsu kuwa shi ne ya zamana an tsarkake su daga dukkan wata kazanta, sannan duk inda suka dan lalace a gyara su.

Dukkan wannan aiki za a yi shi ne saboda girmama wadanda suka kasance a cikin wadannan gidaje suna tasbihin ubangiji suna salloli kuma ba su kin fitar da zakka, domin girmama wadannan mutane ne Allah ya yi horo da a girmama wadannan gidaje, sannan a kare su daga rushewa.

Kowa ya san cewa an rufe Manzo (S.A.W) a cikin gidansa, wato a wurin da ya kasance yana ambaton Allah da yabonsa. Saboda haka tare da bin hukuncin wannan aya gidan Manzo ya cancanci girmamawa da daukaka matsayinsa, sannan a kiyaye shi daga kowane irin rushewa da lalacewa. Sannan kuma a kaurace wa sanya masa duk wani nau’i na kazanta, kai da yawa daga bangarorin Madina kaburburan manyan bayin Allah ne. Kamar yadda ya zo a cikin ingantattun ruwayoyi sayyida Fadima (A.S) ita an rufe ta ne a cikin gidanta[69]

Haka nan Imam Hadi da Imam Askari (A.S) an rufe su a gidajensu wadanda suka kasance suna ibada da zikirin ubangiji a cikinsu. saboda haka wadannan gidaje bisa la’akari da wannan aya sun cancanci a daukaka su, sannan dole ne a kauce wa rusa su domin ya saba wa wannan aya. A unguwar Bani Hashim a garin Madina shekaru kadan da suka gabata gidan Imam Hasan da Husain (A.S) da makarantar Imam Sadik (A.S) sun kasance a wadannan wurare, Marubucin wannan littafi shi kansa ya ziyarci wadannan wurare, amma abin bakin ciki tare da fakewa da fadada masallacin Manzo duk an rusa wadannan wurare masu dimbin tarihi da albarka. Duk da cewa ana iya yin wannan aiki na fadada masallacin Manzo (S.A.W) ba tare da rusa wadannan wurare ba.

Soyayyar Manzo (S.A.W) Da Iyalansa

Ayoyi da hadisai da dama sun zo domin bayani a kan soyayya ga Manzo da ‘yan gidansa (A.S). Kur’ani ya nuna mana cewa imanin abin ceta shi ne ya kasance yana tare da wanda yake son Manzo da jihadi a tafarkin Allah fiye da komai a cikin zuciyarsa: "Ka ce idan iyayenku da ‘ya’yanku da matanku da ‘yan’uwanku da dukiyoyinku wadda kuka tara, da kasuwanci da kuke tsoran ku fadi a cikinsa, da gidajenku da kuke kaunarsu, idan sun kasance sun fi soyuwa a gareku daga Allah da manzonsa da jihadi a tafarkin Allah sai ku saurara har al’amarin Allah ya zo, Allah ba ya shiryar da mutane fasikai".[70]

Ayar sama tana magana ne a kan abubuwa guda uku wadanda mafi yawa soyayyar mutum takan ta’allaka da su, wato Iyalai da dukiya da gidaje da saye da sayarwa. Amma mumini na hakika shi ne wanda Allah da mazonsa da jihadi a tafarkin Allah ya fi soyuwa a gare shi fiye da wadancan abubuwa da aka ambata. Amma a wata aya ana bayani ne a kan soyayyar iyalan gidan Manzo ga abin da take cewa: "Ka ce ban nemi wani abu a kan sakon manzancin da na zo da shi ba a matsayin lada sai soyayya ga iyalan gidana". [71]

Sannan Manzo yana bayyana wasu abubuwa guda uku wadanda suke nuna dandana zakin imanin mutum, daya daga cikinsu shi ne soyayya ga Allah da shi manzon: Abubuwa guda uku ne duk wanda yake da su to ya dandana zakin imani, daya daga cikinsu kuwa shi ne ya kasance a wajan mutum son Allah da manzonsa ya fi komai a wajensa… Ruwayoyi da suka zo dangane da son Manzo da iyalansa sun wuce gaban mu kawo su a cikin wannan littafi, saboda haka a nan zamu takaia da wasu ruwayoyi a matsayin misali dangane da wannan al’amari, muhimmin abu a nan shi ne mu san ta yaya wannan soyayya zata tabbata, domin mutum ya isa zuwa ga wannan hadafi akwai hanyoyi guda biyu:

1-Mutum ta hanyar magana da ayyukansa ya yi koyi da koyarwar Allah da manzonsa, ta yadda zai kasance a rayuwa ya yi kokari ya ga bai kauce wa koyarwarsu ba, domin kuwa idan mutum ya zamana yana tsananin soyayya ga wani ba zai taba saba masa ba. Saboda haka ne ake cewa "soyayya ita ce biyayya". Wato sonka da abu yana lizimta maka da yi masa biyayya.

Sannan Imam Sadik (A.S) a wasu baituka yana bayyana bambanci tsakanin soyayya ta gaskiya da nuna soyayya da ba ta hakika ba, Inda yake bayani akan cewa: Kana sabon Allah alhali kana nuna soyayya gare shi, Wannan ba zai taba yiwuwa ba, Domin da sonka ya kasance a gaskinya ne, to da ka yi biyayya a gare shi, Domin kuwa masoyi yana bin abin da abin so yake so. [72]

2-Bayyana soyayya ta hanyoyi daban-daban kamar haka:

A- Nuna farin cikin yayin da masoyi yake cikin farin ciki, da nuna bakin ciki yayin da masoyi yake cikin bakin ciki;

B-Gabatar da buki na farin cikin a lokacin haiwuwar Manzo ko lokacin tayar da shi a matsayin ma’aiki;

C-Yada maganganunsa da abin da ya rubuta;

D-Kiyaye kayan tarihin da suka shafe shi;

D-Girmama Kabarinsa da yin gini domin kiyaye shi daga lalacewa;

Aikata wadannan abubuwa da makamantansu wadanda suke sun halasta a musulunci, yin su ga Manzo da iyalan gidansa ya nuna kauna ne a gare su.

Tirmizi yana ruwaitowa a cikin sunan dinsa: "Manzo (S.A.W) ya kama hannun Hasan da Husain sai ya ce: Duk wanda yake so na ya kuma so wadannan yara guda biyu da babansu da mamansu, to zai kasance a matsayina a ranar kiyama[73].

Kowannenmu ya san da cewa babban jikan Manzo yana rufe ne a "bakiyya" Sannan mai biye masa yana rufe a Karbala, Sannan wadannan wurare kodayaushe suna ganin al’ummar musulmi masu ziyara, Saboda haka duk wani gini kowane abu wanda za a yi domin kiyaye wadannan wurare, nau’i ne na nuna soyayya ga wadannan jikoki na Manzo kuma bin umarnin Manzo ne a kan soyayya gare su, kamar yadda muka yi bayani a ruwayar da ta gabata.

A yau al’ummu da dama suna kokari wajen tunawa da manyan tarihinsu (kamar sojoji da ‘yan siyasa da wadanda suka yi wasu ayyuka na gyara) ta hanyoyi daban-daban, sakamakon haka ne suke halarta jana’izarsu yadda ya kamata. Sannan su rufe a wani wuri na musamman a karkashin gini mai kawatarwa, ta yadda wadanda zasu zo a nan gaba kamar yadda na yanzu suke kulawa ta musamman a kan su, suma su yi kulawa da girmamamawa ta musamman a kan wadannan manyan mutane. Don haka mu ma musulmi dole mu yi kokari don yin gine-gine da zasu kare kabuburan manyan mutanemmu.

Kaburburan Manzanni Da Tarihin Magabata Ma’abota Tauhidi

Tafiye-tafiye domin bude ido zuwa wuraren da aka rufe annabawa da ‘ya’yansu wani abu ne wanda yake ba sabo ba a cikin al’umma. Wannan kuwa yana nuna cewa mabiya annabawa suna nuna kulawa ta musamman dangane da wadannan wurare, tare da gina gine-gine a kan kaburburansu suna kare su daga rushewa. A yanzu a kasashen Iraki, Palasdin, Jordan, Misra da Iran, akwai kaburburan annabawa (A.S) wadannan aka yi gine-gine masu kawatarwa ta yadda kodayaushe mutane suna zuwa wurin domin ziyara. Sannan dakarun musulunci da su kai hare-hare don bude garuruwan Sham, sam ba ruwansu da wadannan kabuburan annabawa, ba ma haka ba kawai sun bar mutanen da suke hidima a wadannan wurare don su cigaba da aikinsu a wajen kamar yadda suke a da. Sannan ba su nuna rashin amincewarsu a kan hakan ba ko kankani. Idan da yin gine-gine a kan kaburburan annabawa wani aiki ne da ya haramta kuma ya shafi shirka, da wadannan dakaru da suka zo da umarnin khalifa domin bude wadannan garuruwa duka sun rusa wadannan gine-gine, amma koda wani dan karamin canji ba su yi ba ga wadannan kaburbura an cigaba da tafiyar da su kamar yadda suke kafin wannan lokaci. Sannan har zuwa yanzu wadannan gine-gine suna nan kamar yadda suke ta suke jawo hankalin al’ummar musulmi da ma duk mai bin addinan da Allah ya aiko da su. Sannan a farkon zuwan musulunci ma musulmai sun rufe annabinsu a cikin dakinsa, kuma babu wani daga cikin wadannan musulmai da yake tunani cewa yin gini a kan kabarin Manzo haramun ne.

Sannan binciken littattafan tarihi da labaran tafiye-tafiyen masana addinin muslunci yana bayar da shedar cewa akwai daruruwan kaburbura a kasar da wahayi ya sauka da sauran kasashen musulmi:

1-Mas’udi wanda ya rasu 345Bh. wanda yake shahararren masanin tarihi ne, ga abin da yake cewa dangane da kaburburan imamai (A.S) da suke a "bakiyya" yana cewa:

"A bisa kaburburansu a akwai dutse wanda aka rubuta: Da sunan Allah mai rahma mai jin kai, godiya ta tabbata ga Allah wanda yake kashe al’umma yake kuma raya matattu. wannan shi ne kabarin Fadima "yar manzon Allah (S.A.W) wadda take ita ce shugabar matan duniya. Da kabarin Hasan bn Ali bn Abi Dalib da kabarin Ali bn Husain bn Ali bn Abi Dalib da kabarin Muhammad Bn Ali Bn Husain bn Ali Bn Abi Dalib da Kabarin Ja’farus Sadik Bn Muhammad". [74]

Mas’udi ya kasance daga cikin masana tarihi na karni hudu Bayan hjira. ’Yan salafiya wadanda suke da kankamo sun tafi a kan cewa, wannan karni da karnonin da suke kafinsu su ne fiyayyun karnonin tarihin musulunci, sannan ayyukan da suka yadu a tsakanin musulmi a wannan zamani suna nuna kasantuwar abubuwan da shari’a ta yarda da su. Amma abin bakin ciki wannan babban dutse wanda Mas’udi yake fada wanda aka yi wannan rubutu a kansa, sakamakon rushewar da wahabiyawa suka yi wa "bakiyya" yanzu babu shi a samuwa. Saboda haka yanzu wadannan kaburbura ba a iya bambance su.

Ibn jubair[75] (540-614) shahararren mai yawo bude ido ya ziyarci kaburburan annabawa da bayin Allah a kasashen Misra, Makka, Madina, Iraki da Sham, yayin tafiye-tafiyensa kuma ya yi bayani a kan kowane daya daga cikinsu a cikin littafinsa na tafiye-tafiye, ta yadda dukkammu zamu iya samun wannan a cikin wannan littafin nasa. Ta hanyar karanta wannan littafin musulmi suna samun masaniya a kan tarihin gina hasumiyoyi da gine-ginen kaburburan annabawa da waliyyan Allah. Dangane da abin da ya zo a cikin wannan littafin tafiye-tafiye nasa shi ne: Tarihin gina manya-manyan gine-gine a kan kaburburan Imamai da waliyyai da shahidai a tafarkin Allah, wanda yake komawa zuwa ga zamanin sahabbai da tabi’ai. Wanda yake nuna yadda a wancan zamanin da musulmai suke nuna kauna da kulawarsu dangane da shugabanni da manyan addini, ta yadda suka tashi domin gina wurare masu kawatarwa domin girmamawa gare su. Sannan babu wani daga cikin sahabbai wanda ya nuna cewa wannan aiki yana komawa ne zuwa ga shirka ko kuma ya saba wa tauhidi da kadaita ubangiji. Kamar yadda Ibn Jubair ya fara tafiyarsa daga gaban duniyar musulunci (Andulus) zuwa yammacinta ta yadda kasar Misra ta kasance wuri mafi kusa gare shi, Sai ya fara da wuraren tarihin da suke a Misra musamman Alkahira. Zamu kawo wasu daga cikin abin da ya rubuta daga cikin wadannan gine-gine na musulunci a wannan kasa:

Gini Mai Girma Na Kan Imam Husain (A.S) A Alkahira

Wasu sun tafi a kan cewa an rufe kan Imam Husain (A.S) a garin Alkahira, saboda haka suka gina wani wuri da sunan "Ra’asul Husain" inda mutane suke zuwa ziyara daga cikin gida da waje. Masu sabon aure a wannan gari sukan je Masallacin Husain (A.S) wanda yake a wannan wuri sukan yi dawafi.. [76]

Ibn Jubair yana cewa: Daya daga cikin wurare masu tsarki a Alkahira shi ne Wurin da aka rufe kan Husain, an kawata wannan wuri da azurfa, wannan gini yana da girma da daukaka ta yadda harshe ba zai iya siffanta shi ba. A kan wannan gini akwai wani dutse na alfarma kai kace madubin Indiya ne, ta yadda yake haske yana dauko hotunan abubuwan da suke a gabansa. Yace: Da idanuna na ga masu ziyarar Husaini (A.S) yadda suke kuka suna sumbatar yadin da aka dora a kan abin da aka rufe kabarinsa da shi suna neman tabarraki suna addu’a, ta yadda kwallarsu kamar ta rufe wannan kabari.

Ibn Jubair ya ambaci wani wuri da ake kira "Karafa" inda yake cewa yana daga cikin wurare masu ban al’ajabi kamar yadda ya bayyana akwai kaburburan annabawa da iyalan Manzo da sahabbansa da tabi’ai da sauran kaburburan manyan malamai da aka rufe a wannan wuri. Dan Annabi Salih (Raubil) dan Annabi Yakub (Ishak) da matar Fir’auna dukkansu an rufe su ne a wannan wuri. Haka nan daga cikin iyalan Manzo akwai dan Imam Ja’afar mai suna kasim da dansa Abdullah bn Kasim da dansa Yahya bn Kasim, sannan da kabarin Ali bn Kasim bn Abdullah bn Kasim da dan’uwansa Isa bn Abdullah.

Ibn Jubair ya ambaci da yawa daga cikin ‘ya’yan Ali (A.S) wadanda aka rufe su a can. Haka nan akwai kaburburan Sahabbai tabi’ai ba shugabanni kamar Imam Shafi’i ta yadda yake magana a kan girma da matsayin haraminsa, kamar yadda yake cewa: Salahuddin Al’ayubi shi yake biyan kudin da ake bukata domin gabatar da bukukuwa a wannan harami na Imam Shafi’i.