Tattaunawa Ta Sha Daya

MARUBUCI: Hafiz Muhammad Sa'id hfazah@yahoo.com
TATTAUNAWA TA SHA D'AYA Amma da kake cewa: ((idan kayi baya kadan a shafi na8 wannan malami na addinin Shi'a yace `Allah zai shigar da wanda ya yiwa Aliyu biyayyah Aljanna koda kuwa ya sabawa Allah wanda kuwa ya sabawa Aliyu za'a shigar da shi wuta ko da ya yiwa Allah biyayyah)).
Sai na ce maka: Wadannan maganganu naka suna dada mini haske kan karancin saninka, ka sani hadisai sun inganta daga Sunna da Shi'a cewa; da mutum zai bauta wa Allah shekara saba'in a gefen ka'aba sannan sai ya zo wa Allah yana kin Ali (a.s) da wuta zai tafi. Wannan yana akkasuwa da cewa; idan da ya bi Ali (a.s) babu ma'anar ya saba wa Allah ke nan, ba ana nufin idan ya bi Ali (a.s) amma kuma ya saba wa Allah ba!. Ina ganin kana bukatar koma wa aji idan dai ka taba zuwa, domin irin wannan rashin ganewa naka ya yawaita Adamu.
Ka sani duk wanda ya mutu bai san imaminsa ba kuma bai yi bai'a (imani) da shi ba, to ya yi mutuwar jahiliyya.
Tambaya gaya mana imaminka a wannan zamani!?
Sannan akwai dalilai sai ka koma wa littattafai masu yawa: kamar dalilan da suka kawo cewa da bawa zai bauta wa Allah shekaru dubu tsakanin Rukun da Makam sannan sai ya hadu da Allah yana mai kin Ali (a.s) da Allah ya kifar da shi a cikin wuta ranar kiyama a kan fuskarsa. Manaki na Khawarizimi: 43, 44. A'alamuddin fi sifatil muminin, Dailami: shafi; 400. Ikabul a'amal: 1/242.
Akwai littattafai masu yawa kan wannan lamari sai dai mun takaita a nan saboda gudun tsawaitawa.
Amma da ka ce: ((shi kuwa bakin kafirinnan Ibn Babawaishi cewa yayi a littafinsa Ilalul Shara'iu shafi na 205 "Aliyu dan Abi Dalib zai riga Annabi Muhd SAW shiga Aljannah tabbas)).
Sai na ce maka: Nan ma ka ci amanar nakaltowa ka yi kage ga mabiya Ahlul Baiti (a.s), domin babu wannan managa a wannan shafin.
Sannan da ka ce: ((hakan Hassan dan Abdulwahab ya ce a littafinsa Uyunul Mu'ujuzatu "Hakika Aliyu dan abi Dalibi yana raya matattu kuma yana yaye kuncin masu kunci)).
Sai na ce maka: (Ka canja sunan Husain zuwa Hassan domin ka batar da kama ga mai binciken littafin wannan ma cin amanar ilimi ce)
Irinka dole ne ya yi musu karamomin kofar ilimomin Annabi (a.s) wanda aka ba shi ilimin kowane abu, tayar da matacce karamin abu ne gun Imam Ali (a.s) akwai abubuwan da suka fi tayar da mamaci mamaki amma ire-irenka da ba su san wilaya da imama da matsayinta a wurin Allah ba dole su musa. Amma da an ruwaito fadin Umar "ya sariyatal jabala" a nan gaskiya ne tun da shi ba ya cikin Ahlul Baiti (a.s)! Amma falalar aali Muhammad (a.s) kowace iri karama da babba kun yi musun ta.
Fadinka kuwa kana cewa: ((Shi kuma Muhd Assaudi a littafinsa Asrarul Fadimiyyah shafi na 98 yace "da badan Aliyu ba da ba'a halicci Annabi Muhd ba kuma da badan Fatima ba da du su biyun ba'a haliccesu ba" shima mawallafin littafin Fatimatuz – Zahra Minal Mahadi Ilal Lahadi bayan ya cika littafin da tatsuniya sai ya ce a shafi na 38 "Tabbas Fatima tana Magana da mahaifiyarta tun tana cikin mahaifa…)).
A nan ma sai na ce: (Ka canja sunan Mas'udi zuwa sa'udi domin ka batar da kama ga mai binciken littafin wannan ma cin amanar ilimi ce)
Ya kai Adam ire-irenka ba zasu iya fahimtar sirrin maganganun Ahlul Baiti (a.s) ba, domin akwai shamaki da Allah ya sanya maka da ba zaka iya fahimta ba. Misalinka kamar misalin "waja'alna fikulubihim akinnatan an yafkahuhu" ne.
Tambaya: me zaka ce game da abin da ya zo a littafin sunan Ibn Majah da sauran sunan cewa ya inganta kuma haka ma gun Shi'a ya inganta cewa; manzon Allah (s.a.w) ya ce: Husain daga gareni yake ni ma daga Husain nake". ÍÓíä ãäì æ ÃäÇ ãä ÍÓíä.
Yaya kake ganin wannan, shin kana ganin manzon Allah yana nufin shi ma dan Husain ne?
Ka koma ka bincika, ina ganin bai kamata ba in tsaya bata lokaci wurin yin bayanin da ba zaka iya fahimtarsa ba.
Don haka waccen maganar ma ire-irenka ba sa iya gane ta, saboda "am ala kulubin akfaluha".
Da ka ce: ((Zan tsaya anan sai a a rubutu na na uku.zai zo kuma bayan naga raddin da za'a yi mini ina kira ga kananan yan shi'ar dandalinnnan cewa ni Adamun garin baraya su sani, tsohon dan Shi'a ne sama da shekara 20 da suka wuce du mai musu ko yana neman labari na ya tambayi Mal. Adamu Tsoho Jos ko mal Abubakar Maina ko mal Muttari Sahabi zasu gaya masa waye Adamu. Nasan sirrin Shi'a a fili da boye an kulle kofa dani an tura mu mun kai hari kuma du agendar Shi'ar Najeriya tana a tafin hannuna niba sa'an yaro bane na zauna gaban Zakzaky nayi hidima ya sanni tun bai san hukuncin kana wa ak'watuha ba na sani, to du wanda zai yi mini raddi yasan wa yake yiwa raddi.
Adamu m Adamu, Garin Barayar jahar gombe, A yanzu ina zaune a Kano ne domin kamala karatuna)).
Sai na ce maka: Ire-irenka sun dade suna karyar su tsofaffin 'yan Shi'a ne domin su kawo rudu, kuma suna kiran kansu manyan 'yan Shi'a wasu kuwa kanana alhalin a Shi'a babu manya da kanana, wannan yana nuna cewa kai makaryaci ne ba ka ma san Shi'a'nci ba, kana kawo wannan ne domin ka sanya rudu tsakanin Sunna da Shi'a, kuma kai ba Shi'a ba kuma ba Sunna ba.
Sannan dan Shi'a ba ya mamakin falalar Imam Ali (a.s), wannan ya nuna karyar cewa ba ka taba zama dan Shi'a ba.
Saninka da bayin Allah da suke Shi'a ba ya nufin ka yi alfahari, domin ko Annabi don ya sanka ko ka san shi ba abin alfahari ba ne matukar ba ka yi aiki mai imani nagari ba, kamar yadda ayar "yamunnuna…" ta nuna.
Sannan zama da muminai matukar ba ka yi aiki na gari ba shi ma ba abin alfahari ba ne, domin wanda ya zauna hatta da Annabi (s.a.w) amma bai kyautata imani ba duk wuta za shi.
Sannan ka yi karyar sanin sirrin Shi'a alhalin ba ka ma san mene ne Shi'anci ba.
Ka yi karyar sanin ajandar Shi'a, to gaya mana ajendar su a ranar jumma'a mai zuwa, tun da ka yi da'awar sani. Wannan yana nuna bakin jahilcinka, domin ba wanda ya san abin da zai faru gobe. Sannan idan kana nufin ajenda wani tsari da suka shirya to ka sani Shi'a sun fi kowa kishin kasashensu da al'ummarsu, kuma tarihi ya nuna mana yadda suka kare al'ummunsu da dukkan abin da suka mallaka.
Fadinka kai ba sa'ar yaro ba ne, wannan ma yana nufin jahilcinka, sannan ka sani addini ba hauka da karfin tuwo ba ne, addini da ilimi da hankali ne, don haka idan yaro ya fi ka ilimi sai ka rusuna masa.
Koda yake ka yi gadon abin da aka gaya wa Imam Ali (a.s) "Ha'ula'i mash'yakhatu kaumik…"! don haka babu mamaki idan irin wannan kalma ta fito daga bakinka.
Sannan da ka kira malam zakzaki ((tun bai san hukuncin kana wa ak'watuha ba)) wannan ma yabo ne ka yi masa, domin ka nuna da can bai sani ba, amma yanzu ke nan ya sani, don haka wannan yabo ne gareshi da yake nuna cewa yana kara samun ilimi bai tsaya yadda yake dacan ba ke nan.
Amma wanda zai yi maka raddi wallahi ya san wanda yake yi wa raddi, domin yana yi wa wani tantirin jahili raddi ne!!!
Ina ganin ka nuna ba ka neman gaskiya yayin da aka ba ka amsa a bayanin da ka aiko na farko, wanda aka ba ka amsoshi gamsassu:
Ka nuna jahilcinka da siyasar duniya tun farko yayin da ka jahilci gabas ta tsakiya da dukkan abin da yake faruwa tun daga Iran, Iraki, da Labanon, da yadda a yau Isra'ila da Amurka suka kasa, sai suka sanya ire-irenku ku yi ta hanyar alkalumanku, kasashe kuwa irin su Misira sai aka sanya su neman hujumi kan Hizbullah, aka raba ayyuka kowa aka ba shi nasa, don haka mun gane irinku hannayensu.
Sannan nasiha ka daina magana da yawun sunnanci domin sai wasu su dauka sauran musulmi ma'abota mazhabobi kake nufi, ka fadi sunan mazhabinka da tafarkinka da yake kafirta sauran musulmi, idan kuwa babu shi to mun san inda zamu ajiye ka!!!

Hafiz Muhammad Sa'id
hfazah@yahoo.com
www.hikima.org
May, 1, 2009