Nasi Zuwa Dhuha

Hafiz Muhammad Sa'id   hfazah@yahoo.com

 

SURAR NASI ZUWA DHUHA



سورة الفاتحة

Surar Bud'ewa

Ayoyinta 7 ne, Ana kiranta Uwar Littafi domin ta tara ilmin da yake a cikin Kur'ani a dunK'ule. Basmala a cikinta take ga K'ira'ar Asim, ruwayar Hafs, amma banda a K'ira'ar Warsh.

بِِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ

1. Da Sunan Allah Mai Rahama Mai Jin k'ai.

الْحَمْدُ لِلّهِ رَبِّ الْعَالَمِينَ

2. Godiya ta tabbata ga Allah ubangijin talikai.

اَلرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ

3. Mai rahama mai jin k'ai.

مَالِكِ يَوْمِ الدِّينِ

4. Mai mallakar ranar sakamako.

إيَّاكَ نَعْبُدُ وإِيَّاكَ نَسْتَعِينُ

5. Kai kad'ai muke bautawa kuma kai kad'ai ne muke neman taimako.

اِهْدِنَا الصِّرَاطَ المُسْتَقِيمَ
6. Ka shiryar da mu tafarki madaidaici.

صِرَاطَ الَّذِينَ أَنعَمْتَ عَلَيهِمْ غَيرِ المَغضُوبِ عَلَيهِمْ وَلاَ الضَّالِّينَ

7. Tafarkin wad'anda ka yi wa ni'ima, ba wad'anda aka yi fushi da su ba, kuma ba b'atattu ba.

Ubangijin halittu ya tara ilmin Tafiyar da lamurran bayi da halitta su, kamar rayarwa, da matarwa, da ciyarwa, da shayarwa, da tufatarwa, Mai rahama Ya tara dukan rahamar duniya da dukkan ni'imomin samarwa gaba d'aya. Mai jin K'ai ya tara ni'imar duniya mai dogewa zuwa Lahira kamar ni'imar imani. Mai mallakar ranar sakamako, ya had'a dukan abin da ya shafi makoma. Kai muke bauta wa kuma Kai muke neman taimako, ya tara tauhidin bauta da ibada. Hanya madaidaiciya, ta had'a Littafin Allah da Ahlul Baiti (a.s) a matsayin wasiyyar Ma'aikin Allah. Wad'anda aka yi wa ni'ima, su ne Alayen Ibrahim da Alayen Muhammad (a.s). Wad'anda aka yi fushi da su, da kuma B'atattu, sun tara dukkan mutanen da suka kauce wa tafarki madaidaici.



سورة الناس

Surar Mutane

بسم الله الرحمن الرحيم

Da Sunan Allah Mai Rahama Mai Jin k'ai

قُلْ أَعُوذُ بِرَبِّ النَّاسِ (1)

1. Ka ce ina neman tsari ga ubangijin mutane.

مَلِكِ النَّاسِ (2)

2. Mamallakin mutane.

إِلَهِ النَّاسِ (3)

3. Abin bautar mutane.

مِن شَرِّ الْوَسْوَاسِ الْخَنَّاسِ (4)

4. Daga sharrin mai waswasi mai b'oyewa.

الَّذِي يُوَسْوِسُ فِي صُدُورِ النَّاسِ (5)

5. Wanda yake sanya waswasi a cikin zukatan mutane.

مِنَ الْجِنَّةِ وَ النَّاسِ (6)

6. Daga aljanu da mutane.



سورة الفلق

Surar Asuba

بسم الله الرحمن الرحيم

Da Sunan Allah Mai Rahama Mai Jin k'ai

قُلْ أَعُوذُ بِرَبِّ الْفَلَقِ (1)

1. Ka ce ina neman tsari ga ubangijin safiya.

مِن شَرِّ مَا خَلَقَ (2)

2. Daga sharrin abin da ya halitta.

وَمِن شَرِّ غَاسِقٍ إِذَا وَقَبَ (3)

3. Daga sharirn dare idan ya yi duhu.

وَمِن شَرِّ النَّفَّاثَاتِ فِي الْعُقَدِ (4)
4. Daga sharrin mata masu tofi a cikin k'ulle-k'ulle.

وَمِن شَرِّ حَاسِدٍ إِذَا حَسَدَ (5)

5. Daga sharrin mahassadi yayin da ya yi hassada.






سورة الإخلاص

Surar Tsarkakewa

بسم الله الرحمن الرحيم

Da Sunan Allah Mai Rahama Mai Jin k'ai

قُلْ هُوَ اللَّهُ أَحَدٌ (1)

1. Ka ce: Shi ne Allah makad'aici.

اللَّهُ الصَّمَدُ (2)

2. Allah Sid'if yake.

لَمْ يَلِدْ وَلَمْ يُولَدْ (3)

3. Bai haifa ba, kuma ba a haife shi ba.

وَلَمْ يَكُن لَّهُ كُفُواً أَحَدٌ (4)

4. Kuma babu wani da ya kasance tamka a gareshi.




سورة اللهب

Surar Harshen wuta

بسم الله الرحمن الرحيم

Da Sunan Allah Mai Rahama Mai Jin k'ai

تَبَّتْ يَدَا أَبِي لَهَبٍ وَتَبَّ (1)

1. Hannaye biyu na AbuLahab sun halaka, kuma ya halaka.

مَا أَغْنَى عَنْهُ مَالُهُ وَمَا كَسَبَ (2)

2. Dukiyarsa da abin da ya tara, ba su tsare masa komai ba.

سَيَصْلَى نَاراً ذَاتَ لَهَبٍ (3)

3. Zai shiga wuta mai huruwa.

وَامْرَأَتُهُ حَمَّالَةَ الْحَطَبِ (4)

4. Tare da matarsa mai d'aukar itace.

فِي جِيدِهَا حَبْلٌ مِّن مَّسَدٍ (5)
5. A cikin wuyanta akwai igiyar kaba.






سورة النصر

Surar Cin Nasara

بسم الله الرحمن الرحيم

Da Sunan Allah Mai Rahama Mai Jin K'ai

إِذَا جَاء نَصْرُ اللَّهِ وَالْفَتْحُ (1)

1. Idan taimakon Allah da cin nasara suka zo.

وَرَأَيْتَ النَّاسَ يَدْخُلُونَ فِي دِينِ اللَّهِ أَفْوَاجاً (2)

2. Kuma ka ga mutane suna shiga addinin Allah jama'a-jama'a.

فَسَبِّحْ بِحَمْدِ رَبِّكَ وَاسْتَغْفِرْهُ إِنَّهُ كَانَ تَوَّاباً (3)

3. To, ka yi tasbihi da gode wa ubangijinka, kuma ka neme shi gafararsa, Lalle shi ya kasance mai yawan karb'ar tuba ne.



سورة الكافرون

Surar Kafirai

بسم الله الرحمن الرحيم

Da Sunan Allah Mai Rahama Mai Jin K'ai

قُلْ يَا أَيُّهَا الْكَافِرُونَ (1)

1. Ka ce; Ya ku kafirai.

لَا أَعْبُدُ مَا تَعْبُدُونَ (2)

2. Ba zan bauta wa abin da kuke bauta wa ba.

وَلَا أَنتُمْ عَابِدُونَ مَا أَعْبُدُ (3)

3. Kuma ba zaku zama masu bauta ga abin da nake bauta wa ba.

وَلَا أَنَا عَابِدٌ مَّا عَبَدتُّمْ (4)

4. Kuma ni ba zan zama mai bauta wa abin da kuke bauta wa ba.

وَلَا أَنتُمْ عَابِدُونَ مَا أَعْبُدُ (5)

5. Kuma ku ba zaku zama masu bauta wa abin da nake bauta wa ba.

لَكُمْ دِينُكُمْ وَلِيَ دِينِ (6)

6. Addininku na gareku, kuma addinina yana gareni.




سورة الكوثر

Surar Alheri Mai Yawa

بسم الله الرحمن الرحيم

Da Sunan Allah Mai Rahama Mai Jin K'ai

إِنَّا أَعْطَيْنَاكَ الْكَوْثَرَ (1)

1. Lalle ne mu, mun yi maka alheri mai yawa.

فَصَلِّ لِرَبِّكَ وَانْحَرْ (2)

2. Saboda haka ka yi salla domin ubangijinka, kuma ka yi suka (soke taguwa/rak'umi).

إِنَّ شَانِئَكَ هُوَ الْأَبْتَرُ (3)

3. Hak'ik'a mai aibata ka shi ne mai yankakken baya (maras albarka).



سورة الماعون

Surar taimako

بسم الله الرحمن الرحيم

Da Sunan Allah Mai Rahama Mai Jin K'ai

أَرَأَيْتَ الَّذِي يُكَذِّبُ بِالدِّينِ (1)

1. Shin ka ga wanda yake k'aryatawa game da sakamako?

فَذَلِكَ الَّذِي يَدُعُّ الْيَتِيمَ (2)

2. To wannan shi ne yake tunkud'e maraya.

وَلَا يَحُضُّ عَلَى طَعَامِ الْمِسْكِينِ (3)

3. Kuma ba ya kwad'aitarwa bisa ciyarwar miskini.

فَوَيْلٌ لِّلْمُصَلِّينَ (4)
4. To azaba ta tabbata ga masallata.

الَّذِينَ هُمْ عَن صَلَاتِهِمْ سَاهُونَ (5)

5. Wad'annan da suke masu shagala daga sallarsu.

الَّذِينَ هُمْ يُرَاؤُونَ (6)

6. Wad'annan da suke yin riya.

وَيَمْنَعُونَ الْمَاعُونَ (7)

7. Kuma suke hana taimako.




سورة قريش

Surar K'uraishawa

بسم الله الرحمن الرحيم

Da Sunan Allah Mai Rahama Mai Jin K'ai

لِإِيلَافِ قُرَيْشٍ (1)

1. Saboda sabon k'uraishawa.

إِيلَافِهِمْ رِحْلَةَ الشِّتَاء وَالصَّيْفِ (2)

2. Sabonsu na tafiyar hunturu da ta bazara.

فَلْيَعْبُدُوا رَبَّ هَذَا الْبَيْتِ (3)

3. Don haka sai su bauta wa ubangijin wannan d'akin.

الَّذِي أَطْعَمَهُم مِّن جُوعٍ وَآمَنَهُم مِّنْ خَوْفٍ (4)

4. Wanda ya ciyar da su daga yunwa, kuma ya amintar da su daga wani tsoro.



سورة الفيل

Surar Giwa

بسم الله الرحمن الرحيم

Da Sunan Allah Mai Rahama Mai Jin K'ai

أَلَمْ تَرَ كَيْفَ فَعَلَ رَبُّكَ بِأَصْحَابِ الْفِيلِ (1)

1. Ashe ba ka ga yadda ubangijinka ya aikata ga mutanen giwa ba?

أَلَمْ يَجْعَلْ كَيْدَهُمْ فِي تَضْلِيلٍ (2)

2. Ashe bai sanya kaidinsu a cikin tab'ewa ba.

وَأَرْسَلَ عَلَيْهِمْ طَيْراً أَبَابِيلَ (3)

3. Kuma ya aika musu da wasu tsuntsaye gungu-gungu.

تَرْمِيهِم بِحِجَارَةٍ مِّن سِجِّيلٍ (4)

4. Suna jifar su da wasu duwatsu na yumb'un wuta.

فَجَعَلَهُمْ كَعَصْفٍ مَّأْكُولٍ (5)

5. Sai ya sanya su kamar karmami abin cinyewa.



سورة الهُمَزَة

Surar Mai Zumd'e

بسم الله الرحمن الرحيم

Da Sunan Allah Mai Rahama Mai Jin K'ai

وَيْلٌ لِّكُلِّ هُمَزَةٍ لُّمَزَةٍ (1)

1. Azaba ta tabbata ga dukkan wani, mai zumd'e, mai gatsine.

الَّذِي جَمَعَ مَالاً وَعَدَّدَهُ (2)

2. Wanda ya tara dukiya ya yi tattalinta.

يَحْسَبُ أَنَّ مَالَهُ أَخْلَدَهُ (3)

3. Yana tsammanin dukiyarsa zata dawwamar da shi.

كَلَّا لَيُنبَذَنَّ فِي الْحُطَمَةِ (4)

4. A'aha! Lalle sai an jefa shi a cikin hud'ama.

وَمَا أَدْرَاكَ مَا الْحُطَمَةُ (5)

5. Kuma me ya sanar da kai ko mece ce hud'ama.

نَارُ اللَّهِ الْمُوقَدَةُ (6)

6. Wutar Allah ce abar hurawa.

الَّتِي تَطَّلِعُ عَلَى الْأَفْئِدَةِ (7)

7. Wacce take lek'awa a kan zuciya.

إِنَّهَا عَلَيْهِم مُّؤْصَدَةٌ (8)

8. Hak'ik'a ita abar kullewa ce a kansu.

فِي عَمَدٍ مُّمَدَّدَةٍ (9)

9. A cikin wasu ginshik'ai mik'ak'k'u.



سورة العصر

Surar Zamani

بسم الله الرحمن الرحيم

Allah Sunan Allah Mai Rahama Mai Jin K'ai

وَالْعَصْرِ (1)

1. Ina rantsuwa da zamani

إِنَّ الْإِنسَانَ لَفِي خُسْرٍ (2)

2. Hak'ik'a mutum yana cikin hasara.

إِلَّا الَّذِينَ آمَنُوا وَعَمِلُوا الصَّالِحَاتِ وَتَوَاصَوْا بِالْحَقِّ وَتَوَاصَوْا بِالصَّبْرِ (3)

3. Sai dai wad'anda suka yi imani, kuma suka yi ayyukan k'warai, kuma suka yi wa juna wasici da bin gaskiya, kuma suka yi wa juna wasici da yin hak'uri.





سورة التكاثر

Surar Yawan Tara Arziki


بسم الله الرحمن الرحيم

Da Sunan Allah Mai Rahama Mai Jin K'ai

أَلْهَاكُمُ التَّكَاثُرُ (1)

1. Rigen Yawan tara arziki ne ya shagaltar da ku.

حَتَّى زُرْتُمُ الْمَقَابِرَ (2)

2. Har kuka ziyarci kaburbura.

كَلَّا سَوْفَ تَعْلَمُونَ (3)

3. A'aha! Zaku sani.

ثُمَّ كَلَّا سَوْفَ تَعْلَمُونَ (4)

4. Sannan tabbas zaku sani.

كَلَّا لَوْ تَعْلَمُونَ عِلْمَ الْيَقِينِ (5)

5. Hak'ik'a da ku san sani na yak'ini.

لَتَرَوُنَّ الْجَحِيمَ (6)

6. Da kun ga wutar Jahim.

ثُمَّ لَتَرَوُنَّهَا عَيْنَ الْيَقِينِ (7)

7. Kuma tabbas zaku gan ta idanu k'uru-k'uru.

ثُمَّ لَتُسْأَلُنَّ يَوْمَئِذٍ عَنِ النَّعِيمِ (8)


8. Sannan tabbas za a tambaye ku a wannan ranar game da ni'imar.



سورة القارعة

Surar Mai K'wank'wasa

بسم الله الرحمن الرحيم

Da Sunan Allah Mai Rahama Mai Jin K'ai

الْقَارِعَةُ (1)

1. Mai K'wank'wasa.

مَا الْقَارِعَةُ (2)

2. Mece ce mai k'wank'wasa.

وَمَا أَدْرَاكَ مَا الْقَارِعَةُ (3)

3. Kuma me ya sanar da kai mece ce mai k'wank'wasa.

يَوْمَ يَكُونُ النَّاسُ كَالْفَرَاشِ الْمَبْثُوثِ (4)

4. Ranar da mutane zasu kasance kamar fari masu watsuwa.

وَتَكُونُ الْجِبَالُ كَالْعِهْنِ الْمَنفُوشِ (5)

5. Kuma duwatus su kasance kamar gashin suf da aka sab'e.

فَأَمَّا مَن ثَقُلَتْ مَوَازِينُهُ (6)

6. To amma wanda ma'aunansa suka yi nauyi.

فَهُوَ فِي عِيشَةٍ رَّاضِيَةٍ (7)

7. To shi yana cikin wata rayuwa yardajjiya.

وَأَمَّا مَنْ خَفَّتْ مَوَازِينُهُ (8)
8. To amma kuma wanda ma'aunansa suka yi sako-sako.

فَأُمُّهُ هَاوِيَةٌ (9)

9. To uwarsa Hawiya ce.

وَمَا أَدْرَاكَ مَا هِيَهْ (10)

10. Me ya sanar da kai mece ce ita?.

نَارٌ حَامِيَةٌ (11)

11. Wata wuta ce mai zafi.



سورة العاديات

Surar Dawakai

بسم الله الرحمن الرحيم

Allah Sunan Allah Mai Rahama Mai Jin K'ai

وَالْعَادِيَاتِ ضَبْحاً (1)


1. Ina rantsuwa da dawakai masu gudu, suna masu k'ugin ciki.

فَالْمُورِيَاتِ قَدْحاً (2)

2. Da masu k'yasta wuta k'yastawa.

فَالْمُغِيرَاتِ صُبْحاً (3)

3. Sannan da masu kai hari lokacin Asuba.

فَأَثَرْنَ بِهِ نَقْعاً (4)

4. Sai su tayar da k'ura da shi (harin).

فَوَسَطْنَ بِهِ جَمْعاً (5)
5. Sai su kutsa cikin jama'ar mayak'a da ita (k'urar).

إِنَّ الْإِنسَانَ لِرَبِّهِ لَكَنُودٌ (6)

6. Hak'ik'a mutum mai tsananin butulci ne ga Ubangijinsa.

وَإِنَّهُ عَلَى ذَلِكَ لَشَهِيدٌ (7)

7. Kuma lalle shi mai sheda ne a kan hakan.

وَإِنَّهُ لِحُبِّ الْخَيْرِ لَشَدِيدٌ (8)

8. Kuma lalle shi mai tsananin so ne ga alheri.


أَفَلَا يَعْلَمُ إِذَا بُعْثِرَ مَا فِي الْقُبُورِ (9)‏

9. Shin ba ya sanin idan aka tone abin da yake cikin kaburbura.

وَحُصِّلَ مَا فِي الصُّدُورِ (10)

10. Kuma aka bayyana abin da yake cikin zukata.

إِنَّ رَبَّهُم بِهِمْ يَوْمَئِذٍ لَّخَبِيرٌ (11)

11. Lalle Ubangijinsu masani ne game da su a wannan ranar.




سورة الزلزلة

Surar Girgiza

بسم الله الرحمن الرحيم

Da Sunan Allah Mai Rahama Mai Jin K'ai

إِذَا زُلْزِلَتِ الْأَرْضُ زِلْزَالَهَا (1)

1. Idan aka girgiza k'asa girgizawarta.

وَأَخْرَجَتِ الْأَرْضُ أَثْقَالَهَا (2)

2. Kuma k'asa ta fitar da kayan nauyin da suke cikinta.

وَقَالَ الْإِنسَانُ مَا لَهَا (3)

3. Kuma mutum ya ce: Mene ne ya same ta?.

يَوْمَئِذٍ تُحَدِّثُ أَخْبَارَهَا (4)

4. A ranar nan zata fad'i labaranta.

بِأَنَّ رَبَّكَ أَوْحَى لَهَا (5)

5. Cewa Ubangijinka ne ya yi mata umarni.

يَوْمَئِذٍ يَصْدُرُ النَّاسُ أَشْتَاتاً لِّيُرَوْا أَعْمَالَهُمْ (6)

6. A ranar nan mutane zasu zo jama'a-jama'a domin a nuna musu ayyukansu.

فَمَن يَعْمَلْ مِثْقَالَ ذَرَّةٍ خَيْراً يَرَهُ (7)
7. To wanda ya aikta wani aiki gwargwadon nauyin zarra na alheri, zai gan shi.

وَمَن يَعْمَلْ مِثْقَالَ ذَرَّةٍ شَرّاً يَرَهُ (8)

8. Kuma wanda ya aikata wani aiki gwargwadon nauyin zarra na sharri, zai gan shi.



سورة البينة

Surar Hujja

Tana karantar da halayen kifirai da mutanen Littafi, wato Yahudu da Nasara game da Annabi (s.a.w), da Mushirikai tun gabanin da kuma bayan bayyanarsa.

بِِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ

Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin K'ai

لَمْ يَكُنِ الَّذِينَ كَفَرُوا مِنْ أَهْلِ الْكِتَابِ وَالْمُشْرِكِينَ مُنفَكِّينَ حَتَّى تَأْتِيَهُمُ الْبَيِّنَةُ

1. Wad'anda suka kafirta daga mutanen Littafi, da mushirikai, ba su kasance masu gushewa daga gaskiya ba har sai da hujja ta zo musu.

رَسُولٌ مِّنَ اللَّهِ يَتْلُو صُحُفًا مُّطَهَّرَةً

2. Wani Manzo daga Allah yana karanta wasu takardu masu tsarki.

فِيهَا كُتُبٌ قَيِّمَةٌ

3. A cikinsu akwai wasu littattafai masu d'aukaka.

وَمَا تَفَرَّقَ الَّذِينَ أُوتُوا الْكِتَابَ إِلَّا مِن بَعْدِ مَا جَاءتْهُمُ الْبَيِّنَةُ

4. Kuma wad'anda aka bai wa Littafi ba su rarrabu ba sai bayan hujja ta zo musu.

وَمَا أُمِرُوا إِلَّا لِيَعْبُدُوا اللَّهَ مُخْلِصِينَ لَهُ الدِّينَ حُنَفَاء وَيُقِيمُوا الصَّلَاةَ وَيُؤْتُوا الزَّكَاةَ وَذَلِكَ دِينُ الْقَيِّمَةِ

5. Kuma ba a umarce su da komai ba sai su bauta wa Allah suna masu tsarkake addini gare Shi, masu daidaito, kuma su tsayar da salla, kuma su bayar da zakka, kuma wannan shi ne addinin nagarta.

إِنَّ الَّذِينَ كَفَرُوا مِنْ أَهْلِ الْكِتَابِ وَالْمُشْرِكِينَ فِي نَارِ جَهَنَّمَ خَالِدِينَ فِيهَا أُوْلَئِكَ هُمْ شَرُّ الْبَرِيَّةِ

6. HaK'iK'a ne wad'anda suka kafirta daga mutanen Littafi da mushirikai suna cikin wutar Jahannama suna madawwama a cikinta, wad'annan su ne mafi sharrin talikai.

إِنَّ الَّذِينَ آمَنُوا وَعَمِلُوا الصَّالِحَاتِ أُوْلَئِكَ هُمْ خَيْرُ الْبَرِيَّةِ

7. HaK'iK'a wad'annan nan da suka yi imani kuma suka yi ayyuka na gari, wad'annan su ne mafifitan talikai.

جَزَاؤُهُمْ عِندَ رَبِّهِمْ جَنَّاتُ عَدْنٍ تَجْرِي مِن تَحْتِهَا الْأَنْهَارُ خَالِدِينَ فِيهَا أَبَدًا رَّضِيَ اللَّهُ عَنْهُمْ وَرَضُوا عَنْهُ ذَلِكَ لِمَنْ خَشِيَ رَبَّهُ

8. Sakamakonsu, a wurin Ubangijinsu, shi ne gidajen Aljannar Adnu, K'oramu suna gudana daga K'arK'ashinsu suna madawwama a cikinta har abada, Allah Ya yarda da su, kuma su ma sun yarda da Shi, wannan (sakamako ne) ga wanda ya ji tsoron Ubangijinsa.


سورة القدر
Surar Daraja

Tana karantar da son Allah ga wannan al'umma ta Musulmi da Ya ba su Dare mai Daraja "Lailatul K'adr" domin Ya yawaita ladar ayyukansu ko da yake rayukansu ba su da tsawo kamar na al'ummomin farko, kamar yadda take nuna cewa; alaK'ar Allah (s.w.t) da bayinsa ba ta yankewa da yankewar Annabci.

بِِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ

Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin K'ai.

إِنَّا أَنزَلْنَاهُ فِي لَيْلَةِ الْقَدْرِ

1. Lalle ne Mu, Mun saukar da shi a cikin Dare mai daraja.

وَمَا أَدْرَاكَ مَا لَيْلَةُ الْقَدْرِ

2. To, me ya sanar da kai abin da ake cewa Lailatul K'adari?

لَيْلَةُ الْقَدْرِ خَيْرٌ مِّنْ أَلْفِ شَهْرٍ

3. Lailatul K'adari mafi alheri ne daga watanni dubu.

تَنَزَّلُ الْمَلَائِكَةُ وَالرُّوحُ فِيهَا بِإِذْنِ رَبِّهِم مِّن كُلِّ أَمْرٍ

4. Mala'iku da Ruhi suna sauka a cikinsa da izinin Ubangijinsu daga kowane umurni.

سَلَامٌ هِيَ حَتَّى مَطْلَعِ الْفَجْرِ

5? Aminci ne shi har B'ollowar alfijiri.



سورة العلق

Surar Gudan Jini

Tana karantar da cewa karatu shi ne gaba da komai, amma a gama shi da sunan Allah, kuma duk wanda ya kauce wa hanyar Allah zai samu uK'uba


بِِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ

Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin K'ai

اقْرَأْ بِاسْمِ رَبِّكَ الَّذِي خَلَقَ

1. Ka yi karatu da sunan Ubangijinka, wanda Ya yi halitta.

خَلَقَ الْإِنسَانَ مِنْ عَلَقٍ

2. Ya hahitta mutum daga gudan jini.

اقْرَأْ وَرَبُّكَ الْأَكْرَمُ

3. Ka yi karatu, kuma Ubangijinka shi ne Mafi karimci.

الَّذِي عَلَّمَ بِالْقَلَمِ

4. Shi ne wannan da ya koyar da alK'alami.

عَلَّمَ الْإِنسَانَ مَا لَمْ يَعْلَمْ

5. Ya sanar da mutum abin da bai sani ba.

كَلَّا إِنَّ الْإِنسَانَ لَيَطْغَى

6. A'aha! Lalle, ne mutum yana girman kai.

أَن رَّآهُ اسْتَغْنَى

7. Domin ya ga kansa, ya wadatu.

إِنَّ إِلَى رَبِّكَ الرُّجْعَى

8. HaK'iK'a zuwa ga Ubangijinka makoma take.

أَرَأَيْتَ الَّذِي يَنْهَى

9. Shin, ka ga wanda ke hana.

عَبْدًا إِذَا صَلَّى

10. Bawa idan ya yi salla?

أَرَأَيْتَ إِن كَانَ عَلَى الْهُدَى

11. Ashe, ka gani, idan ya kasance a kan shiriya?

أَوْ أَمَرَ بِالتَّقْوَى

12. Ko ya yi umurni da taK'awa?
أَرَأَيْتَ إِن كَذَّبَ وَتَوَلَّى

13. Ashe, ka gani, idan ya K'aryata, kuma ya juya baya?

أَلَمْ يَعْلَمْ بِأَنَّ اللَّهَ يَرَى

14. Ashe, bai sani ba cewa Allah Yana gani?

كَلَّا لَئِن لَّمْ يَنتَهِ لَنَسْفَعًا بِالنَّاصِيَةِ

15. A'aha! Lalle ne, idan bai hanu ba, tabbas zamu ja gashin maK'warK'wad'a.

نَاصِيَةٍ كَاذِبَةٍ خَاطِئَةٍ

16. MaK'warK'wad'a, maK'aryaciya, mai laifi.

فليدع نادية.

17. To sai ya kira K'ungiyarsa.

سَنَدْعُ الزَّبَانِيَةَ

18. Zamu kira zabaniyawa.

كَلَّا لَا تُطِعْهُ وَاسْجُدْ وَاقْتَرِبْ

19. A'aha kada ka bi shi, kuma ka yi sujada, ka nemi kusanci.



سورة التين

Surar B'aure

Tana karantar da cewa dukkan abin da ya shafi imani da aiki na gari ba ya taB'ewa, amma sauran abubuwa suna halaka

بِِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ

Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin K'ai

وَالتِّينِ وَالزَّيْتُونِ

Ina rantsuwa da B'aure da Zaitun.

وَطُورِ سِينِينَ

Da Dutsen Sina.

وَهَذَا الْبَلَدِ الْأَمِينِ

Da wannan gari amintacce.

لَقَدْ خَلَقْنَا الْإِنسَانَ فِي أَحْسَنِ تَقْوِيمٍ

Lalle ne, Mun halitta mutum a cikin mafi kyawon daidaito.

ثُمَّ رَدَدْنَاهُ أَسْفَلَ سَافِلِينَ

Sannan Muka mayar da shi mafi K'asK'antar K'asK'antattu.

إِلَّا الَّذِينَ آمَنُوا وَعَمِلُوا الصَّالِحَاتِ فَلَهُمْ أَجْرٌ غَيْرُ مَمْنُونٍ

Sai dai wad'anda suka yi imani, kuma suka yi ayyuka na K'warai, To wad'annan suna da sakamako wanda ba ya yankewa.

فَمَا يُكَذِّبُكَ بَعْدُ بِالدِّينِ

To, bayan haka me ya sanya ka K'aryata sakamako.

أَلَيْسَ اللَّهُ بِأَحْكَمِ الْحَاكِمِينَ

Ashe Allah ba Shi ne Mafi iya hukuncin masu hukunci ba?



سورة الشرح

Surar Yalwatawa

Tana nuna ni'imomin da Allah Ya yi wa Annabi, (s.a.w) domin ya K'ara godiya ga Allah (s.w.t)

بِِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ

Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin K'ai

أَلَمْ نَشْرَحْ لَكَ صَدْرَكَ

1. Shin ba Mu yalwata maka zuciyarka ba.

وَوَضَعْنَا عَنكَ وِزْرَكَ

2. Kuma Muka saryar maka da nauyinka.

الَّذِي أَنْقَضَ ظَهْرَكَ

3. Wanda ya nauyaya bayanka.

وَرَفَعْنَا لَكَ ذِكْرَكَ

4. Kuma Muka d'aukaka maka ambatonka.

فَإِنَّ مَعَ الْعُسْرِ يُسْرًا

5. To, lalle ne tare da tsanani akwai wani sauK'i.

إِنَّ مَعَ الْعُسْرِ يُسْرًا

6. Lalle ne tare da tsanani akwai wani sauK'in.

فَإِذَا فَرَغْتَ فَانصَبْ

7. Saboda haka idan ka K'are sai ka kafu.

وَإِلَى رَبِّكَ فَارْغَبْ

8. Kuma ka yi kwad'ayi zuwa ga Ubangijinka.



سورة الضحى

Surar Hantsi

Tana karantar da ni'imomin da Allah Ya yi wa Annabi, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, da neman ya yi godiya a kansu ta hanyar biyayya ga umarnin Allah.

بِِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ

Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin K'ai

وَالضُّحَى

1. Ina rantsuwa da hantsi

وَاللَّيْلِ إِذَا سَجَى

2. Da dare a lokacin da ya rufe (da duhunsa)

مَا وَدَّعَكَ رَبُّكَ وَمَا قَلَى

3. Ubangijinka bai K'yale ka ba, kuma bai K'i kaba

وَلَلْآخِرَةُ خَيْرٌ لَّكَ مِنَ الْأُولَى

4. Kuma lalle K'arshe ce mafi alheri a gare ka daga farko

وَلَسَوْفَ يُعْطِيكَ رَبُّكَ فَتَرْضَى

5. Kuma lalle ne, Ubangijinka zai yi ta ba ka kyauta sai ka yarda.

أَلَمْ يَجِدْكَ يَتِيمًا فَآوَى

6. Ashe, bai same ka maraya ba, sa'an nan Ya yi maka mafaka?

وَوَجَدَكَ ضَالًّا فَهَدَى

7. Kuma Ya same ka ba ka da shari'a, sai Ya shiryar da kai?

وَوَجَدَكَ عَائِلًا فَأَغْنَى

8. Kuma Ya same ka matalauci, sai Ya wadata ka?

فَأَمَّا الْيَتِيمَ فَلَا تَقْهَرْ

9. Saboda haka, amma maraya, to, kada ka rinjaye shi.

وَأَمَّا السَّائِلَ فَلَا تَنْهَرْ

10. Kuma amma mai tambaya, kada ka yi masa kyara.

وَأَمَّا بِنِعْمَةِ رَبِّكَ فَحَدِّثْ

11. Kuma amma ni'imar Ubangijinka, sai ka fad'a.