Lail Zuwa Mudaffifin

Hafiz Muhammad Sa'id  hfazah@yahoo.com

 

SURAR LAIL ZUWA MUD'AFFIFIN



سورة الليل

Surar Dare

Tana karantar da dangantaka tsakanin d'abi'a da halitta da ak'ibar mutum bisa aikinsa, da kuma kasuwar abubuwa tsakanin alheri da sharri.

بِِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ

Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin K'ai

وَاللَّيْلِ إِذَا يَغْشَى

1. Ina rantsuwa da dare a lokacin da yake rufewa.

وَالنَّهَارِ إِذَا تَجَلَّى

2. Da lokacin rana yayin da bayyana.

وَمَا خَلَقَ الذَّكَرَ وَالْأُنثَى

3. Da abin da ya halitta namiji da mace.

إِنَّ سَعْيَكُمْ لَشَتَّى

4. Hak'ik'a ayyukanku, mabambanta ne.

فَأَمَّا مَن أَعْطَى وَاتَّقَى

5. To, amma wanda ya yi kyauta, kuma ya yi tak'awa.

وَصَدَّقَ بِالْحُسْنَى

6. Kuma ya gaskata kalma mai kyawo.

فَسَنُيَسِّرُهُ لِلْيُسْرَى

7. To, za Mu sauk'ak'e masa har ya kai ga sauki.

وَأَمَّا مَن بَخِلَ وَاسْتَغْنَى

8. Kuma amma wanda ya yi rowa, kuma ya wadatu da kansa.

وَكَذَّبَ بِالْحُسْنَى

9. Kuma ya k'aryatar da kalma mai kyawo.

فَسَنُيَسِّرُهُ لِلْعُسْرَى

10. To, za Mu sauk'ak'e masa har ya kai ga tsanani.

وَمَا يُغْنِي عَنْهُ مَالُهُ إِذَا تَرَدَّى

11. Kuma dukiyarsa ba ta wadatar masa da komai idan ya gangara (wuta).

إِنَّ عَلَيْنَا لَلْهُدَى

12. Lalle aikinMu ne, Mu bayyana shiriya.

وَإِنَّ لَنَا لَلْآخِرَةَ وَالْأُولَى

13. Kuma lalle ne Lahira da duniya Namu ne.

فَأَنذَرْتُكُمْ نَارًا تَلَظَّى

14. Saboda haka, Na yi maku gargad'i da wuta mai babbaka.

لَا يَصْلَاهَا إِلَّا الْأَشْقَى

15. Babu mai shigarta sai mafi shak'awa.

الَّذِي كَذَّبَ وَتَوَلَّى

16. Wanda ya k'aryata, kuma ya juya baya.

وَسَيُجَنَّبُهَا الْأَتْقَى

17. Kuma mafi tak'awa zai nisance ta.

الَّذِي يُؤْتِي مَالَهُ يَتَزَكَّى

18. Wanda yake bayar da dukiyarsa ,alhali yana tsarkaka.

وَمَا لِأَحَدٍ عِندَهُ مِن نِّعْمَةٍ تُجْزَى

19. Alhali babu wani mai wata ni'ima wurinsa wadda ake neman sakamakonta.

إِلَّا ابْتِغَاء وَجْهِ رَبِّهِ الْأَعْلَى

20. Face dai neman yardar Ubangijinsa Mafi d'aukaka.

وَلَسَوْفَ يَرْضَى

21. Kuma tabbas da sannu zai yarda.



سورة الشمس

Surar Rana

Tana karantar da cewa idan azaba ta sauka a kan mutane takan shafi mai laifi da wanda ba shi da laifi daga cikinsu, da kuma nuni zuwa ga had'arin k'aryata ayar Allah mad'aukaki.

بِِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ

Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin K'ai.

وَالشَّمْسِ وَضُحَاهَا

1. Ina rantsuwa da rana da hantsinta.

وَالْقَمَرِ إِذَا تَلَاهَا

2. Kuma da wata idan ya bi ta.

وَالنَّهَارِ إِذَا جَلَّاهَا

3. Da yini a lokacin da ya bayyana ta.

وَاللَّيْلِ إِذَا يَغْشَاهَا

4. Da dare a lokacin da ya ke rufe ta.

وَالسَّمَاءِ وَمَا بَنَاهَا

5. Da sama da abin da ya gina ta.

وَالْأَرْضِ وَمَا طَحَاهَا

6. Da k'asa da abin da ya shimfid'a ta.

وَنَفْسٍ وَمَا سَوَّاهَا

7. Da rai da abin da ya daidaita shi.

فَأَلْهَمَهَا فُجُورَهَا وَتَقْوَاهَا

8. Sa'an nan ya sanar da shi fajircinsa da shiryuwarsa.

قَدْ أَفْلَحَ مَن زَكَّاهَا

9. Lalle ne wanda ya tsarkake shi (rai) ya sami babban rabo.

وَقَدْ خَابَ مَن دَسَّاهَا

10. Kuma lalle ne wanda ya turbud'e shi (da laifi) ya tab'e.

كَذَّبَتْ ثَمُودُ بِطَغْوَاهَا

11. Samudawa sun k'aryata domin girman kansu.

إِذِ انبَعَثَ أَشْقَاهَا

12. A lokacin da mafi shak'awarsu ya tafi.

فَقَالَ لَهُمْ رَسُولُ اللَّهِ نَاقَةَ اللَّهِ وَسُقْيَاهَا

13. Sai Manzon Allah ya gaya musu cewa: "Ina tsoratar da ku ga rakumar Allah da ruwan shanta!"

فَكَذَّبُوهُ فَعَقَرُوهَا فَدَمْدَمَ عَلَيْهِمْ رَبُّهُم بِذَنبِهِمْ فَسَوَّاهَا

14. Sai suka k'aryata shi, sa'an nan suka soke ta. Saboda haka Ubangijinsu Ya darkake su saboda zunubinsu kuma ya daidaita ta (azabar).

وَلَا يَخَافُ عُقْبَاهَا

15. Kuma ba ya tsoron ak'ibarta (ita halakawar).


سورة البلد

Surar Gari

Tana karantar da cewa mutum an halitta shi cikin wahala, komai amfaninsa idan ya bi umurnin Allah ko kuma cutarsa idan ya sab'a wa umurnin Allah


بِِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ

Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin K'ai

لَا أُقْسِمُ بِهَذَا الْبَلَدِ

1. Ba sai Na yi rantsuwa da wannan gari ba.

وَأَنتَ حِلٌّ بِهَذَا الْبَلَدِ

2. Da kuma kai kana mai sauka a cikin wannan gari.

وَوَالِدٍ وَمَا وَلَدَ

3. Da mahaifi da abin da ya haifa.

لَقَدْ خَلَقْنَا الْإِنسَانَ فِي كَبَدٍ

4. Lalle ne, Mun halitta mutum cikin wahala.

أَيَحْسَبُ أَن لَّن يَقْدِرَ عَلَيْهِ أَحَدٌ

5. Shin ko yana zaton babu wani mai iya samun iko a kansa?

يَقُولُ أَهْلَكْتُ مَالًا لُّبَدًا

6. Yana cewa; Na kashe dukiya mai yawa.

أَيَحْسَبُ أَن لَّمْ يَرَهُ أَحَدٌ

7. Shin, ko yana zaton cewa wani bai gan shi ba?

أَلَمْ نَجْعَل لَّهُ عَيْنَيْنِ

8. Shin, ba Mu sanya masa idanu biyu ba?

وَلِسَانًا وَشَفَتَيْنِ

9. Da harshe, da leb'b'a biyu.

وَهَدَيْنَاهُ النَّجْدَيْنِ

10. Kuma muka shiryar da shi ga hanyoyi biyu?

فَلَا اقْتَحَمَ الْعَقَبَةَ

11. To, don mene ne bai shiga Ak'aba ba?

وَمَا أَدْرَاكَ مَا الْعَقَبَةُ

12. Kuma mene ne ya sanar da kai abin da ake ce wa Ak'aba?

فَكُّ رَقَبَةٍ

13. Ita ce fansar wuyan bawa.

أَوْ إِطْعَامٌ فِي يَوْمٍ ذِي مَسْغَبَةٍ

14. Ko kuma ciyar da ma'abucin yunwa, a cikin yini.

يَتِيمًا ذَا مَقْرَبَةٍ

15. Ga maraya ma'abucin zumunta.

أَوْ مِسْكِينًا ذَا مَتْرَبَةٍ

16. Ko kuwa wani matalauci ma'abucin turb'aya.

ثُمَّ كَانَ مِنَ الَّذِينَ آمَنُوا وَتَوَاصَوْا بِالصَّبْرِ وَتَوَاصَوْا بِالْمَرْحَمَةِ

17. Sa'an nan kuma ya kasance daga wad'anda suka yi imani, kuma suka yi wa juna wasiyya da yin hak'uri, kuma suka yi wa juna wasiyya da tausayi.

أُوْلَئِكَ أَصْحَابُ الْمَيْمَنَةِ

18. Wad'annan ne ma'abuta albarka.

وَالَّذِينَ كَفَرُوا بِآيَاتِنَا هُمْ أَصْحَابُ الْمَشْأَمَةِ

19. Kuma wad'anda suka kafirta da ayoyinmu, su ne ma'abuta shu'umci.

عَلَيْهِمْ نَارٌ مُّؤْصَدَةٌ

20. A kansu akwai wata wuta abar kullewa.




سورة الفجر

Surar Alfijir

بِِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ

Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin K'ai

وَالْفَجْرِ

1. Ina rantsuwa da alfijiri.

وَلَيَالٍ عَشْرٍ

2. Da darare goma.

وَالشَّفْعِ وَالْوَتْرِ

3. Da (adadi na) cika da (na) mara.

وَاللَّيْلِ إِذَا يَسْرِ

4. Da dare idan yana shud'ewa.

هَلْ فِي ذَلِكَ قَسَمٌ لِّذِي حِجْرٍ

5. Ko a cikin wad'annan akwai abin rantsuwa ga mai hankali.

أَلَمْ تَرَ كَيْفَ فَعَلَ رَبُّكَ بِعَادٍ

6. Ba ka ga yadda Ubangijinka Ya aikata da Adawa ba?

إِرَمَ ذَاتِ الْعِمَادِ

7. Iramawa masu sakon k'irar jiki.

الَّتِي لَمْ يُخْلَقْ مِثْلُهَا فِي الْبِلَادِ

8. Wad'anda ba a halitta kwatankwacinsu ba a cikin garuruwa.

وَثَمُودَ الَّذِينَ جَابُوا الصَّخْرَ بِالْوَادِ

9. Da samudawa wad'anda suka fasa duwatsu a cikin Wadi.

وَفِرْعَوْنَ ذِي الْأَوْتَادِ

10. Da Fir'auna mai turaku.

الَّذِينَ طَغَوْا فِي الْبِلَادِ

11. Wad'anda suka k'etare iyakarsu, a cikin garuruwa.

فَأَكْثَرُوا فِيهَا الْفَسَادَ

12. Sai suka yawaita yin b'arna a cikinsu.

فَصَبَّ عَلَيْهِمْ رَبُّكَ سَوْطَ عَذَابٍ

13. Saboda haka Ubangijinka Ya zuba musu bulalar azaba.

إِنَّ رَبَّكَ لَبِالْمِرْصَادِ

14. Lalle ne, Ubangijinka Yana nan a mafaka.

فَأَمَّا الْإِنسَانُ إِذَا مَا ابْتَلَاهُ رَبُّهُ فَأَكْرَمَهُ وَنَعَّمَهُ فَيَقُولُ رَبِّي أَكْرَمَنِ

15. To, amma fa mutum idan Ubangijibsa Ya jarraba shi, wato Ya girmama shi kuma Ya yi masa ni'ima, sai ya ce; Ubangijina Ya girmama ni.

وَأَمَّا إِذَا مَا ابْتَلَاهُ فَقَدَرَ عَلَيْهِ رِزْقَهُ فَيَقُولُ رَبِّي أَهَانَنِ

16. Kuma idan Ya jarraba shi, wato Ya k'untata masa arzikinsa, sai ya ce; Ubangijina Ya wulak'anta ni.

كَلَّا بَل لَّا تُكْرِمُونَ الْيَتِيمَ

17. A'aha! Bari wannan, ai ba kwa girmama maraya!

وَلَا تَحَاضُّونَ عَلَى طَعَامِ الْمِسْكِينِ

18. Ba kwa kwad'aita wa junanku ga (tattalin) abincin matalauci!

وَتَأْكُلُونَ التُّرَاثَ أَكْلًا لَّمًّا

19. Kuma kuna cin dukiyar gado, ci na tarawa.

وَتُحِبُّونَ الْمَالَ حُبًّا جَمًّا

20. Kuma kuna son dukiya, so mai yawa.

كَلَّا إِذَا دُكَّتِ الْأَرْضُ دَكًّا دَكًّا

21. A'aha! Idan aka nik'e k'asa nik'ewa sosai.

وَجَاء رَبُّكَ وَالْمَلَكُ صَفًّا صَفًّا

22. Kuma Ubangijinka Ya zo, alhali mala'iku na jere, safu- safu.

وَجِيءَ يَوْمَئِذٍ بِجَهَنَّمَ يَوْمَئِذٍ يَتَذَكَّرُ الْإِنسَانُ وَأَنَّى لَهُ الذِّكْرَى

23. Kuma a ranar nan aka zo da Jahannama. A ranar nan mutum zai yi tunani. To, ina fa tunani yake a gare shi!

يَقُولُ يَا لَيْتَنِي قَدَّمْتُ لِحَيَاتِي

24. Yana dinga cewa, Kaicona, ina ma dai na gabatar (da aikin k'warai) domin rayuwata!

فَيَوْمَئِذٍ لَّا يُعَذِّبُ عَذَابَهُ أَحَدٌ

25. To, a ranar nan babu wani mai yin azaba irin azabar Allah.

وَلَا يُوثِقُ وَثَاقَهُ أَحَدٌ

26. Kuma babu wani mai d'auri irin d'aurinSa.

يَا أَيَّتُهَا النَّفْسُ الْمُطْمَئِنَّةُ

27. Ya kai rai mai natsuwa!

ارْجِعِي إِلَى رَبِّكِ رَاضِيَةً مَّرْضِيَّةً

28. Ka koma zuwa ga Ubangijinka, alhali kana mai yarda, abin yardarwa.

فَادْخُلِي فِي عِبَادِي

29. Sabobda haka, ka shiga cikin .

وَادْخُلِي جَنَّتِي

30. Kuma ka shiga Aljannata.


Wadi: Shi ne "Wadil-kura" sunan wuri ne a k'asar Siriya "Sham".


سورة الغاشية

Surar Mai Rufewa

Tana karantar da yin hujja da abin da ake iya gani da ido domin a fahimci abin da ake gani da hankali, gwargwadon tunanin abokin magana.


بِِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ

Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin K'ai

هَلْ أَتَاكَ حَدِيثُ الْغَاشِيَةِ

1. Shin labarin (K'iyama) mai rufe (mutane da tsoronta) ya zo maka?

وُجُوهٌ يَوْمَئِذٍ خَاشِعَةٌ

2. Wasu fuskoki a ranar nan k'ask'antattu ne.

عَامِلَةٌ نَّاصِبَةٌ

3. Masu aikin wahala ne, masu gajiya.

تَصْلَى نَارًا حَامِيَةً

4. Za su shiga wata wuta mai zafi.

تُسْقَى مِنْ عَيْنٍ آنِيَةٍ

5. Ana shayar da su daga wani marmaro mai zafin ruwa.

لَّيْسَ لَهُمْ طَعَامٌ إِلَّا مِن ضَرِيعٍ

6. Ba su da wani abinci face dai daga danyi.

لَا يُسْمِنُ وَلَا يُغْنِي مِن جُوعٍ

7. Ba ya sanya k'iba, kuma ba ya wadatarwa daga yunwa.

وُجُوهٌ يَوْمَئِذٍ نَّاعِمَةٌ

8. Wasu fuskoki a ranar nan masu ni'ima ne.

لِسَعْيِهَا رَاضِيَةٌ

9. Masu yarda ne game da aikinsu.

فِي جَنَّةٍ عَالِيَةٍ

10. A cikin Aljanna mad'aukakiya.

لَّا تَسْمَعُ فِيهَا لَاغِيَةً

11. Ba za su ji yasassar magana ba, a cikinta.

فِيهَا عَيْنٌ جَارِيَةٌ

12. A cikinta akwai marmaro mai gudana.

فِيهَا سُرُرٌ مَّرْفُوعَةٌ

13. A cikinta akwai gadaje mad'aukaka.

وَأَكْوَابٌ مَّوْضُوعَةٌ

14. Da kofuna ar'aje.

وَنَمَارِقُ مَصْفُوفَةٌ

15. Da filoli (matasan kai) a jere.

وَزَرَابِيُّ مَبْثُوثَةٌ

16. Da katifu shimfid'e.

أَفَلَا يَنظُرُونَ إِلَى الْإِبِلِ كَيْفَ خُلِقَتْ

17. Ashe to ba zasu yi duba ga rakuma ba yadda aka halitta su?

وَإِلَى السَّمَاءِ كَيْفَ رُفِعَتْ

18. Da zuwa ga sama yadda aka daukaka ta?

وَإِلَى الْجِبَالِ كَيْفَ نُصِبَتْ

19. Da zuwa ga duwatsu yadda aka kafa su?

وَإِلَى الْأَرْضِ كَيْفَ سُطِحَتْ

20. Da zuwa ga k'asa yadda aka shimfid'a ta?

فَذَكِّرْ إِنَّمَا أَنتَ مُذَكِّرٌ

21. Saboda haka, ka yi wa'azi, kai mai yin wa'azi ne kawai.

لَّسْتَ عَلَيْهِم بِمُصَيْطِرٍ

22. Kai ba mai tankwasawa a kansu ba ne.

إِلَّا مَن تَوَلَّى وَكَفَرَ

23. Sai dai duk wanda ya juya baya, kuma ya kafirta.

فَيُعَذِّبُهُ اللَّهُ الْعَذَابَ الْأَكْبَرَ

24. To, Allah zai yi masa azaba, azabar nan da take mafi girma.

إِنَّ إِلَيْنَا إِيَابَهُمْ

25. Lalle ne, zuwa gare Mu komowarsu take.

ثُمَّ إِنَّ عَلَيْنَا حِسَابَهُمْ

26. Sa'an nan lalle ne aikinMu ne Mu yi musu hisabi.



سورة الأعلى

Surar Mafi D'aukaka

Tana karantar da cewa rayarwa da matarwa a hannun Allah suke, su kuma nau'i-nau'i ne

بِِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ

Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin K'ai

سَبِّحِ اسْمَ رَبِّكَ الْأَعْلَى

1. Ka tsarkake sunan Ubangijinka Mafi d'aukaka.

الَّذِي خَلَقَ فَسَوَّى

2. Wanda Ya yi halitta sa'an nan Ya daidaita abin halittar.

وَالَّذِي قَدَّرَ فَهَدَى

3. Kuma Wanda Ya k'addara (abin da ya so) sannan Ya shiryar.

وَالَّذِي أَخْرَجَ الْمَرْعَى

4. Kuma Wanda Ya fitar da makiyaya.

فَجَعَلَهُ غُثَاءً أَحْوَى

5. Sa'an nan Ya mayar da ita k'ek'asassa, bak'a.

سَنُقْرِؤُكَ فَلَا تَنسَى

6. Za mu karantar da kai, saboda haka ba za ka manta ba.

إِلَّا مَا شَاءَ اللَّهُ إِنَّهُ يَعْلَمُ الْجَهْرَ وَمَا يَخْفَى

7. Face abin da Allah Ya so, lalle ne Shi (Allah) Ya san bayyane da abin da yake b'oye.

وَنُيَسِّرُكَ لِلْيُسْرَى

8. Kuma za Mu sauk'ak'e maka zuwa ga mai sauk'i.

فَذَكِّرْ إِن نَّفَعَتِ الذِّكْرَى

9. Saboda baka, ka tunatar, idan tunatarwa za ta yi amfani.

سَيَذَّكَّرُ مَن يَخْشَى

10. Wanda yake tsoron (Allah) Zai tuna.

وَيَتَجَنَّبُهَا الْأَشْقَى

11. Kuma shak'iyyi, zai nisanceta.

الَّذِي يَصْلَى النَّارَ الْكُبْرَى

12. Wanda zai shiga wuta mafi girma.

ثُمَّ لَا يَمُوتُ فِيهَا وَلَا يَحْيَى

13. Sa'an nan ba zai mutu ba a cikinta, kuma ba zai rayu ba.

قَدْ أَفْلَحَ مَن تَزَكَّى

14. Lalle ne wanda ya tsarkaka ya samu babban rabo.

وَذَكَرَ اسْمَ رَبِّهِ فَصَلَّى

15. Kuma ya ambaci sunan Ubangijinsa, sa'an nan ya yi salla.

بَلْ تُؤْثِرُونَ الْحَيَاةَ الدُّنْيَا

16. Ba haka ba! Kuna dai zab'in rayuwar duniya ne.

وَالْآخِرَةُ خَيْرٌ وَأَبْقَى

17. Alhalin Lahira ita ce mafi alheri kuma mafi wanzuwa.

إِنَّ هَذَا لَفِي الصُّحُفِ الْأُولَى

18. Hak'ik'a wannan yana cikin littattafan farko.

صُحُفِ إِبْرَاهِيمَ وَمُوسَى

19. Littattafan Ibrahim da Musa.




سورة الطارق

Surar Mai Aukowa

Tana karantar da tsaron Al1ah ga kome bisa ga tsari, kuma kome asirinsa ne, sannan duk masu kaidi su sani cewa; Allah yana nan a madakata

بِِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ

Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin K'ai

وَالسَّمَاءِ وَالطَّارِقِ

1. Ina rantsuwa da sama da mai aukowa da dare.

وَمَا أَدْرَاكَ مَا الطَّارِقُ

2. To, me ya sanar da kai abin da ake cewa mai aukowa da dare?

النَّجْمُ الثَّاقِبُ

3. Shi ne tauraron nan mai tsananin haske.

إِن كُلُّ نَفْسٍ لَّمَّا عَلَيْهَا حَافِظٌ

4. Babu wani rai face a kansa akwai wani mai tsaro.

فَلْيَنظُرِ الْإِنسَانُ مِمَّ خُلِقَ

5. To, mutum ya duba, daga me aka halitta shi?

خُلِقَ مِن مَّاء دَافِقٍ

6. An halitta shi daga wani ruwa mai tunkud'ar juna.

يَخْرُجُ مِن بَيْنِ الصُّلْبِ وَالتَّرَائِبِ

7. Yana fita daga tsakanin tsatso da karankarman k'irji.

إِنَّهُ عَلَى رَجْعِهِ لَقَادِرٌ

8. Lalle ne Shi (Allah), ga mayar da shi (mutum), tabbas Mai iyawa ne.

يَوْمَ تُبْلَى السَّرَائِرُ

9. Ranar da ake jarrabawar asirai.

فَمَا لَهُ مِن قُوَّةٍ وَلَا نَاصِرٍ

10. Saboda haka, ba shi da wani karfi, kuma ba shi da wani mai taimako.

وَالسَّمَاءِ ذَاتِ الرَّجْعِ

11. Ina rantsuwa da sama ma'abuciyar ruwa mai komawa yana yankewa.

وَالْأَرْضِ ذَاتِ الصَّدْعِ

12. Da k'asa ma'abuciyar tsagewa.

إِنَّهُ لَقَوْلٌ فَصْلٌ

13. Hak'ik'a shi magana ce dalla-dalla (daki-daki).

وَمَا هُوَ بِالْهَزْلِ

14. Kuma shi ba bananci (kakaci da raha) ba ne.

إِنَّهُمْ يَكِيدُونَ كَيْدًا

15. Lalle ne su, suna k'ulla kaidi na sosai.

وَأَكِيدُ كَيْدًا

16. Kuma Ni, Ina (mayar da) kaidi sosai.

فَمَهِّلِ الْكَافِرِينَ أَمْهِلْهُمْ رُوَيْدًا

17. Saboda haka, ka yi wa kafirai jinkiri, ka dakata musu, sannu-sannu.




سورة البروج

Surar Taurari

Tana bayanin mugunyar ak'ibar masu wahalar da muminai a kan addininsu, ba da wata hujja ba ta shari'a

بِِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ

Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin K'ai

وَالسَّمَاءِ ذَاتِ الْبُرُوجِ

1. Ina rantsuwa da sama mai taurarin lissafin shekara.

وَالْيَوْمِ الْمَوْعُودِ

2. Da yinin da aka yi alk'awarin zuwansa.

وَشَاهِدٍ وَمَشْهُودٍ

3. Da yini mai shaidu, da yini da ake halarta.

قُتِلَ أَصْحَابُ الْأُخْدُودِ

4. An la'ani mutanen rami.

النَّارِ ذَاتِ الْوَقُودِ

5. Wuta ce wacce aka hura.

إِذْ هُمْ عَلَيْهَا قُعُودٌ

6. A lokacin da suke a gefenta a zazzaune.

وَهُمْ عَلَى مَا يَفْعَلُونَ بِالْمُؤْمِنِينَ شُهُودٌ

7. Alhali su, bisa ga abin da suke aikatawa ga muminai, suna halarce.

وَمَا نَقَمُوا مِنْهُمْ إِلَّا أَن يُؤْمِنُوا بِاللَّهِ الْعَزِيزِ الْحَمِيدِ

8. Kuma ba su azabtar da su ba, sai kawai domin sun yi imani da Allah Mabuwayi, abin godewa.

الَّذِي لَهُ مُلْكُ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ وَاللَّهُ عَلَى كُلِّ شَيْءٍ شَهِيدٌ

9. Wanda Yake shi ne da mulkin sammai da k'asa, kuma Allah a kan kome halarce Yake.

إِنَّ الَّذِينَ فَتَنُوا الْمُؤْمِنِينَ وَالْمُؤْمِنَاتِ ثُمَّ لَمْ يَتُوبُوا فَلَهُمْ عَذَابُ جَهَنَّمَ وَلَهُمْ عَذَابُ الْحَرِيقِ

10. Lalle ne wad'anda suka fitini muminai maza da muminai mata, sa'an nan ba su tuba ba, to suna da azabar Jahannama, kuma suna da azabar gobara.

إِنَّ الَّذِينَ آمَنُوا وَعَمِلُوا الصَّالِحَاتِ لَهُمْ جَنَّاتٌ تَجْرِي مِن تَحْتِهَا الْأَنْهَارُ ذَلِكَ الْفَوْزُ الْكَبِيرُ

11. Lalle ne wad'anda suka yi imani, kuma suka aikata ayyukan k'warai suna da gidajen Aljanna, k'oramu suna gudana daga k'ark'ashinsu, wancan abu fa shi ne rabo babba.

إِنَّ بَطْشَ رَبِّكَ لَشَدِيدٌ

12. Hak'ik'a damk'ar Ubangijinka mai tsanani ce k'warai.

إِنَّهُ هُوَ يُبْدِئُ وَيُعِيدُ

13. Hak'ik'a shi ne Mai k'aga halitta, kuma Ya mayar da ita.

وَهُوَ الْغَفُورُ الْوَدُودُ

14. Kuma Shi ne Mai gafara, Mai bayyana soyayya.

ذُو الْعَرْشِ الْمَجِيدُ

15. Mai Al'arshi mai girma

فَعَّالٌ لِّمَا يُرِيدُ

16. Mai aikatawa ga abin da Yake nufi.

هَلْ أَتَاكَ حَدِيثُ الْجُنُودِ

17. Ko labarin rundanoni ya zo maka.

فِرْعَوْنَ وَثَمُودَ

18. Fir'auna da samudawa?

بَلِ الَّذِينَ كَفَرُوا فِي تَكْذِيبٍ

19. A'aha! wad'anda suka kafirta suna cikin k'aryatawa.

وَاللَّهُ مِن وَرَائِهِم مُّحِيطٌ

20. Alhali, Allah Mai kewaye daga bayansu ne.

بَلْ هُوَ قُرْآنٌ مَّجِيدٌ

21. A'aha! Shi Kur'ani ne mai girma.

فِي لَوْحٍ مَّحْفُوظٍ

22. A cikin Allo tsararre.


Ma'abota Rami: Ko kuma Mutanen Rami: Su ne mutanen Najiran da suka yi rami suka hura wuta a ciki, domin su k'one wanda ya yi imani da addinin Masih Isa domin su hana yad'uwarsa. Suka umurci kowane Musulmi ya jefa kansa a ciki, su kuma suna zazzaune suna kallo.




سورة الإنشقاق

Surar Kecewa

Tana karantar da tabbatar Tashin K'iyama, kuma duka abin da ake aikatawa idan ba na tattalin K'iyamar ba ne, to, ya zama wahalar da kai, maras amfani, da b'ata lokaci.

بِِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ

Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin K'ai

إِذَا السَّمَاءُ انشَقَّتْ

1. Idan sama ta kece.

وَأَذِنَتْ لِرَبِّهَا وَحُقَّتْ

2. Ta saurari Ubangijinta, kuma aka wajabta mata yin sauraron.

وَإِذَا الْأَرْضُ مُدَّتْ

3. Kuma idan k'asa aka mike ta.

وَأَلْقَتْ مَا فِيهَا وَتَخَلَّتْ

4. Kuma ta jefar da abin da yake a cikinta, ta wofinta daga kome.

وَأَذِنَتْ لِرَبِّهَا وَحُقَّتْ

5. Kuma ta saurari Ubangijinta, aka wajabta mata yin sauraren.

يَا أَيُّهَا الْإِنسَانُ إِنَّكَ كَادِحٌ إِلَى رَبِّكَ كَدْحًا فَمُلَاقِيهِ

6. Ya kai mutum! Lalle ne kai mai aikin wahalar da kai ne zuwa ga Ubangijinka, wahala mai tsanani, kuma kai mai had'uwa da Shi ne.

فَأَمَّا مَنْ أُوتِيَ كِتَابَهُ بِيَمِينِهِ

7. To, amma wanda aka bai wa littafinsa a damansa.

فَسَوْفَ يُحَاسَبُ حِسَابًا يَسِيرًا

8. To, za a yi masa hisabi, hisabi mai sauk'i.

وَيَنقَلِبُ إِلَى أَهْلِهِ مَسْرُورًا

9. Kuma ya juya zuwa ga iyalinsa yana mai raha.

وَأَمَّا مَنْ أُوتِيَ كِتَابَهُ وَرَاءَ ظَهْرِهِ

10. Kuma amma wanda aka bai wa littafinsa, daga wajen bayansa.

فَسَوْفَ يَدْعُو ثُبُورًا

11. To, zai dinga kiran halaka!

وَيَصْلَى سَعِيرًا

12. Kuma ya shiga sa'ir.

إِنَّهُ كَانَ فِي أَهْلِهِ مَسْرُورًا

13. Lal1e ne shi, ya kasance a cikin iyalinsa yana mai raha.

إِنَّهُ ظَنَّ أَن لَّن يَحُورَ

14. Lalle ne ya yi zaton ba zai komo ba.

بَلَى إِنَّ رَبَّهُ كَانَ بِهِ بَصِيرًا

15. Na'am! Hak'ik'a Ubangijinsa Ya kasance Mai gani gare shi.

فَلَا أُقْسِمُ بِالشَّفَقِ

16. To, ba sai Na rantse da shafak'i ba.

وَاللَّيْلِ وَمَا وَسَقَ

17. Da dare, da abin da ya k'unsa.

وَالْقَمَرِ إِذَا اتَّسَقَ

18. Da wata idan ya cika.

لَتَرْكَبُنَّ طَبَقًا عَن طَبَقٍ

19. Lalle ne kuna hawan wani hali daga wani halin.

فَمَا لَهُمْ لَا يُؤْمِنُونَ

20. To, me ya same su, ba sa yin imani?

وَإِذَا قُرِئَ عَلَيْهِمُ الْقُرْآنُ لَا يَسْجُدُونَ

21. Kuma idan an karanta Kur'ani garesu ba sa k'ask'an da kai?

بَلِ الَّذِينَ كَفَرُواْ يُكَذِّبُونَ

22. Ba haka ba! wad'anda suka kafirta, sai k'aryatawa suke yi.

وَاللَّهُ أَعْلَمُ بِمَا يُوعُونَ

23. Alhali Allah Shi ne Mafi sani ga abin a suke tarawa.

فَبَشِّرْهُم بِعَذَابٍ أَلِيمٍ

24. Saboda haka, ka yi musu bushara da azaba mai rad'ad'i.

إِلَّا الَّذِينَ آمَنُواْ وَعَمِلُواْ الصَّالِحَاتِ لَهُمْ أَجْرٌ غَيْرُ مَمْنُونٍ

25. Sai dai wad'anda suka yi imani, suka aikata ayyukan k'warai, suna da wani sakamako wanda ba ya yankewa.


سورة المطففين

Surar Masu Tauye Awo

Tana karantar da wajabcin tsare hak'k'ok'in mutane tsakaninsu a ciniki da wasu mu'amalolin zamantakewa

بِِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ

Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin K'ai

وَيْلٌ لِّلْمُطَفِّفِينَ

1. Bone ya tabbata ga masu tauyewa.

الَّذِينَ إِذَا اكْتَالُواْ عَلَى النَّاسِ يَسْتَوْفُونَ

2. Wadanda suke idan suka auna daga mutane suna cika mudu.

وَإِذَا كَالُوهُمْ أَو وَّزَنُوهُمْ يُخْسِرُونَ

3. Kuma idan sun auna musu awon kwano ko awon sikeli, suna ragewa.

أَلَا يَظُنُّ أُولَئِكَ أَنَّهُم مَّبْعُوثُونَ

4. Ashe! Wad'ancan ba sa tsammanin cewa tabbas ana tayar da su ba?

لِيَوْمٍ عَظِيمٍ

5. Domin yini mai girma.

يَوْمَ يَقُومُ النَّاسُ لِرَبِّ الْعَالَمِينَ

6. Yinin da mutane ke tashi zuwa ga Ubangijin halitta?

كَلَّا إِنَّ كِتَابَ الفُجَّارِ لَفِي سِجِّينٍ

7. A'aha! Hak'ik'a littafin fajirai tabbas yana a cikin Sijjin.

وَمَا أَدْرَاكَ مَا سِجِّينٌ

8. Kuma, me ya sanar da kai abin da ake ce wa Sijjin?

كِتَابٌ مَّرْقُومٌ

9. Wani 1ittafi ne rubutacce.

وَيْلٌ يَوْمَئِذٍ لِّلْمُكَذِّبِينَ

10. Bone ya tabbata a ranar nan ga masu k'aryatawa.

الَّذِينَ يُكَذِّبُونَ بِيَوْمِ الدِّينِ

11. Wad'anda suke k'aryatawa game da ranar sakamako.

وَمَا يُكَذِّبُ بِهِ إِلَّا كُلُّ مُعْتَدٍ أَثِيمٍ

12. Babu mai k'aryatawa da ita sai dukkan mai k'etare haddi mai yawan zunubi.

إِذَا تُتْلَى عَلَيْهِ آيَاتُنَا قَالَ أَسَاطِيرُ الْأَوَّلِينَ

13. Idan ana karanta masa ayoyinmu, sai ya ce: Tatsuniyoyin mutanen farko ne.

كَلَّا بَلْ رَانَ عَلَى قُلُوبِهِم مَّا كَانُوا يَكْسِبُونَ

14. A'aha! Ba haka ba, abin da suka kasance suna aikatawa dai, ya yi tsatsa a cikin zukatansu.

كَلَّا إِنَّهُمْ عَن رَّبِّهِمْ يَوْمَئِذٍ لَّمَحْجُوبُونَ

15. A'aha! Hak'ik'a, su wad'anda ake shamakancewa daga Ubangijinsu ne a wannan ranar.

ثُمَّ إِنَّهُمْ لَصَالُوا الْجَحِيمِ

16. Sa'an nan, lalle ne, su masu shiga cikin Jahim ne.

ثُمَّ يُقَالُ هَذَا الَّذِي كُنتُم بِهِ تُكَذِّبُونَ

17. Sannan a ce; Wannan shi ne abin da kuka kasance kuna k'aryatawa da shi.

كَلَّا إِنَّ كِتَابَ الْأَبْرَارِ لَفِي عِلِّيِّينَ

18. A'aha! Hak'ik'a littafin masu d'a'a yana a cikin Illiyyina?

وَمَا أَدْرَاكَ مَا عِلِّيُّونَ

19. Kuma mene ne ya sanar da kai abin da ake cewa Illiyyuna?

كِتَابٌ مَّرْقُومٌ

20. Wani littafi ne rubutacce.

يَشْهَدُهُ الْمُقَرَّبُونَ

21. Mukarrabai ne suke halartar sa.

إِنَّ الْأَبْرَارَ لَفِي نَعِيمٍ

22. Hak'ik'a masu d'a'a suna cikin ni'ima.

عَلَى الْأَرَائِكِ يَنظُرُونَ

23. A kan karagu, suna ta kallo.

تَعْرِفُ فِي وُجُوهِهِمْ نَضْرَةَ النَّعِيمِ

24. Kana sanin walwalin ni'ima a fuskokinsu.

يُسْقَوْنَ مِن رَّحِيقٍ مَّخْتُومٍ

25. Ana shayar da su daga wata giya wadda aka yunk'e a kan rufinta.

خِتَامُهُ مِسْكٌ وَفِي ذَلِكَ فَلْيَتَنَافَسِ الْمُتَنَافِسُونَ

26. K'arshen kurb'inta al'miski ne. To, a cikin wannan, masu rige su yi ta rige.

وَمِزَاجُهُ مِن تَسْنِيمٍ

27. Kuma abin da ake gauraya ta da shi, daga tasnim yake.

عَيْنًا يَشْرَبُ بِهَا الْمُقَرَّبُونَ

28. Wani marmaro ne wanda muk'arrabai suke sha daga gare shi.

إِنَّ الَّذِينَ أَجْرَمُوا كَانُواْ مِنَ الَّذِينَ آمَنُوا يَضْحَكُونَ

29. Lalle ne, wad'anda suka kafirta sun kasance suna yi wa wad'anda suka yi imani dariya.

وَإِذَا مَرُّواْ بِهِمْ يَتَغَامَزُونَ

30. Kuma idan sun shud'e su sai su dinga yin zund'e.

وَإِذَا انقَلَبُواْ إِلَى أَهْلِهِمُ انقَلَبُواْ فَكِهِينَ

31. Kuma idan suka juya zuwa ga iyalansu, sai su tafi suna kakaci.

وَإِذَا رَأَوْهُمْ قَالُوا إِنَّ هَؤُلَاءِ لَضَالُّونَ

32. Kuma idan sun gan su sai su ce; Lalle wad'annan b'atattu ne.

وَمَا أُرْسِلُوا عَلَيْهِمْ حَافِظِينَ

33. Alhali kuwa, ba a aike su ba domin su zama masu lura da su.

فَالْيَوْمَ الَّذِينَ آمَنُواْ مِنَ الْكُفَّارِ يَضْحَكُونَ

34. To, yau fa wad'anda suka yi imani, su ne suke yi wa kafirai dariya.

عَلَى الْأَرَائِكِ يَنظُرُونَ

35. Suna masu kallo a kan karagu.

هَلْ ثُوِّبَ الْكُفَّارُ مَا كَانُوا يَفْعَلُونَ

36. Shin an saka wa kafirai abin da suka kasance suna aikatawa?