Makamin Ahlul-baiti

Makamin Ahlul-baiti25%

Makamin Ahlul-baiti Mawallafi:
: Mu'assasar Al-Balagh
: Muhummad Auwal Bauchi
Gungu: Asasin Addini

  • Farawa
  • Na Baya
  • 36 /
  • Na Gaba
  • Karewa
  •  
  • Gurzawa HTML
  • Gurzawa Word
  • Gurzawa PDF
  • Budawa: 11002 / Gurzawa: 3571
Girma Girma Girma
Makamin Ahlul-baiti

Makamin Ahlul-baiti

Mawallafi:
Hausa

Tafarkin Ahlulbaiti (a.s) Kan Ayyukan Siyasa

Duk wanda ya bibiyo salon siyasar Ahlulbaiti (a.s) da gwagwarmayarsu ta bayyane da ta boye a tsawon karno-ni biyu da rabi zai iya gano cewa aikin da suka yi na siyasa yana bisa ginshikai kamar haka:

(1). Tarbiyyantar da al'umma kan kin zalunci da tabbatar da manufar adalci da bayyana fikirar imamanci da siyasa da fayyace rukunan hukumci da shugabanci cikin addinin Musulunci. Sun yi haka ne domin karfafa fahimtar siyasa ga al'umma da karfafa kulawarta da kiyayyarta ga azzalumai, da farkar da ita daga barci. Wanda ya yi bitar abin da Ahlulbaiti (a.s) suka ruwaito suka watsa daga Manzon Allah (s.a.w.a.) dangane da wannan al'amari, zai gane muhimmancin wannan mataki wajen farfado da ruhin siyasa da kiyayewa ta Musulunci. A nan za mu ambaci wasu daga cikin ruwayoyin da suke magana dangane da shugabanci da kuma nauyin da suka hau kan shugaba musulmi, da kuma kyamar da Musulun-ci yake wa zalunci da kuma kira zuwa ga adalci, don mu fahimci fikira da tunanin Ahlulbaiti (a.s) wajen fada da zalunci da kuma kwadaitar da al'umma zuwa ga canji da kuma motsi na siyasa.

An ruwaito daga Imam Muhammad Bakir (a.s.) cewa wani dattijo daga kabilar Nakh'a ya ce: "Na ce wa Abu Ja'afar (a.s.) cewa: Ni na kasance gwamna ne tun zamanin Hajjaj har yau din nan, shin za a karbi tuba ta? Sai na yi shiru, sannan na sake maimaita wannan tambayar, sai yace min: "A a; har sai ka mai da wa duk wani mai hakki, hakkinsa([211]) ".

Abu Hamza al-Thumali ya ruwaito daga Imam Abu Ja'afar al-Bakir (a.s.) cewa: "Yayin da Aliyu bn Husaini (a.s.) ya zo cikawa sai ya rungume ni ya zuwa kirginsa sannan ya ce: "Ya dana, ina maka wasicci da abin da babana (a.s.) ya mini wasicci yayin da cikawa ta zo masa, kuma da abin da ya ambata cewa babansa ya yi masa wasicci. Ya ce: Ya dana, na hane ka zaluntar wanda ba shi da mai taimako kanka sai Allah Ta'ala([212]) ".

Imam Sadik (a.s.) ya ce: "Babu zaluncin da yafi zaluncin da wanda aka zaluntan ba shi da mai taimakonsa a kan shi sai Allah Mai Girma da Daukaka([213]) ".

Imam Sadik (a.s.) ya ruwaito daga kakansa Manzon Allah (s.a.w.a.) yana cewa: "Ku tsoraci zalunci domin shi duhu ne a ranar lahira([214]) ".

Imam Sadik (a.s.) ya ce: "Allah Mai Girma da Daukaka Ya yi wasicci ga wani Annabi da cikin Annabawansa wanda yake cikin masarautar wani jabbarin sarki cewa: 'Ka je wajen wannan azzalumin ka ce da shi; Ni ban shugabantar da kai domin zubar da jini da tara dukiya ba, sai dai kawai na shugabantar da kai ne domin ka raba Ni da sautin (karar) wadanda aka zalunta. Domin Ni ba zan bar zaluncin da aka yi masu ba ko da kafirai ne([215]) ".

Imam Sadik (a.s.) ya ce: "Da wanda ya aikata zalunci da mai taimakonsa da kuma wanda ya yarda da shi, to dukkansu ukun masu tarayya ne (cikin zaluncin)([216]) ".

Imam Sadik (a.s.) din dai ya ce: "Duk wanda ya yi uzuri wa zaluncin azzalumi, Allah zai dora masa wani azzalumi da zai zalunce shi, kuma idan ya yi addu'a ba za a amsa masa ba, kuma Allah ba zai ba shi ladar zaluncin da aka masa ba([217]) ".

Abu Basir ya ruwaito cewa: "Mutane biyu sun zo wajen Imam Sadik (a.s.) a kan wani lamari na mu'amala tsakaninsu. Yayin da Imam (a.s.) ya ji zancen kowannensu, sai ya ce: "Hakika wanda ya cimma bukatarsa da zalunci bai cimma kome ba. Lallai za a biya wanda aka zalunta da addinin azzalumin fiye da abin da shi ya dauka daga dukiyar wanda aka zalunta", daga nan sai ya ce: "Duk wanda yake aikata wa mutane sharri kada ya yi kyama idan aka yi masa. Hakika babu abin da dan Adam zai girba face abin da ya shuka. Babu wanda zai girbi abu mai dadi baicin ya shuka mai daci, babu kuma wanda zai girbi mai daci baicin ya shuka mai dadi". Sai mutane biyun nan suka yi sulhu kafin ma su tashi daga gare shi([218]) ".

A'imman Ahlulbaiti (a.s) sun ruwaito cewa Manzon Allah (s.a.w.a.) ya ce: "Duk wanda ya tafi tare da azzalumi domin ya taimake shi, alhalin ya san cewa shi azzalumi ne, to, hakika ya fice daga Musulunci([219]) ".

Manzon Allah (s.a.w.a.) ya ce: "Adalci na sa'a guda ya fi ibadar shekaru saba'in na sallar dararensu da azumtar yininsu. Zalunci a hukumci na sa'a guda kuma ya fi tsanani da girma wajen Allah a kan sabon shekara sittin([220]) ".

Jabir bn Abdullah al-Ansari (r.a.) ya ce: 'Manzon Allah (s.a.w.a.) ya ce: "Wanda ya nemi yardar wani sarki da abin da yake fusata Allah, to ya fita daga addinin Allah([221]) ".

Manzon Allah (s.a.w.a.) ya ce: "Wanda ya shugabanci mutum goma sannan bai yi adalci a tsakaninsu ba, zai zo ranar lahira hannayensa da kafafunsa da kansa na cikin ramin gatari([222]) ".

Imam Ali (a.s) ya ce: "Duk mutumin da ya shugabanci wani al'amari na musulmi, sannan ya rufe kofa (ya ki sauraronsu) to yana cikin azabar Allah Mai Girma da Daukaka da la'anarSa har sai ya bude kofarsa ga mai wata bukata da mai (karar) wani zalunci, sun shigo([223]) ".

Kamar haka A'imma (a.s.) suke tarbiyyar mabiyansu da karkato da ra'ayin jama'a zuwa ga canji da gyara da shiga fagen siyasa ta hanyarta ta asali.

(2). Yankewa daga Azzalumai: Bayan shiryarwa da tarbiyya kan munin zalunci, Ahlulbaiti (a.s) sun kara da umurni da yanke hulda da azzalumai, kamar yadda ya zo cikin hadisi cewa:

"Duk wanda ya yi tafiya tare da azzalumai, alhali yana sane da cewa azzaluman ne, to hakika ya fice daga Musulunci" da kuma cewa: "Mai aikata zalunci da mai taimaka masa da mai yarda da shi dukkansu masu tarayya da juna ne".

Haka nan suke kira da yanke hulda da azzalumai da rashin taimaka masu. An ruwaito cikin hadisi cewa: "Idan ranar alkiyama ta zo mai kira zai yi kira: Ina azzalumai da mataimakansu; wanda ya shirya masu kurtun tawada ko ya daure musu wata jaka ko ya fere musu kan alkalami, ku tara su tare da azzalumai([224]) ".

Kyakkyawan misalin yankewa azzalumai shi ne abin da A'imma (a.s.) suka yi da matakan da suka dauka dangane da zalunci da azzaluman mahukuntan Umayyawa da Abbasiyawa a zamanin Imam Sajad, Imam Bakir, Imam Sadik, Imam Kazim, Imam Ridha([225]) (*), Imam Jawad([226]) (**), Imam Hadi da kuma Imam Hasan Askari (a.s.).

A wannan lokacin A'imma (a.s.) sun gamu da wahalhalu daban-daban daga mahukunta, kamar cutarwa da kora da sa ido da shiga kurkuku da matsi da tsoratarwa, za mu kawo kadan daga cikin irin wadannan abubuwa a cikin wannan littafi.

A matsayin misali na irin wannan yankewa, shi ne matsayin da Imam Sadik (a.s.) ya dauka dangane da halifan Abbasiyawa Abu Ja'afar Mansur wanda ya shahara da mugun hali da zubar da jini da zalunci ga zuriyar Imam Ali (a.s.). Malaman tarihi sun rubuta cewa, wata rana Mansur ya rubuta wasika zuwa ga Imam Sadik (a.s.) yana neman zama da shi don kokarin sanya shi cikin malaman hukuma. Sai Imam yaki duk kuwa da halin tsoratarwa da kaushin halin da mahukuntan suke nunawa.

Ga abin da Mansur ya rubuta: "Me zai hana ka ziyarce mu kamar yadda mutane suke ziyartarmu"?, sai Imam (a.s.) ya rubuta masa cewa: "Babu abin da muke tsoronka dominsa, babu wani abu daga sha'anin lahira a gare ka wanda zai sa mu kaunaci (saduwa da) kai dominsa. Ba ka kuma cikin wata ni'ima ballantana mu yi maka murna, ba ma kuma ganinsa a matsayin azaba ballantana mu yi maka jaje". Sai Mansur ya rubuto amsa ya ce: "Ka zauna da mu saboda ka yi mana nasiha". Sai Imam (a.s.) ya amsa masa da cewa:"Mai nufin samun duniya ba ya maka nasiha, wanda kuwa yake nufin lahira ba ya zama da kai([227]) ". Haka nan dai matsayar A'imma (a.s.) da raddinsu ya kasance ga mahukuntan da ba sa tsai da shari'a, ba su lizimtar ginshikanta.

To haka nan ma malaman fikihun mazhabar Ahlulbaiti (a.s) suka bi tafarkin Imamansu wajen yanke hulda da azzaluman mahukunta ta hanyar fatawoyinsu masu haramta taimakawa azzalumai ko karbar aikin hukumominsu. Suna kawo wannan ne galibi a babin makasib wato hanyoyin neman abin masarufi. Bari mu kawo maganar Shahid Muhammad bn Jamal (*) Makki al-Amuli wanda aka fi sani da Shahidul Awwal (Allah Ya rahamshe shi) yayin da yake kawo sana'oi haramtattu cewa: "Da taimakon azzalumai cikin zalunci" (yana daga cikin haramtattun sana'oi), shi kuma mai sharhin littafin ya ce: "Kamar yi musu rubutu da kawo musu wanda suke zaluntarsa da dai makamantansu([228]) ".

Malaman sun hana karbar duk wani aiki a hukumar azzalumai sai dai da nufin yi wa Musulunci hidima da tunkude zalunci ga barin bayin Allah, ta yadda dai za a samu wani gyara ko wani amfani ga al'umma.

(3). Gwargwarmaya da abin da ya shafi amfani da karfi: Wajibcin umurni da aiki mai kyau da hana mummuna wani ginshiki ne wanda ya tabbatar da gwagwarmaya domin kawar da zalunci, kuma an lizimta da shi ga musulmi.

Manzon Allah (s.a.w.a.) ya ce: "Shugaban shahidai shi ne Hamza da kuma mutumin da ya mike ya umarci sarki azzalumi (da kyakkyawan aiki) ya hana shi (mummuna) sannan sarki ya kashe shi".

Duk wanda ya bibiyi tsarin rayuwar Ahlulbaiti (a.s) a fagen siyasa da sabawa zaluncin da suka yi, zai ga cewa hanya ce guda wajen sabawa zalunci da kira zuwa ga gyara da gwagwarmaya. Gwagwarmaya ta faro ne a zamanin mulkin Mu'awiyyah dan Abu Sufyan, yayin da ya dora dansa Yazid a kan wuyar al'ummar musulmi duk da cewa bai cancanci shugabanci ba kuma ya rasa dukkan sharuddansa. Wannan ta'asa ta janyo fasadi da kaucewar al'umma, abin da ya sanya Imam Husaini (a.s.) yin shelar jihadi. Imam (a.s.) ya zauna a Makka na tsawon wata hudu bayan barowarsa birnin Madina, daga bisani sai ya fuskanci kasar Iraki. Can a Karbala ne aka yi gumurzu tsakanin rundunar Yazid da jama'ar Imam Husaini (a.s.) 'yan kalilan, a can tsarkakken jini ya zuba, Imam (a.s.) ya yi shahada. Zubar da jinin Imam Husaini (a.s.) tare da Ahlulbaitinsa da kuma mabiyansa ya girgiza al'umma ya tashe ta daga barcin da take ciki. Wannan kuwa shi ne farkon tawaye wa azzaluman mahukunta masu fakewa da Musulunci don cimma burinsu da warware mubaya'ar jabu da shelar kawar da hukumcin bata-gari mai sabawa rukunan Musulunci. Wannan tawaye wa azzalumai shi ya yaye zanin malaman da suke kiran mutane zuwa kaskanci da mika kai bori ya hau, da gurbata ra'ayin ilahirin jama'a da karfafa cewa sai an lizimci mubaya'ar azzalumi an cika masa alkawari komin lalacewarsa. Wadannan muggan malamai dangin Bal'ama dan Ba'ura sun yi kunnen uwar shegu da fadar Manzon Allah (s.a.w.a.) ce wa: "Ba a karbar rantsuwar mai sabo", Da kuma fadinsa (s.a.w.a) cewa: "Babu biyayya ga halitta cikin sabon Mahalicci".

Suna yin biris da fadin Allah Ta'ala cewa: "Kuma kada ku karkata zuwa ga wadanda suka yi zalunci, sai wuta ta shafe ku". (Surar Hud, 11:113).

Shi Shugaban shahidai, Imam Husaini bn Ali (a.s.) ya kaddamar da gwagwarmayarsa ne a shekara ta sittin da daya bayan hijira, kuma a wannan shekarar ne ya yi shahada a can yankin Karbala na kasar Iraki. Da wannan ne kuma ya rushe dukkan kiraye-kirayen muggan malamai na rauni gaban hukumomin zalunci da yarda da su. Hakika sautin shahada da jini ya rinjayi na kwadayi da kaskanci.

Imam Husaini (a.s.) ya bayyana wa mutane dalilan fitowarsa da tsarin da yake tafe bisansa da cewa:

"Ni ban fito domin girman kai ko alfahari ba, ba kuma domin barna a bayan kasa ko zalunci ba. Abin da kawai ya fito da ni shi ne neman gyara a cikin al'ummar kakana, Manzon Allah (s.a.w.a.). Ina nufin yin umurni da kyakkyawan aiki da hana mummuna, in kuma bi irin rayuwar kakana da babana([229]) ".

Sannan ya ayyana wa mutane siffofin shugaba wanda shi ne ja-gora mai jan ragamar musulmi, da wajibcin tsayuwa don gwagwarmayar sauya mai hukumci a yayin da ya karkace ya bar wadannan ginshikin. Ga abin da Imam Husaini (a.s.) ya rubuta wa mutanen Kufa:

"Ina rantsuwa da cewa ba wani ne shugaba ba face mai hukumcin da ya tsayar da adalci, mai riko da addinin gaskiya, mai tsare kansa bisa (umurnin) Zatin Allah([230]) ".

Daga cikin abin da ya rubuta wa manyan mutanen garin Basra kuwa, cewa ya yi: "Ni ina kiranku zuwa ga Littafin Allah da Sunnar AnnabiSa (s.a.w.a), domin an riga an kashe sunna an raya bidi'a. To idan kun saurari fadina kuka bi umurnina zan shiryar da ku tafarkin shiriya. Aminci ya tabbata a gare ku da rahamar Allah([231]) ".

Hakan nan Imam Husaini (a.s.) ya tabbatar wa al'umma yadda shari'a ta yi umarni da sabawa azzalumin shugaba, ya kuma yi shelar rukunan jihadi mai tsarki, domin sauya hukumcin azzalumai.

Bayan jihadin Imam Husaini (a.s.) mai albarka, Ahlulbaiti (a.s) sun taimaka wa yunkuri daban-daban da Alawiyyawa suka yi tsawon sama da karni biyu, a fadin kasashen musulmi.

Zaid bn Ali bn Husaini, wato dan Imam Zainul Abidin kuma jikan Imam Husaini (a.s.) ya yi yunkuri a shekara ta 121 bayan hijira. Wannan kuwa ya faru ne a zamanin Imam Sadik (a.s.) wanda kuwa ya goyi bayansa ya kuma yi juyayin shahadar Zaid (*).

Fudhail Rassan ya ce: "Na shigo wajen Abu Abdullah (a.s.) bayan an kashe Zaid bn Ali, sai aka shigar da ni cikin uwar daki, sai ya ce da ni: "Ya kai Fudhail, an kashe baffana? Sai na ce 'fansar ka nake (e an yi haka), sai ya ce:"Allah Ya jikansa, lallai shi ya kasance mumini mai sani, mai ilmi, mai yawan gaskiya. Lallai da ya yi nasara da ya cika alkawari. Lallai da ya sami mulki da ya san inda zai sanya shi([232]) ". Haka aka yi ta samun taimakawar Ahlulbaiti (a.s) wa masu yunkurin kawo gyara cikin Alawiyyawa.

Daya daga cikin bayyanannen misalin irin wannan mataki na siyasa kuwa, shi ne matakin da Imam Kazim (a.s.) ya nuna dangane da yunkurin da Husaini bn Ali ya yi a shekara ta 169 a birnin Madina, yunkurin da aka fi sani da Yunkurin Fakh([233]) (*) wanda aka yi shi a watan Zulkida na wannan shekarar.

Duk da cewa Imam Kazim (a.s.) ya ga alamun rashin nasarar yunkurin a wancan lokacin, babu shakka magan-ganun da ya yi sun nuna cewa yana goyon bayan ra'ayin jihadi. Ga abin da ya fadi wa shi Husainin yayin da ya ga yayi niyyar fita wannan arangama:

"Za a kashe ka, saboda haka ka tsananta yaki domin mutanen fasikai ne, suna bayyana imani suna boye munafunci da shirka. Lalle ne mu daga Allah muke kuma wajenSa za mu koma! Ga Allah nake neman ladan rashinku([234]) ".

Yayin da Husain ya yi shahada aka kawo kawukan wadanda suka yi shahada tare da shi wajen mahukuntan Abbasiyawa, sai aka tambayi Imam Kazim cewa wannan kan Husaini ne? sai ya ce:

"E, lalle ne mu ga Allah muke, kuma lalle ne mu zuwa gare Shi za mu koma. Na rantse da Allah, ya mutu musulmi ne salihi, mai yawan azumi, mai umurni da kyakkyawa, mai kuma hana mummuna, babu tamkarsa cikin mutanen gidansa([235]) ".

Shi dai Husain ya kasance ne yana kiran mutane da cewa: "Ina kiranku ne zuwa ga abin da Alu Muhammadu suka yarda da shi, da aiki da Littafin Allah da sunnar Annabi (s.a.w.a) a tsakaninku, da kuma tsayar da adalci a tsakanin jama'a([236]) ". Kiran da Husain ya yi, kira ne zuwa ga biyayya ga mutumin da ya cancanci shugabanci, wanda yake daga Alu Muhammadu, kuma shi ne Imam Kazim (a.s.), kamar yadda Zaid ya yi nufin mai da shugabanci ga Imam Sadik (a.s.) da ya yi nasara. Hakika halifan Abbasiyawa ya fahimci goyon bayan da Imam Kazim (a.s.) yake yi wa yunkurin Husain a yakin Fakh.

Allamah Majilisi ya ruwaito cewa: "Sai ya (halifan Abbasiyawa) ci gaba da zagin Dalibiyawa (jikokin Ali bn Abi Talib) har ya ambaci Musa bn Ja'afar (a.s.), sai ya zage shi yana cewa: 'Wallahi Husaini bai yunkura ba sai da umarninsa (Musa bn Ja'afar), ba abin da ya bi face abin da yake so domin shi (Imam Kazim) ne ma'abucin wasiyya a cikin mutanen wannan gidan. Idan na bar shi, Allah Ya kashe ni([237]) ".

Imam Jawad, jikan Imam Kazim (a.s.) shi ma ya bayyana tasa matsayar dangane da masu gwagwarmar, inda ya ce: "Bayan Dif (Karbala), ba a cutar da mu kamar cutarwar Fakh ba([238]) ".

Akwai misalai masu yawa na yunkuri da goyon bayan Ahlulbaiti (a.s) gare su, har wannan (yunkurin) ya zama tafarki da salo na aikin siyasa wanda yake da goyon bayan shari'a.

(4). Gwagwarmaya ta Siyasa: Wannan yana da muhimmancin gaske a rayuwar siyasar al'umma a duk lokacin da azzalumin shugaba ya bayyana ba ya gudanar da hukumce-hukumcen Allah Ta'ala, ba ya kuma tsaifa adalci a tsakanin mutane. Kowane Imami na Ahlulbaiti (a.s) ya shugabanci al'umma a fagen siyasa a zamaninsa, kuma ya kasance shi ne alamar bijirewa azzalumai a zukatan jama'ar musulmi. Wannan kuwa shi ne ya bai wa yunkure-yunkuren da aka yi siffar dacewa da shari'a. Halifofin Banu Umayya da Banu Abbas wadanda tarihi ya yi wa shaidar rashin lizimtar addini da barin adalci sun san irin kimar Ahlulbaiti (a.s) a zukatan musulmi, saboda haka suka bi hanyoyi daban-daban domin su nisantar da kaunar Ahlulbaiti (a.s) daga mutane, hanyoyi kamar su tsoratarwa da kai su kurkuku da kisa da rashawa da mukamai da sauransu. A matsayin misali, Mu'awiyya ya yi tawaye ga Imam Ali (a.s.) ya yake shi duk da cewa shi ne halaltaccen halifa.

Baya ga haka kuma, bai tsaya ba sai da ya yaki Imam Hasan (a.s.) ya yi tawaye wa halifancinsa, ya kashe shi da guba a shekara ta hamsin, bayan hijira. Yazid dan Mu'awiyya, shi ma ya dauki mataki irin na ubansa akan Imam Husain (a.s.), ya kashe shi tare da mutanen gidansa, ya ribaci zuriyar Manzon Allah (s.a.w.a.) yayin da Imam Husaini (a.s.) ya jagoranci yunkurin bijirewa hukumar Banu Umayya ta zalunci da aka tilasta ta a kan al'umman musulmi.

Bayan Imam Husaini (a.s.) ya yi shahada, musulmi sun karkata hankalinsu ga Imam Ali bn Husain, Zainul Abidin (a.s.), suna ganinsa a matsayin wata alama kana kuma makoma gare su, don haka ne masu yunkuri

Gwagwarmaya suke neman izininsa. Don haka ne ma a zamaninsa an sami masu jihadi domin kare Ahlulbaiti (a.s) da yawa, kamar yunkurin Madina da Makka da na Mukhtar Al-Thakafi da na Tawwabun, dukkansu suna yaki domin daukar fansa kan wadanda suka kashe Imam Husaini (a.s.). A wancan lokacin mutane suna ganin Imam Zainul Abidin a matsayin kololuwar bijirewa azzalumai duk da cewa bai motsa ba. Matsayin da ya dauka kan Yazid bn Mu'awiyya da Marwan bn Hakam da Abdul Malik bn Marwan da sauran azzaluman mahukunta, matsayi ne na mai bijirewa a asirce da taimakon masu yunkuri ba tare da shelar hakan ba. har ma Imam (a.s.) ya roki rahamar Allah ga Mukhtar, wanda ya dauki fansa kan wadanda suka kashe Imam Husaini (a.s.) ya kuma yaba da jihadin Mukhtar. Sannan kuma Imam (a.s.) ya yi amfani da makamin addu'a([239]) (*) mai bayyana irin ra'ayinsa na siyasa da akida, mai sabawa da ra'ayin su Yazid.

Imam Bakir (a.s.) dan Imam Zainul Abidin (a.s.) shi ma ya nuna matsayin da yake kai na bijirewar siyasa daga Banu Umayya. Imam ya sha wahala kwarai a hannunsu, musamman ma Hisham bn Abdul Malik mai bayyana kiyayya da gaba ga Alawiyyawa. A zamaninsa ne Zaid bn Ali dan uwan Imam Bakir (a.s.) ya fito jihadi.

Shi dai wannan halifa na Banu Umayya ya tabbatar cewa tushen wannan yunkuri na Zaid daga Imam Bakir da dansa Ja'afar Sadik (a.s.) yake. Don haka sai ya kira su daga Madina zuwa ga helkwatarsa da ke Sham, yayin da Imam Bakir (a.s.) ya shiga fadar Hisham sai ya yi sallama yana nuni zuwa ga mahalarta majalisar, amma bai yi gaisuwar sarauta ga halifan ba. Sai Imam ya zauna ba tare da da wani izinin sarki ba, hakan ya kara wa Hisham kiyayyarsa ga Imam har ma ya kama sukansa da cewa:

"Ya Muhammad bn Ali, ko yaushe sai an sami wani mutum daga cikinku yana raba kan musulmi, da kiran jama'a don su bi shi, domin wauta da karancin ilmi".

Sai Hisham ya ci gaba da suka, jama'ar da ke fada su ma suka fara sukar Imam din bayan Hisham ya yi shiru. Da ganin wannan ka san cewa an umurce su da hakan ne kafin ma Imam din ya shigo tare da dansa, Imam Sadik (a.s.). Ganin haka ke da wuya, sai Imam Bakir (a.s.) ya mike tsakiyar majalisar yana mai raddi ga sarki da cewa:

"Ya ku mutane! Ina kuke zuwa ne? Ina aka nufa da ku ne? Da mu Allah Ya shiryar da farkonku, da mu kuma Zai cika (shiryar) da na karshenku. Idan kuna da mulki abin gaggautarwa, to mu muna da mulki da aka jikirta, kuma babu wani mulki bayan namu, domin mu ne masu mulkin karshe".

Allah Madaukakin Sarki Yana cewa: "Kuma kyakkyawan karshe tana tabbata ga masu tsoron Allah". (Surar A'araf, 7: 128). Jin haka, ya sa Hisham ya tsare shi([240]) .

To a cikin kurkukun ma Imam Bakir (a.s.) bai yi shiru ba, ya wayar da kan fursunoni kan batutuwan siyasa da jihadi har fursunonin suka sami tasirin wa'azinsa, inda suka tayar da hargowa a cikin kurkukun. Ganin haka, sai shugaban kurkukun ya isar da lamarin zuwa ga Hisham, inda shi kuma ya yi umarni da a fitar da Imam (a.s.) daga kurkukun a mai da shi birnin Madina, a hannun wani dan aiken sarki([241]) .

Muhammad bn Jarir Tabari ya rubuta cewa dalilin da ya sa aka mai da Imam Bakir (a.s.) zuwa Madina shi ne bazuwar tasirinsa kan tunanin mutanen Sham sakamakon wata muhawara da ta gudana tsakaninsa da wani shugaban kiristoci([242]) .

A wata muhawara da ta gudana tsakanin Hisham bn Abdul Malik da Zaid, a lokacin da labarin yunkurin Zaid din ya isa kunnen Hisham, Hisham ya ce da Zaid: "Na sami labarin kana ambaton halifanci kuma kana burinsa, alhali kai ba ka cikin mazowansa, kuma kai dan baiwa ne".

Sai Zaid ya mayar masa da martani da cewa, Annabi Isma'il dan baiwa ne kuma Allah Ta'ala Ya ba shi annabta. Sannan Hisham ya dora ambaton Imam (a.s.) da zagi, yana mai tambayan Zaid da cewa:

"Dan'uwanka Bakara kuwa...", sai Zaid ya amsa masa da cewa: "Manzon Allah (s.a.w.a.) ya ambace shi da Al-Bakir([243]) (*) kai kuma ka kira shi da Bakara (wato saniya), lalle sabaninka da Manzon Allah (s.a.w.a.) ya yi yawa kuma za ka saba da shi a ranar lahira kamar yadda ka saba da shi a nan duniya, domin Annabi (s.a.w.a) zai shiga aljanna kai kuwa za ka shiga wuta". To wannan shi ne matakin da Imam Bakir (a.s.) ya dauka da kuma yunkurinsa na siyasa, har lokacin da ya yi shahada.

To daga nan sai zamanin dansa Imam Ja'afar Sadik (a.s.), a wannan lokaci na Imam Sadik (a.s.) kuwa bala'i ya yawaita kan al'ummar Annabi (s.a.w.a), ya kuma fi tsanani kan Alayensa (s.a.w.a). Imam Sadik (a.s.) ya kasance shi ne jagoran bijirewa azzalumai ta hanyar siyasa duk da yake bai yi magana bayyananniya kan masu iko ba. Masu yunkuri suna neman shawararsa da goyon bayansa, kai har da neman ya karbi jagorancin harkar, kamar yadda Abu Muslim Khorasani ya bukata yayin da ya mika mubaya'arsa ga Imam. Imam Sadik (a.s.) ya ki karbar wannan mubaya'a saboda rashin cikar sharudda da kasantuwar yanayi bai dace ba, kamar dai yadda ya yi lokacin yunkurin Zaid a zamanin Hisham bn Abdul Malik Ba'umayye.

Abul Abbas Saffah ya yi kokarin kashe Imam domin saninsa da mukaminsa na jagoranci da goyon bayansa ga bijirewa mahukunta. To amma Allah Ya kare shi daga sharrinsa, duk kuwa da cewa ya taba kiran Imam din daga Madina zuwa garin Hira da ke kasar Iraki, inda ya tsananta masa da kuma sanya shi karkashin 'yan leken asiri.

Yayin da Abu Ja'afar Mansur ya gaji Al-Saffah, shi ma ya ji tsoron matsayin Imam Sadik (a.s.) kamar yadda magabatansa suka ji, sau da yawa ya kan kira Imam (a.s.) daga Madina zuwa Iraki.

Ga yadda yake siffanta karfin Imam a fagen siyasa da tasirinsa kan masu gwagwarmaya, inda ya ke cewa: "Wannan bakin cikin (yana nufin Imam Sadik) da rike makoshin halifofi, korarsa ba ta halalta, kisan sa ba ya halalta. Ba don mun hadu da shi a bishiya mai kyakkyawan tushe, mai rassan da suka gabata, mai dadadan 'ya'ya, an kuma albarkaci zuriyarta aka tsarkake ta cikin Littattafai ba, da an sanya shi cikin mummunan karshe, saboda labarin da muka samu na tsananin aibantamu da mummunan magana da yake fada game da mu([244]) ". Wannan shi ne matsayin Imam Sadik (a.s.) da aikin da ya yi na bijirewa azzaluman mahukunta, da goyon bayan masu yunkurin kawo gyara.

Daga nan sai zamanin Imam Musa bn Ja'afar Kazim (a.s), dan Imam Sadik (a.s.), a lokacinsa cutar da musulmi da karkata addini da kwadaitar da mutane da dukiya sun tsananta a hannun Abbasiyawa. Don haka ne Imam (a.s.) ya kasance jogora wajen gyaran al'amarin Musulunci.

An sanya Imam (a.s.) karkashin leken asiri a zamanin Mansur wanda shi ya kai matuka wajen zaluntar Alawiyyawa da kwace dukiyoyinsu, da gina turakun gadoji da kadarkai da soraye a kansu da ransu, da azabtar da su cikin kurkuku.

To amma bayan da Muhammad Al-Mahdi ya gaji sarautar Abbasiyyawa sai tsoransa ga Imam Kazim ya yi tsanani, don haka sai ya kirayi Imam (a.s.) daga Madina zuwa Bagadaza domin ya hukunta shi. Al-Mahdi ya sa aka rufe Imam Kazim (a.s.) a kurkuku har zuwa wata rana da halifan ya ga Imam Ali bn Abi Talib (a.s.) a mafarko yana ce da shi: "To, shin, kuna fatan idan kun juya za ku yi barna a cikin kasa, kuma ku yanyanke zumuntarku?" (Surar Muhammadu, 47: 22). Wannan sai ya tsoratar da Mahdi ya fitar da Imam Kazim (a.s.) daga kurkuku.

A mulkin Al-Hadi, sarkin Abbasiyawa, ne bala'i ya tsananta kan Imam (a.s.) da kuma Alu Ali (a.s.). Ya ci gaba da korarsu da kashe su da neman batar da su gaba daya musamman ma bayan yunkurin Husain bn Ali wanda aka fi sani da waki'ar Fakh. Imam Kazim (a.s.) ya gamu da tsanantarwa da matsarwa har sai da ta kai Al-Hadi din ya hukumta Imam (a.s.) da hukumcin kisa ya kuma tasanma aiwatar da hakan. Malaman tarihi sun ruwaito cewa alkali Abu Yusuf almajirin Imam Abu Hanifa shi ne ya shiga tsakanin Al-Hadi da wannan kuduri da ya dauka na kashe Imam Kazim (a.s.), don Al-Hadin ya zaku kan kashe Imam (a.s.) har cewa ya yi: "Allah ya kashe ni idan na yi wa Musa ibn Ja'afar afuwa".

Daga nan sai Al-Hadi ya sanya Imam Kazim (a.s.) a kurkuku da hana shi damar gudanar da aikinsa na ilmantarwa da jagoranci a bayyane. Amma mutuwa ba ta bar shi ya aikata mummunan nufinsa, don kuwa ta kawo karshen wannan azzalumi jabberi.

Daga nan sai lokacin Haruna Rashid wanda aka sami jayayya mai tsananin gaske tsakaninsa da Imam Kazim (a.s.). Haruna Rashid ya yi kiran Imam da ya taho daga birnin Madina zuwa Iraki, inda ya ci gaba da tozarta shi da sanya shi a kurkuku da azabtarwa nau'i daban-daban, wadanda suka hada da daure shi da karfe yana daukansa daga wannan kurkukun zuwa wancan. Imam (a.s.) ya zauna a kurkuku tsawon shekaru, daga karshe Haruna Rashid ya ci da shi guba ta hannun shugaban dogarawan-sa mai suna Al-Sandi bn Shahik. Imam (a.s.) ya yi shaha-da ne a ranar 25 ga watan Rajab a shekara ta 183 bayan hijira.

Daga nan sai zamanin Imam Ridha, Aliyu bn Musa bn Ja'afar (a.s.), wanda shugabancinsa na siyasa ya wajabtawa Abbasiyawa la'akari da shi a sakamakon karfin alkadarin Imam (a.s.) da kaunar al'umma gare shi ga kuma tsanantar bijirewa ga Abbasiyawa. Wannan yanayi ya tilastawa halifan Abbasiyawa Ma'amun sanya Imam (a.s.) a matsayin magajinsa. Imam Ridha (a.s.) ya karbi wannan matsayi ba don sonsa ba, kana kuma da sharadin cewa shi ba zai shiga harkokin shugabanci ba, sannan idan Ma'amun ya mutu, halifanci zai koma hannunsa. To amma Imam Ridha (a.s.) ya yi shahada yayin da Ma'amun ya ba shi guba a shekara ta dari biyu da uku bayan hijira.

To bayan shahadar Imam Ridha (a.s.), wanda ya karbi jagoranci al'umma da lamarin Imamanci shi ne dansa Imam Muhammad Jawad (a.s.) wanda ya yi zamani da Ma'amun na dan lokaci. Ma'amun ya yi mu'amala da shi da girmamawa a munafunce, ya aurar masa da 'yarsa Ummul Fadhl domin ya sami soyayyar al'umma, yayi hakan ne kuwa domin ya juya hankulan mutane ya karkata ra'ayin masu gaba da shi, wadanda suke ganin Imam (a.s.) a matsayin jagora. Sai dai fa Ma'amun bai tsinana komai ba domin Imam Jawad (a.s.) ya bar Bagadaza ya koma birnin Kakansa Manzon Allah (s.a.w.a.) saboda ci gaba da aikinsa na ilmantarwa da jagorancin al'umma a can.

To bayan da Ma'amun ya mutu sai dansa Al-Mutasim ya hau karagar mulkin Abbasiyawa, sai dai kuma shi Al-Mutasim bai jima a kan mulkin ba, to amma dai shi ma ya kasance yana jin tsoron Imam Jawad (a.s.) da kuma hadarin zamansa a Madina. To shi ma Al-Mutasim bai yi wata-wata ba sai ya kama tafarkin iyayensa yayin da ya dauko Imam daga Madina ya kawo shi helkwatarsa domin ya sanya ido a kansa. Marubuta tarihi sun ce Imam Jawad (a.s.) ya yi shahada ne a hannun Mutasim ta hanyar guban da ya sa masa cikin abinci a shekarar da ya kawo shi Bagadaza a lokacin kuwa hijira tana da shekara dari biyu da ashirin da biyar.

To bayan shahadar Imam Jawad (a.s.) dansa Imam Ali Hadi shi ne ya gaji jagorancin al'umma da Imamanci daga mahaifin nasa. A zamanin Mutawakkil Abbasi ne Imam Hadi (a.s.) ya fuskanci keta da cutarwar Abbasiya-wa. Mutawakkil da ma sananne ne da son wasa da kuma gaba da Alayen Manzon Allah (s.a.w.a.) da kashe su da korar su da yanke abincinsu da hana mutane taimakonsu. Imam Hadi (a.s.) ya kasance yana tsorata halifa Mutawakkil saboda haka sai ya dauko shi daga Madina ya kai shi garin Samarra ya sa ido sosai a kansa, ya kuma tilasta masa zama a can. To lokacin da al'amurra suka yi zafi wa Mutawakkil, sai ya fara barazanar kisa ga Imam Hadi (a.s.) baya ga daure shi da ya sha yi. A wasu lokuta ya kan sa a binciki gidan Imam Hadi (a.s.) da kai hari wa gidan, bugu da kari kan tsananta sanya ido a kansa saboda tsoron irin tasirin da Imam (a.s.) yake da shi a idon al'umma.

Marubuta tarihi sun ambaci dalilan da suka sa Mutawakkil ya ta da Imam Hadi (a.s.) daga Madina. Sibt Al-Jawziyya ya ce: "Malaman tarihi sun ce: Ya fito da shi daga Madinar Manzon Allah (s.a.w.a.) zuwa Bagadaza ne don yana tsananin kin Aliyu da zuriyarsa sai kuma ya sami labarin irin matsayin Aliyu Hadi a Madina da karkatar mutane zuwa gare shi. Wannan ya sa shi tsoronsa([245]) ".

Bayan shahadar Imam Hadi (a.s.) garin Samarra a shekara ta 254 bayan hijira, sai dansa Imam Abu Muhammad Hasan Askari (a.s.) ya kasance Imami mai kula da harkar al'umma da kuma shiryar da su. To shi ma dai matsayinsa kan Abbasiyawa tamkar na iyayensa ne, wajen fito-na-fito a fagen siyasa. To shi ma dai mahu-kumtan ba su bar shi don kuwa sun cutar da shi kamar yadda suka cutar da mahaifansa. Al-Muhtadi bn Al-Wasik sarkin Abbasiyawa ya sanya shi a kurkuku a garin Samarra, inda ya mika shi ga hannun gandurobobin kurkukun wadanda suka shahara da mugun hali da zalunci don azabtar da shi, amma Imam (a.s.) ya yi tasiri kansu har suka shiryu suka zamo mutanen kwarai.

Malaman tarihi sun kiyaye abubuwan da suka sami Imam Hasan Askari (a.s.) na matsanancin bala'i, kamar abin da Ahmad bn Muhammad ya ruwaito, inda ya ce:

"Yayin da Al-Muhtadi da fara kashe magoya bayan Ahlulbaiti (a.s) sai na rubuta wa Abu Muhammad Hasan Askari (a.s.) na ce masa: Ya shugabana, godiya ta tabbata ga Allah Wanda Ya shagaltar da shi (Muhtadi) daga barinka. Hakika na sami labari cewa yana maka barazana da cewa: "Wallahi sai na kore su daga duk sababbin kasashe", sai Abu Muhammad (a.s.) ya rubuta da hannunsa cewa: "Wannan shi zai takaita rayuwarsa([246]) ".

An ruwaito cewa, Imam Askari (a.s.) ya kasance cikin kurkuku a zamanin Al-Mutamad har lokacin da ya kira shi don warware wata matsala da ta faru tsakanin musulmi da wani malamin Nasara, a kan shayarwa (ruwan sama). Sai Imam (a.s.) ya warware ta, to a saboda haka Al-Mutamad ya fito da shi daga kurkukun kuma ya nemi a saki mabiyansa da ke tare da shi a kurkuku, hakan kuwa aka yi, wato a ka sake su.

Wannan shi ne kadan daga tarihin Ahlulbaiti (a.s) a fagen siyasa da fito-na-fiton da suka yi da hukumomin zalunci na lokacinsu wadanda suka doru a kan al'umma. Idan an duba da kyau za a ga cewa, silsilar Imamai goma sha daya mai albarka ta Ahlulbaiti (a.s) ta kasance wani fage ne na jagorantar al'umma da kuma shiryar da su. Don kuwa kowane Imami za a ga shi ne jagorar al'um-mar da ya kasance a cikinta, wanda kuma ya fi kowa ilmi da sanin ya kamata. Irin wannan tsari ba zai yiyu a same shi ba sai da shiri gabatacce daga Allah Ta'ala. Kuma babu makawa wannan bibiya ta jagorancin Ahlulbaiti (a.s) yana sanar da mu mukaminsu da fagensu na shugabancin akida da siyasa a rayuwar wannan al'umma.

Dubi Cikin Mazhabobin Fikihu

A zamanin Manzon Allah (s.a.w.a.) musulmi suna samun hukumce-hukumce da dokoki masu tsara al'amurransu na zamantakewa da ibada, kamar su salla, rabon gado, zaman iyali, kasuwanci, jihadi, aikin hajji da abin da ya shafi kasa da filaye da shari'u da sauransu ne kai tsaye daga Annabi (s.a.w.a), domin shi ne mai isar da sako, mai kira zuwa ga shiriya ta hanyar wahayi.

Bayan da ya koma ga Ubangijinsa Mahalicci, al'ummar musulmi sun koma ga Littafin Allah da Sunnar Ma'aiki (s.a.w.a.), suna daukar dokoki da sanin ra'ayin shari'a kan dukkan abubuwan da suka shafe su ta hanyar sahabbai da Ahlulbaiti (a.s), wadanda suka kiyaye Sunna da kuma Littafin Allah. Daga nan al'ummar musulmi ta sami ci gaba cikin salon rayuwa, saboda faruwar sabbin abubuwa cikin rayuwar mutane. Babu shakka wadannan sabbin abubuwa suna bukatar hukumcin Musulunci da sanin dokokin shari'a domin daidaitasu. Wannan fadada-wa cikin shari'a ya fara samuwa kusan a karshen karnin farko a zamanin Imam Muhammad Bakir (a.s.), wanda shi ne malamin Madina, kuma mokamar dukkan malaman zamaninsa. Malaman tarihi da na fikihu sun ruwaito cewa saboda hakan ne ma ake kiransa da Al-Bakir, domin fadadawarsa wajen ilmomi da yada su. A zamanin dansa Imam Ja'afar Sadik (a.s.) ne fannonin ilmi da fikihu da shari'a suka yi fure, yayin da shugabannin mazhabobi suka yi karatu a wajen Imam Sadik (a.s.) din. Da shi babansa Imam Bakir (a.s.) sun kasance masu ruwaito Sunna ne da kuma bayanin abin da Littafin Allah da sunnar suka kunsa, ba wai masu ijtihadi ba ne su.

A zamanin Imam Sadik ne aka fara samun mazhabobin fikihu kamar masu bin ra'ayi da kiyasi, wato mazhabar Imam Abu Hanifa, wanda ya yi karatu na wani lokacin a wajen Imam Sadik (a.s.) da sauran mazhabobi, wadanda daga baya suka takaitu cikin mazhabobi guda hudu, wato: Mazhabobin Malikiyya, Hannifiyya, Shafi'iyya da kuma Hambaliyya. Wadanda su ma wadannan mazhabobi sun rarrabu a tsakaninsu a wajen tafarkin Ijtihadi da yarda da wata ruwaya, a gefe guda kuma ga mazhabar nassi wacce Imam Sadik (a.s.) yake jagoranta, wacce ta dogara da Littafin Allah da Sunnar Annabi (s.a.w.a) wajen fitar da hukumce-hukumcen Musulunci, sannan kuma take watsi da ra'ayi da kiyasi. A daidai lokacin da kuma sauran mazhabobin suka sanya wasu hanyoyi da gano shari'a bayan Littafin Allah da Sunna, kamar su:

1. Kiyasi.

2. Istihsan (ganin dacewar ko kyaun abu)

3. Masalihul Mursala (maslahar al'amari)

4. Fathul Zara'i'i wa sadduha (bude kofar hanzari da rufe ta)

Mazhabobin Ahlussunnan nan guda hudu, Hanafiyya, Malikiyya, Hambaliyya da Shafi'iyya sun sassaba kan karbar wadannan hujjoji, ba su hadu gaba daya akansu ba. Za ka ga wasunsu suna tabbatar da wannan su yi watsi da wancan daga cikin hujjojin (hanyoyin samun hukumci).

A dalilin sassabawa wajen dauka ko watsi da wasu hujjoji mazhabobin fikihu guda hudun nan suka sami sabani tsakaninsu kuma suka saba da mazhabar nassi wacce A'imman Ahlulbaiti (a.s) suke jagoranta. Kuma a dalilin hakan ne mazhabobin nan biyar suka sassaba ka bayanan hukumce-hukumcen filla-filla. Wannan sabanin yana komawa ne ga abubuwa na tushe guda biyu, su ne:

1. Rikon wasu hujjojin (na fitar da hukumcin shari'a) daban tare da Alkur'ani da Sunna da sashen mazhabobin suka yi da kuma rashin riko da su a wajen wani sashen.

2. Sassabawa wajen karbar sashen ruwayoyi (hadisai) ko watsi da su domin dogaro da sharuddan karbar hadisi da gaskata sashen maruwaita ko a'a.

A sarari yake cewa sabanin da ke tsakanin mazha-bobin Musulunci, sabani ne na ilmi wanda bai kamata ya raba musulmi ba, ko ya nisanta tsakaninsu. Domin abin lura shi ne ana iya magance irin wannan sassabawa ta hanyar muhawara da bincike mai tsabta wanda babu son zuciya ciki. Wajibi ne irin wannan bincike a yi shi karkashin ginshikin ilimi yardaddu ga dukkan musulmi, tare da bude kofar ijtihadi wacce take rufe a wurin wasu mazhabobi. Yana da muhimmanci a gane cewa wannan sabani ba tsakanin Sunna da Shi'a yake ba, sai dai ya wanzu ne tsakanin mazhabobin fikihu kamar guda shida: Hanafiyya, Malikiyya, Shafi'iyya, Hambaliyya, Ja'afariyya da Zaidiyya, a kara kuma da ra'ayoyi da ijtihadin sashin malaman fikihu ko cikin wadannan mazhabobi ambatattu ko waje da su.

Yayin da aka bude kofar ijtihadi wa dukkan sassan musulmi, malaman fikihu kuma suka karbi aikinsu da aka sansu da shi, to za a iya iyakance ginshikan istinbadi (tsamo hukumci daga Alkur'ani da hadisi ko dai wani tushe na shari'a) da ayyana ko mene ne mabubbugan shari'a da kuma hanyar ciro hukumce-hukumce daga mabubbugar nan na tushe (wato Alkur'ani da Sunna). Domin ta hanyar komawa garesu su biyun da kokkofin ruwayoyi da hadisai da zubar da wadanda ba su inganta ba daga cikinsu, ba tare da son kai ko karkata ga wani ra'ayi ba, to musulmi za su iya yin watsi da mafi yawan sabanin da yake tsakaninsu, kuma za su iya gane abin da yake shi ne dai-dai, kuma su iya hade kansu waje guda. Duk da haka, irin ra'ayoyi da mahanga na ilmi da malaman fikihu suke da su za su wanzu, kamar yadda yake tsakanin malaman fikihu na ko wacce mazhaba ta Musulunci, kuma wannan wata dabi'a ce ta ilimi a duk wani fagen ilmi da ka sani a rayuwar dan'Adam. Saboda ba makawa a sami ra'ayoyin malamai a fagen ijtihadi da istinbadi domin malaman fikihu ba za su iya gano ainihin hukumce-hukumcen Ubangiji dukkansu gaba daya ba. Dole a samu mujtahidi (mai yin ijtihadi) yana dacewa yana kuskure kuma shi abin yi wa uzuri ne da kuma sakantawa da lada matukar ya yi bincikensa bisa tushen ilmi da ingantacciyar hanya ta shari'a.

Ga wasu misalan yadda ra'ayoyin malaman fikihu suke dacewa ko sassabawa, ba kuma tare da la'akari da ko daga Shi'a ko Sunna suke ba:

Imamiyya da Hambaliyya sun ce: Tahiyar farko wajiba ce a salla, amma Hanafiyya da shafi'iyya da Malikiyya sun ce mustahabi take ba wajiba ba. Amma tahiya ta karshe kuwa wajiba ce a ganin Shafi'iyya da Imamiyya da Hambaliyya, amma Malikiyya da Hanafiyya sun ce mustahabi ce .

Batun sallama kuwa, Shafi'awa da Malikawa da Hanbalawa sun ce wajiba ce, Hanafawa kuma suka ce ba wajiba ba ce. To amma Imamiyya kuma sun saba, wasu suna cewa wajiba ce, saura kuwa suka ce mustahabi ce. Daga cikin masu cewa mustahabi ce kawai har da Shaikh Mufid, Shaikh Tusi da Allama Hilli([247]) .

Dangane da sallar jam'i kuwa, Hanbalawa sun ce wajiba ce, wajibcin kuwa kan kowane mukallafi ne idan har zai iya, amma idan ya bar jam'i ya yi salla shi kadai, to ya yi zunubi, amma sallar tasa ta inganta. Imamiyya da Hanafiyya da Malikiyya da mafiya yawa cikin Shafi'awa sun ce ba ta wajaba wajibci na aini (wanda dole kowa ya yi) ko ma na kifaya (wanda wani yake dauke wa wani) ba, sai dai mustahabi ce mai karfi.

Kan cancantar zakka kuwa, shafi'awa da Hanbalawa sun tafi a kana cewa wanda ya mallaki rabin abin da zai ishe shi, ba a sa shi cikin fakirai, ba ya halalta a ba shi zakka. Imamiyya da Malikiyya suka ce fakiri a shar'ance shi ne wanda bai mallaki abin da zai biya bukatunsa da na iyalansa a shekara ba. Saboda haka duk wanda ke da wata gona ko kaddara ko dabbobi amma ba za su biya bukatun iyalansa tsawon shekara ba, to ya halalta a ba shi Zakka.

Imamiyya da Shafi'iyya da Hambaliyya sun ce wanda yake da ikon nema ba ya halalta ya karbi zakka. Hanafawa da Malikawa kuma suka ce ya halalta kuma ana iya ba shi.

Kan kwana a Muzdalifa a yayin aikin hajji kuwa, Hanafiyya da Shafi'iyya da Hanbaliyya sun ce wajibi ne a kwana a can, wanda ya bar shi sai ya yi yanka (haka Al-Mugni ya kawo). Imamiyya da Malikiyya kuwa suka ce bai wajaba ba, amma shi ya fi.

Wajen jifa a Jamratul Akba kuwa, Malikiyya da Hanafiyya da Hambaliyya da Imamiyya suka ce bai halalta a yi jifa gabannin alfijir ba, idan kuwa aka yi hakan ba da wani uzuri ba, sai an sake. Sai dai sun halalta gabatarwar domin uzurai kamar gajiyawa ko rashin lafiya ko tsoro. Shafi'awa kuwa suka ce babu laifi a yi jifa gabannin alfijir domin lokacin da aka ambata na mustahabbanci ne ba wajibci ba (Al-Tazkira da Bidaya na Ibn Rushdi).­­­

Kan daurin aure Imamiyya da Hambalawa da Shafi-'awa cewa suka yi ba ya halalta a daura aure da rubutu, watau dole ne a yi da baki. Hanafawa suka ce yana inganta idan mai neman aure da wacce ake nema ba sa guri guda.

Shafi'awa da Malikawa suka ce: waliyi na iya aurar da baliga shiryayya idan budurwa ce ko ba da yardarta ba. Idan kuwa bazawara ce, to sai da yardar ta, ba zai gudanar da daura mata aure shi kadai ba, ita ma haka. Ko da yake wajibi ne shi zai yi siga, ita ba za ta iya siga ba.

Hannafawa kuwa suka ce baliga mai hankali tana iya zabin miji da siga da kanta, budurwa take ko bazawara, ba wanda yake da walicci a kanta ko hakkin sabawa zabinta da sharadin ta zabi mutumin da ya yi daidai da ita, kuma kada ta yi aure da mafi karanci daga sadakin tamkarta.

Mafi yawan malaman Imamiyya sun ce baliga shiryayya tana da mallakar dukkan lamurran da suka shafi kulla wata yarjejeniya har da na aure, budurwa take ko bazawara, hakan kuwa saboda balaga da kuma shiryuwarta ne. Tana iya daura aure wa kanta ko waninta, ko ta yi da kanta ko da wakili, ko ta bayar ko karba. Ita kamar namiji take ba tare da wani bambanci ba.

Batun sakin aure kuwa, Abu Zuhra ya fada cikin littafinsa Ahwalul Shaksiyya shafi na 283 cewa: "A mazhabar Hanafiyya saki yana aukuwa ne daga kowani mutum idan ba yaro ko mahaukaci ko mai raunin hankali ba, saboda haka saki yana aukuwa daga mai wasa ko mai maye daga abin da yake haram, ko wanda aka tilasta". A shafi na 286 ya ce: "Tabbatacce yake a mazhabar Hanafiyya cewa sakin wanda ya yi kuskure ko mantuwa yana aukuwa"([248]) .

A shafi na 284 kuma ya ce: "Malik da Shafi'i sun dace da Abu Hanifa da mutanensa kan batun sakin mai wasa, Ahmad ya saba da shi, yana ganin rashin aukuwar sakin". Imamiyya sun ruwaito daga Ahlulbaiti (a.s) cewa: "Babu saki sai ga wanda ya nufi sakin".

Dangane da iddar macen da ta yi zina kuwa: Hanafawa da Shafi'awa da mafiya yawa daga Imamiyya sun ce: Idda ba ta wajaba domin zina, domin ruwan (maniyyin) mazinaci ba shi da wata alhurma (girmama-wa). Saboda haka ya halalta a daura aure wa macen da ta yi zina, da kuma ingancin takar ta ko da tana da ciki. Amma Hanafawa sun haramta takar mai ciki sai ta haihu duk da yake ana iya daura mata aure.

Malikawa kuwa sun ce: Wanda ya yi zina da mace tamkar takan ta ne cikin rashin sani, dole ne ta yi istibra'i gwargwadon idda sai fa idan ana nufin tsayar da haddi kanta ne, a nan kam sai ta yi istibra'i da haila guda. Hanbalawa kuwa suka ce: Idda wajiba ce kan mazinaciya kamar yadda take kan sakakka (AlMugni, juzu'i na 6 da kuma Majma'ul Anhar)

Kan batun wasiyya ga ciki (wato dan da ke cikin ciki) kuwa, malaman fikihu sun saba kan cewa shin dole ne a samu cikin yayin wasiyyar ko kuma a'a.

Imamiyya da Hanafiyya da Hambaliyya da Shafi'iyya bisa mafi ingancin zantuttukansu sun ce ana shardanta hakan, kuma cikin ba ya gado sai idan an san cewa samamme ne yayin wasiyyar. Ana tabbatar da hakan ne, idan matar ta haihu kafin wata shida bayan an yi wasiyyar idan tana da miji mai iya saduwa da ita. Idan kuwa ta haihu bayan wata shida ko fiye, to ba a bai wa ciki kome daga cikin wasiyyar saboda yiyuwar samuwar sabon ciki. Tushe shi ne rashin samuwar ciki yayin da aka yi wasiyyar. Wannan kauli kuwa ya ginu ne kan rashin halalcin wasiyya wa wanda ba samamme ba.

Malikawa kuwa sun ce: Wasiyya tana inganta wa cikin da yake samamme ne da wanda zai samu nan gaba, domin suna ganin halalcin wasiyya wa wanda ba samamme ba. (Dubi Tazkiratul Hilli da Fikihu ala Mazahib Al-Arba' da litattafan fikihu na Hanbaliyya da dama a babin wasiyya).

Wadannan misalai ne 'yan kadan daga fikihu idan an kwatanta mazhabobin Musulunci da junansu. Muna iya ganin yadda wasu mazhabobi suka dace ko suka saba da juna a mas'alolin hukumce-hukumce. Za a ga Malikiyya da Shafi'iyya sun dace da Imamiyya, su saba da Hanafiyya da Hambaliyya, ko Hanafiyya ko Hambaliyya su dace da Imamiyya, su saba da sauran mazhabobi Ahlussunna, da dai sauran irin wannan. Saboda haka sassabawa ba ta dogara da kasancewa cikin Sunna ko Shi'a, sassabawar ta ilimi da tunani, ba sabawar Sunna da Shi'a ba ce, ko kusa, sai dai sabawa ce ta tsarin ilmin ciro hukumce-hukumce na mazhabobin nan biyar. Saboda haka ya zama wajibi a kan mu mu tantance dalilai na shari'a ta hanyar tattaunawa ta ilmi domin isa ga dacewa, sabili da hukumcin Allah dai daya ne akan kowace mas'ala.

Masu kokarin nuna cewa sabanin da ke akwai tsakanin Sunna da Shi'a tamkar ya mai da su kishiyoyi masu jayayya tsakanin juna, ba abin da suke yi sai karkata gaskiya da nisantar tsarin kubutaccen tattaunawa ta ilmi. Babu abin da suke yi sai aiki wa abokan gaban musulmi ta hanyar wargaza hadin kan musulmi.

Ayar Wilaya

"Abin sani kawai, majibincinku Allah ne da ManzonSa da wadanda suka yi imani, wadanda suke tsayar da salla, kuma suna bayar da zakka alhali suna masu ruku'i. Kuma wanda ya jibinci Allah da ManzonSa da wadanda suka yi imani, to, kungiyar Allah su ne masu rinjaye". (Surar Ma'ida, 5: 55-56)

Zamakhshari cikin tafsirinsa ya bayyana cewa: "Wannan aya ta sauka ne dangane da Aliyu (Allah Ya karrama fuskarsa) lokacin da wani ya roke shi alhaliyana cikin ruku'in salla, sai ya sake masa zobensa wanda yake loko-loko a dan kuriyarsa, wanda cire shi baya bukatar aiki mai yawa da ka iya bata salla. Idan ka ce ta ya ya za a ce da Ali ake alhali lafazin na jam'i ne? sai in ce maka: An zo da shi akan lafazin jam'i ne ko da yake dalilin saukar ayar a kan mutum guda ne domin a kwadaitar da mutane wajen yin tamkar aikinsa, sai su sami tamkar ladansa. Domin kuma tambihi cewa halayen muminai wajibi ne su kasance da wannan koluwa wajen kwadayin aikin alheri da bibiyar lamarin mabukata ta yadda idan wani abin da ba ya son jinkiri ya lizimce su suna cikin salla, ba sa jinkirta shi sai an idar da sallar([26])

Al-Wahidi ya ambata cewa al-Kalbi ya fadi cikin dalilin saukar wannan aya, cewa: "Lalle karshen wannan aya a kan Aliyu dan Abi Talib (r.a.) take domin ya ba da zobensa ga wani mai bara alhali yana cikin ruku'un salla([27]) ".

Littattafan tafsiri da hadisi masu yawa sun ambato cewa wannan aya mai albarka ta sauka ne dangane da Imam Ali (a.s.). Akwai cikakken bayani kan hakan cikin wadannan littattafa ga mai karin bayani([28]) .

Ayar Tablig (Isar da Sako)

Ya kai Manzo! Ka iyar da abin da aka saukar maka daga Ubagijinka. Kuma idan baka aikata ba, to, ba ka iyar da sakonSa ba kenan, kuma Allah Zai tsare ka daga mutane([29]) ” (Surar Ma'ida: 5:67.

An saukar da wannan aya ne a wani kwari da ake ce ma Ghadir Khum. Ga bayanin akan abin da ya faru:

An ruwaito cewa, yayin da Manzon Allah (s.a.w.a.) yake dawowa daga Hajjin Ban Kwana([30]) sai wannan aya (da muke magana a kanta) ta sauka a gare shi a rana ta goma sha takwas ga watan Zul Hajji([31]) .

To sai ya yada zango a Ghadir Khum daga Juhfa([32]) , inda a nan ne kuma hanyoyi suka rarrabu zuwa birnin Madina, Masar da kuma Sham. Sai ya tsaya a nan har wadanda suke bayansa suka iso, wadanda suke gaba kuwa suka komo inda yake([33]) . Akwai wasu itatuwan kaya a rarrabe, sai aka hana Sahabbai sauka a karkashinsu. Sai Manzon Allah (s.a.w.a.) ya sa aka sare wadannan itatuwa na kaya([34]) , sai ya sa aka yi kiran salla([35]) , ya sallaci azahar tare da jama'a cikin garjin rana([36])

Daga nan sai ya mike ya gudanar da huduba bayan ya yi godiya ga Allah da kuma tsarkake Shi da kuma yin wa'azi ga al'umma, sai ya ce: "Hakika an kusa a kira ni kuma in amsa, ni kuma abin tambaya ne ku ma abin tambaya ne, to me za ku ce?

Sai suka amsa: "Za mu ba da shaidar cewa kai ka isar da sako, ka yi nasiha, to Allah Ya saka maka da alheri".

Sai Annabi (s.a.w.a) ya ce: "Shin ba kwa shaidar cewa babu abin bauta da gaskiya face Allah ba, kuma Muhammadu bawanSa ne kuma ManzonSa, da cewa aljanna gaskiya ce, wuta ma gaskiya ce"?

Sai suka ce: "Haka ne, mun shaida hakan".

Sai ya ce: "Ya Allah Ka shaida", sai ya ci gaba da cewa: "Shin ba kwa ji".

Sai suka ce: "Na'am" (watau suna ji).

Sai ya ce: "Ya ku mutane! Ni mai gabata ne ku kuma masu iske ni ne a bakin tabki, fadinsa tamkar tafiyar tsakanin garin Basra da San'a'([37]) ne, akwai kofuna na azurfa, yawansu kamr adadin taurari, ni kuma mai tamabayarku ne batun abubuwa biyu masu nauyi (Sakalaini), to ku kula da yadda za ku kasance game da su a bayana".

Sai wani ya yi kira ya ce: "Mene ne wadannan nauyaya biyu, Ya Manzon Allah?

Sai ya ce masa: "Littafin Allah, gefe yana hannun Allah, gefe kuma yana hannunku, to ku yi riko da shi, ba za ku bata ba, ba za ku canjba ba, da kuma iyalina, mutanen gidana. Hakika Mai Tausayawa, Masani, Ya sanar da ni cewa su biyun ba za su rabu da juna ba har sai sun iske ni a bakin tafki. Na roka musu wannan wajen Ubagijina, saboda haka kada ku gabace su sai ku halaka, kada ku takaita (ga barinsu), sai ku halaka, kada ku sanar da su domin sun fi ku sani([38]) .

Sannan sai ya ce: "ashe ba ni ne nafi cancanta ga kowane mumini a kan kansa ba"?

Sai suka ce: "Haka ne, Ya Manzon Allah([39]) ".

Daga nan sai ya kama hannun Aliyu bn Abi Talib (a.s.) ya daga sama har mutane suka ga farin hammatarsa([40]) , ya ce:

Ya ku mutane! Allah Shi ne Majibincina, ni kuma ni ne majibincinku([41]) . To duk wanda na ke majibincinsa, wannan Aliyun majibincinsa ne. Ya Allah! Ka jibinci wanda ya jibince shi, Ka yi gaba da wanda ya yi gaba da shi([42]) , Ka taimaki wanda ya taimake shi, Ka wulakanta wanda ya wulakanta shi([43]) , Ka so mai son sa, Ka ki wanda ya ki shi([44]) ". Sannan sai ya ce: "Ya Allah Ka shaida([45]) ".

Ba su (Manzon Allah da Aliyu) rabu ba har sai da Allah Ya saukar da wannan aya: "A yau Na kammala muku addininku, kuma na cika muku ni'imaTa a kanku, kuma Na yarda da Musulunci ya zama addini a gare ku". (Surar Ma'ida, 5:3)

Sai Manzon Allah (s.a.w.a.) ya ce: "Allahu Akbar! Bisa kammalar addini da cikar ni'ima da yardar Ubangiji da Manzancina da walittakan Aliyu([46]) ".

Akwai ayoyi masu yawa, wadanda wannan karamin littafi ba zai iya tattaro su ba, da suke magana a kan matsayin Ahlulbaiti (a.s) da karamar su da girman mutanen ciki, wadanda wasu daga cikinsu sun kebanta ne ga Uban wannan itace mai tsarki, wato Imam Ali (a.s.). Mai karatu zai iya samun wadannan ayoyi cikin littattafan tafsiri, hadisi, tarihi da kuma masu bayani kan falalolin wadannan taurari da kuma wadanda suka yi magana kan Asbabun Nuzul na wadannan ayoyi. To amma bari mu kawo kadan daga cikin irin wadannan ayoyi, su ne kuwa:

(1). Fadin Allah Madaukakin Sarki: "Abin sani kawai kai mai gargadi ne kuma a cikin kowadanne mutane akwai mai shiryarwa". (Surar Ra'ad, 13:7)

Hadisi ya zo cewa Manzon Allah (s.a.w.a.) ya sanya hannunsa bisa kirjinsa, ya ce: "Ni mai gargadi ne, ko wadanne mutane kuma suna da mai shiryarwa", sai ya yi nuni da hannunsa zuwa Ali (a.s.), sai ya ce kai ne mai shiriyarwan, Ya Aliyu, da kai masu shiryuwa za su shiryu a bayana([47]) ".

(2). Fadar Allah Madaukakin Sarki: "Shin wanda ya zama mumini yana kamar wanda ya zama fasiki? Ba za su yi daidai ba". (Surar Sajada, 36: 18)

Wannan mumini kuwa shi ne Aliyu (a.s.), fasikin kuma shi ne Walid bn Ukba([48]) .

(3). Fadar Allah Madaukakin Sarki:

"Shin wanda ya kasance a kan hujja bayyananna daga Ubangijinsa, kuma shaida na binsa daga gare shi..." (Surar Hudu, 11:17)

Manzon Allah (s.a.w.a.) shi ne yake bisa hujja bayyananna a al'amarinsa, shaidan kuwa shi ne Imam Ali (a.s.)([49]) .

(4). Fadar Allah Madaukakin Sarki:

"...to lalle Allah Shi ne Mataimakinsa da Jibrilu da Salihin muminai..." (Surar Tahrim, 66: 4) Salihin muminai a nan shi ne Aliyu bn Abi Dalib (a.s.)([50]) .

(5). Fadar Allah Madaukakin Sarki:

"...kuma wani kunne mai kiyayewa ya kiyaye". (Surar Alhakkatu, 69: 12)

Manzon Allah (s.a.w.a.) ya karanta wannan aya, sai ya juya ga Ali (a.s.), ya ce: "Na roki Allah da ya sanya shi shi ne kunnenka". Sai Ali (a.s.) ya ce: "Babu wani abu da na ji daga Manzon Allah (s.a.w.a.) na manta shi([51]) ".

Al-Wahidi ya nakalto cikin Asbabun Nuzul daga maruwaita daga Buraida, cewa: "Manzon Allah (s.a.w.a.) ya ce wa Aliyu (a.s.) cewa: "Allah Ya umurce ni da in kusato da kai, kada kuma in nisantar da kai, cewa kuma in ilmantar da kai, don ka kiyaye, kuma Allah Ya yi alkawarin Zai sa ka kiyaye din. Sai aya ta sauka: "Kuma wani kunne mai kiyayewa ya kiyaye".

(6). FadinSa Madaukakin Sarki cewa: "Hakika wadanda suka ba da gaskiya suka kuma yi aiki na nagari, to (Allah) Mai rahama Zai sanya soyayya a tsakaninsu". (Surar Maryam, 19: 96)

Manzon Allah (s.a.w.a) ya ce wa Aliyu (a.s.) cewa: "Ya Aliyu ka ce: "Ya Allah Ka sanya mini wani alkawari, kuma Ka sanya mini soyayya cikin zukatan muminai". Sai Allah Ya saukar da wannan ayar dangane da Aliyu (a.s.)([52]) .

(7). Fadar Allah Ta'ala cewa: "Lalle ne wadanda suka yi imani, kuma suka aikata ayyukan kwarai, wadannan su ne mafifita alherin halitta" (Surar Bayyina, 98:7)

Manzon Allah (s.a.w.a) ya ce: "Ya Aliyu, mafifita alherin halitta (a cikin wannan aya) su ne, kai da 'yan shi'arka([53]) ".

(8). Fadar Allah Madaukakin Sarki cewa: "Yanzu kwa mayar da shayar da alhazai da raya Masallaci mai alfarma kamar wanda ya ba da gaskiya da Allah da ranar lahira kuma ya yi jihadi domin Allah?..." (Surar Tauba, 9: 19) Lalle wadannan su ne Abbas da Dalha, wanda ya yi imani kuwa shi ne Aliyu (a.s.). Akwai wasu ayoyi da dama a kan wannan lamari da muke magana a kansa, amma za mu takaita saboda takaitawa.

Ahlulbaiti (a.s) Cikin Sunnar Annabi

Dukkan wanda ya bibiyi sunnar Manzon Allah (s) da tarihinsa na aikace da kuma alakarsa da mutanen gidansa wadanda nassin Alkur'ani ya kawo, sannan shi (Manzo) kuma ayyanasu (Aliyu da Fadima da 'ya'yansu biyu), zai san cewa mutanen wannan gida suna da wata rawar da za su taka a bangaren nauyin rike sako da kuma wayewar wannan al'umma. Hakika Manzon Allah (s.a.w.a.) ya kasance mai tsare-tsare domin al'ummar tasa da kuma shirya da ita domin ta karbi wannan ni'ima ta Ahlulbaiti (a.s), da umarnin Allah (S.W.T.).

Hakika wannan yanki mai haske na tsare-tsaren Annabi (s.a.w.a), wadanda ya yi da umurnin Allah, ya soma ne da aurar da Fadima (a.s.) ga Imam Ali (a.s.), da dasa wannan itaciya mai albarka, domin rassanta su mamaye sansanin wannan al'umma, tsawon rayuwarta.

An ruwaito Manzon Allah (s.a.w.a.) ya ce wa Aliyu (a.s.) yayin da ya aurar masa da Fadima (a.s.) cewa: "Lalle Allah Madaukakin Sarki Ya umurce ni da in aurar maka da Fadima bisa sadaki gwargwadon nauyin miskalin azurfa dari hudu, shin ka yarda da hakan". Sai Aliyu (a.s.) ya ce: "Lalle na yarda da hakan, Ya Manzon Allah". Anas bin Malik ya ce: Sai Annabi (s.a.w.a) ya ce: "Allah Ya hada kanku, Ya arzurta kokarinku, Ya albakace ku, Ya kuma fitar da zuriya mai albarka". Sai Anas ya ce: "Wallahi, hakika kuwa Allah Ya fitar da zuriya mai albarka daga gare su"([54]) .

An ruwaito cewa yayin da Annabi (s.a.w.a) ya aurar da Fadima ga Aliyu (a.s.), sai ya shiga wajenta ya kira ta sai Ummu Aiman ta kawo kasko da ruwa a ciki, sai Manzon Allah (s.a.w.a.) ya yi tofi a ciki sannan ya yayyafa a kanta da tsakanin nononta, sannan ya ce: "Ya Allah! Ni ina nema mata tsarinKa da zuriyarta daga shaidan jefaffe". Sai kuma ya ce wa Ali (a.s.): "Miko min ruwa", sai Aliyu (a.s.) ya kawo masa, sai ya zuba a kansa da kuma tsakanin kafadunsa (a.s.), sai ya ce: "Ya Allah! Ina nema masa tsarinKa da zuriyarsa daga shaidan jefaffe".

A wata ruwayar kuma cewa aka yi, sai ya bukaci a kawo masa ruwa, bayan ya yi alwala da shi sai ya zuba a kan Aliyu da Fadima (a.s.), sai ya ce: "Ya Allah! Ka albarkace su cikin zuriyarsu([55]) ".

Manzon Allah (s.a.w.a.) ya kasance yana neman uzuri ga duk wani daga cikin sahabbai da ya zo neman a ba shi Fadima (a.s.), yana mai cewa: "Hukumci bai sauko ba tukunna([56]) ".

Hakika wannan kula ta Ubangiji da AnnabinSa ta aurar da Fadima (a.s.) ga Aliyu (a.s.) ta sanya aurar da ita bai faru ba face da umurni daga Allah (S.W.T.) domin wannan ya yi nuni ga matsayin Ahlulbaiti (a.s) da kuma alherin al'umma da Manzon Allah (s.a.w.a.) yake nufi da alakarsa da su. Wannan matsayi na su kuwa shi ne Alkur'ani mai girma ya fassara, haka nan ma sunnar Annabi (s.a.w.a) mai daraja.

Watakila hasken da muke tsinkaya daga ruwayoyi da hadisai Manzon Allah (s.a.w.a.) da Ahlulbaiti (a.s) (wadanda kuwa masu yawa ne) suna riskar da mu ne irin zurfaffar kula ta Allah da ManzonSa (s.a.w.a) wajen gina wannan gida, da yawaita soyayya da albarka da kula gare shi. Domin mutanen wannan gida su zama ja-gororin al'umma cikin rayuwarsu da kuma hanyoyin tsirarsu daga bala'u da kuma kasancewa tsari da makoma ta hadin kanta yayin da ta rarraba, kamar yadda ruwayoyi da hadisai suka yi nuni da hakan.

Manzon Allah (s.a.w.a.) yana danganta zuriyar Aliyu da Fadima (a.s.) da kansa, yana cewa: "Lalle su zuriyata ne 'ya'ya ne, kamar yadda Alkur'ani ya bayyana hakan da cewa: "To, wanda ya yi musu da kai a cikinsa, a bayan abin da ya zo maka daga ilmi, to ka ce: "Ku zo mu kirayi 'ya'yanmu da 'ya'yanku da matanmu da matanku da kanmu da kanku". (Surar Ali Imrana, 3: 61)

Abin nufi da 'ya'yansa a wannan aya su ne Hasan da Husaini (a.s.), kamar yadda maganganun malaman tafsiri da ma'abuta tarihi suka sanar da mu.

Hakika Manzon Allah (s.a.w.a.) ya karfafa wannan ma'anar wa al'ummarsa sau da yawa, bari mu ambaci kadan daga cikinsu. Manzon Allah (s.a.w.a.) yana cewa:

"Allah Ya sanya zuriyar kowane Annabi daga tsatsonsa, (ni kuma) Ya sanya zuriyata cikin tsatson wannan", yana nufin Aliyu (a.s.)([57]) .

Manzon Allah (s.a.w.a.) ya kasance yana rungumar Hasan da Husaini (a.s.), yana cewa: "Dukkan 'ya'yan wani uba dangantakarsu ta ubansu ce, ban da 'ya'yan Fadima, ni ne ubansu, da ni ake dangantasu". Imam Ahmad ya fito da wannan hadisin cikin al-Manakib([58]) .

Hakika Manzon Allah (s.a.w.a.) yana karfafa matsa-yin Ahlulbaiti (a.s) a kowani muhimmin lokaci, domin al'umma ta koma gare su, ta lizimci tafarkinsu, ta kuma yi riko da soyayyarsu. A ruwayoyi da dama, muna samun cewa Manzon Allah (s.a.w.a.) ya nuna mana su a matsayin tudun tsira ga wannan al'umma, yana gwama su da Alkur'ani, yana kuma sanya rawar da za su taka a fagen akida da rike sakon Musulunci, mai lizimtar Littafin Allah ne, ba sa rabuwa da shi. Hakan kuwa don al'umma ta fuskanto su wajen fahimtar Alkur'ani mai girma, da ciro ma'anoninsa da hukumce-hukumcensa.

Littattafan hadisi da tarihi sun taru bisa kawo hadisin Annabi (s.a.w.a) da ake kira da Hadisin Nauyaya Biyu (Hadith al-Thakalain). Musulmi sun ruwaito wannan hadisi duk da bambance-bambancen mazhabobinsu na siyasa da fikihu. Za mu ambace shi a nan tare da sashin isnadinsa (maruwaitan da suka ruwaito shi), kamar yadda masu ruwaya da malaman hadisi suka nakalto.

1- Hadisus Sakalain (Nauyaya Biyu)

Manzon Allah (s.a.w.a.) yana cewa: "Na kusata da a kira ni in kuma amsa, amma ni mai bari muku abubuwa masu nauyi guda biyu ne, su ne kuwa: Littafin Allah Mai girma da Daukaka, da kuma zuriyata. Littafin Allah wata igiya ce da aka sako ta daga sama zuwa kasa, zuriyata kuwa su ne mutanen gidana (Ahlulbaiti). Allah Mai tausasawa Ya ba ni labari cewa su biyun ba za su taba rabuwa ba har abada har sai sun iske ni a bakin tafki. To ku lura da yadda za ku rike su a bayana([59]) ".

Al-Shibrawi al-Shafi'i ya nakalto cikin littafinsa mai suna al-Ithafu bi hubbil Ashraf, cewa: "Muslim da Tirmizi sun kyautata shi (hadisin), haka ma Hakim shi ma ya ruwaito shi, lafazin Muslim kuwa daga Zaid bn Arkam cewa ya yi: "Manzon Allah (s.a.w.a.) ya mike a cikinmu domin ya yi mana huduba sai ya yi godiya ga Allah ya yi yabo gare Shi, sannan ya ce:

"Bayan haka, Ya ku mutane, ni dai mai mutuwa ne, kuma zan amsa kiran manzon Ubangijina. To amma na bar muku wasu nauyayan abubuwa guda biyu tare da ku; na farkonsu Littafin Allah, shiriya da haske na cikinsa, to ku kama Littafin Allah ku yi riko da shi". Sannan sai ya ce: "Da Ahlulbaitina, ina gama ku da Allah dangane da Ahlulbaitina([60]) ".

Al-Shibrawi din kuma ya nakalto cewa: "A wata ruwayar kuma Manzon Allah (s.a.w.a.) cewa ya yi: "Ni mai bari muku al'amurra guda biyu , ba za ku bata ba idan har kun bi su, su ne kuwa; Littafin Allah da Ahlulbaitina". A wata ruwayar kuma (aka cika da cewa) "ba za su rabu ba har sai sun iske ni a bakin tafki, to ku kula da yadda za ku rike su a bayana([61]) ". Ya kara da cewa: "Ibn Hajar ya fada cikin Sawa'ikul Muhrika cewa: "Annabi (s.a.w.a) ya ambaci Alkur'ani da zuriyarsa da cewa "Nauyaya Biyu" ne saboda nauyin dukkan wani mutum shi ne abu mafi muhimmanci a gare shi, kuma wadannan guda biyu haka suke. Domin kuwa kowane daga cikinsu taska ce ta ilmummukan addini da sirrorin hankali irin na shari'a, domin haka ne ma aka kwadaitar da koyi da su. Wani kaulin kuma ya ce an ambace su da "Nauyaya Biyu" ne domin wajibcin kiyaye hakkokinsu. Sannan kuma wanda kwadaitarwar ta tabbata a gare su, su ne masana Littafin Allah masu riko da sunnar ManzonSa (s.a.w.a), domin su ne wadanda ba su rabuwa da Littafin har zuwa tabki([62]) ".

Allama Shaikh Muhammad Jawad al-Balagi ya nakalto cikin tafsirinsa Ala'u al-Rahman fi tafsiril Kur'an cewa: "Haka nan ma kamar hadisin Sakalain wanda yake an tabbatar da ingancinsa kamar yadda 'yan'uwanmu Ahlul Sunna suka ambace shi cikin littattafansu suka kawo ruwayarsa daga sahabbai wadanda suka ji shi daga wajen Manzon Allah (s.a.w.a.):

"Ni mai bari muku Nauyaya guda biyu ko kuma halifofi guda biyu, Littafin Allah da zuriyata, Ahlulbaitina, wadanda idan kun yi riko da su ba za ku bata ba har abada, su ba za su rabu da juna ba har sai sun riske ni a bakin tafki".

(1). Imam Ali bn Abi Talib (a.s)

(2). Abdullahi bn Abbas.

(3). Abu Zar Giffari

(4). Jabir al-Ansari.

(5). Abdullahi bn Umar

(6). Hudhaifa bn Usaid.

(7). Zaid bn Arkam.

(8). Abdurrahman bn Awf.

(9). Dhamratul Aslami.

(10). Amir bn Laili.

(11). Abu Ra'fi'.

(12). Abu Huraira.

(13). Abdullah bn Handab

(14). Zaid bn Thabit.

(15). Ummu Salama.

(16). Ummu Hani.

(17). Khazima bn Thabit.

(18). Sahl bn Sa'ad.

(19). Adi bn Hatam.

(20). Ukba bn Amir.

(21). Abu Ayyub Ansari.

(22). Abu Sai'd al-Khudri.

(23). Abu Shuraih Khuza'i.

(24). Abu Kadama Ansari.

(25). Abu Laili.

(26). Abu Haitham bn Al-Tayhan.

Allama al-Balagi ya ci gaba da cewa: Wadannan su ne muka riga muka ambaci sunayensu bayan Ummu Hani. Kowannensu ya ruwaito shi, shi kadai, kamar wadanda suka gabace shi, sun tsaya a dandalin Kufa tare da mutum bakwai Kuraishawa, suka tabbatar da cewa sun ji wannan hadisi daga Manzon Allah (s.a.w.a.), adadinsu kuwa shi ne talatin da uku.

Kuma abu Nu'aim Al-Isfahani ya ruwaito shi cikin littafin Munkabatu al-Mudahharin da isnadi daga Jabir bn Mad'am da kuma wani isnadin daga Anas bn Malik da Al-Barra'u bn Azib, haka nan Muwaffak bn Ahmad ya ruwaito shi daga Amr bn al-As.

Da wuya a sami wani littafin hadisi babba ko karami ko littafin falaloli da Ahlussunna suka rubuta wanda bai kawo wannan hadisin ba, daga farkon wadanda suka kawo hadisin daga hadda da kuma zukatan mahaddata har zuwa takardun malaman hadisi. Kuma bai gushe ba ana ruwaito shi daga sahabbai guda ko masu yawa. Ta yiwu ma a ruwaito shi daga sama da sahabbai ashirin a littafi guda, ko dai a game kamar yadda ya zo cikin littafin Sawa'ikul Muhrika, ko kuma da isnadi rarrabe kamar yadda ya zo cikin littattafan al-Sakhawi da Suyudi da Samhudi da dai sauransu".

Sannan sai ya ce: "Malaman Imamiyya sun ruwaito shi cikin litattafan-su da isnadinsu masu maimaita juna daga Imam Bakir, Ridha da Kazim da Sadik (a.s.) daga iyayensu (a.s.) daga Manzon Allah (s.a.w.a.) da kuma wadansu isnadan na daban daga Amirul Muminina (a.s) da Umar da Ubayyu da Jabir da Abu Sa'id da Zaid bn Arkam da Zaid bn Thabit da Huzaifa bn Usaid da Abu Huraira da sauransu, dukkanninsu sun ji daga Manzon Allah (s.a.w.a.)([63]) .

A cikin Musnad na Ahmad bn Hambal, ya ruwaito ta hanyar Abi Sa'id al-Khudri daga Manzon Allah (s.a.w.a.) yana cewa:

"Ni na kusanta da a kira ni in amsa, ni kuma mai barin nauyayan abubuwa ne guda biyu tare da ku, Littafin Allah Mai Girma da Daukaka da kuma Ahlulbaitna, shi Littafin Allah igiya ce da aka sako daga sama zuwa kasa. Kuma lalle Mai Tausasawa Masani, Ya ba ni labarin cewa baza su taba rabuwa da juna ba har sai sun iske ni a bakin tafki, don haka ku kula da yadda za ku rike su a bayana([64]) ".

Haka nan kuma idan muka duba za mu ga kusan dukkan maruwaita sun ruwaito wannan hadisi da ke gwama Ahlulbaiti (a.s) da Littafin Allah Mai Tsarki. Daga wannan ne musulmi za su fahimci cewa Ahlulbaiti (a.s) su ne makoma baicin Littafin Allah kuma su ne aka bar wa amanar Littafin har su isa ga tabki.

2- Hadisus Safina (Hadisin Jirgin Ruwa)

Yayin da Hadisus Sakalain yake gwama Ahlulbaiti (a.s) da Alkur'ani waje guda domin nauyin da aka dora musu na bayyana Alkur'anin da kwaranye boyayyun abubuwansa da asirorinsa da abubuwan da ke kewaye da shi, to wannan hadisi na Safina kuwa yana bayyana wa al'umma ne cewa su Ahlulbaiti (a.s) su ne jirgin tsira, kuma hanyar kubutar wannan al'umma bayan Manzon Allah (s.a.w.a.). Domin haka, lallai rashin riskan wannan jirgin da rashin hawansa, zai ja wadanda suka ki shiga jirgin zuwa ga nutsewa da halaka. Domin kin binsu, kin bin ja-gora zuwa gabar shiriya da tsira ne.

Al-Shibrawi al-Shafi'i ya nakalto daga Rafi Maulan Abu Zarri, ya ce: "(Wata rana) Abu Zar (r.a.) ya hau dokin kofar Ka'aba, ya kama marikin kofar ya dogara da shi, sai ya ce: "Ya ku mutane, wanda ya sanni to ya sanni, wanda kuma bai sanni ba, to ni ne Abu Zar, na ji Manzon Allah (s.a.w.a.) yana cewa:

"Ahlulbaitina tamkar jirgin Nuhu suke, wanda ya hau shi ya tsira wanda kuwa ya ki hawa ya fada wuta". Na kuma ji Manzon Allah (s.a.w.a.) yana cewa: "Ku sanya Alayena (agareku) matsayin da kai yake da shi a jiki, kuma matsayin idanu ga kai. Domin shi jiki baya shiryuwa sai da kai, shi kuma kai ba ya shiryuwa sai da idanu([65]) ".

Abu Nu'aim([66]) ya ruwaito ta hanyar Sa'id bn Jubair daga Ibn Abbas, ya ce: "Manzon Allah (s.a.w.a.) ya ce:

"Misalin Ahlulbaitina a cikinku, tamkar jirgin (Annabi) Nuhu ne, wanda ya hau shi ya tsira, wanda kuwa ya ki hawa ya nutse (ya halaka)([67]) ".

An ruwaito ta hanyar Anas bn Malik, cewa, ya ce Manzon Allah (s.a.w.a.) ya ce: "Abin sani kawai shi ne cewa, misalin Ahlulbaitina a cikinku, kamar jirgin Nuhu ne, wanda ya hau shi ya tsira, wanda kuwa ya ki hawansa ya halaka([68]) ".

Suyudi ma ya ruwaito wannan hadisin cikin littafinsa Durrul Mansur karkashin tafsirin fadin Allah Madauka-kin Sarki cewa: "Kuma lokacin da Muka ce: "Ku shiga wannan alkarya, sa'an nan ku ci daga gare ta, inda kuka so, bisa wadata, kuma ku shiga kofa kuna masu tawali'u, kuma ku ce: "Kayar da zunubai" Mu gafarta muku laifukanku". Inda ya ce: "Ibn Abi Shaiba ya fitar da hadisi daga Aliyu bn Abi Talib (a.s.) ya ce: "Abin sani dai, misalinmu (Ahlulbaiti) cikin wannan al'umma kamar misalin jirgin Nuhu ne, kuma kamar Kofar Yafuwa (Hidda) ce([69]) ".

Al-Muttaki ya ruwaito shi cikin littafin Kanzul Ummal (juzu'i na 6 shafi na 216) cewa, Manzon Allah (s.a.w.a.) ya ce: "Misalin Ahlulbaitina a cikinku, tamkar jirgin Nuhu ne, wanda ya hau shi ya tsira, wanda kuwa ya ki hawansa ya halaka, kuma tamkar kofar Hidda ne ta Bani Isra'ila". Sannan ya ce Dabarani ma ya ruwaito wannan hadisi daga Abuzarri([70]) .

3- Hadisin Aminta Daga Sassabawa

A cikin wannan hadisin, Manzon Allah (s.a.w.a.) yana bayyana rawar da Ahlulbaiti (a.s) ke takawa a fagen akida da siyasa. Domin mafi hadarin abin da yake samun al'umma shi ne rarraba da sabawa cikin ra'ayi da akida da kuma fuskantarwa ta siyasa. Don haka ne ya sa Manzon Allah (s.a.w.a.) ya kasance yana tsoratar da al'ummarsa wannan fitinar, ya kasance yana tsare-tsare saboda hadin kanta da riko da juna ta bangaren tunani da siyasa. Kana kuma yake fuskantar da al'ummar tasa zuwa ga lizimta da riko da Ahlulbaitinsa da komawa gare su. A saboda hakan ne kuma, ya siffanta su da cewa su masu lizimtar Alkur'ani da kiransa ne, kuma ba za su rabu da juna ba har ranar tashin kiyama. Ya kuma siffanta su da cewa su jirgin tsira ne, kuma kofar yafuwar zunubbai. To a nan kuma yana siffanta su ne da cewa su ne mattara, kuma su ne madogara mai hada kan wannan al'umma ta musulmi ne, da kuma cewa riko da su da rayuwa bisa tafarkinsu lamuni ne daga rarraba da sabawa.

Al-Dabarani ya kawo hadisi daga Ibn Abbas (r.a.) cew, Manzon Allah (s.a.w.a.) ya ce: "Taurari aminci ne ga mazauna kasa daga nutsewa (halaka), Ahlulbaitina kuwa aminci ne ga mazauna kasa daga sassabawa (rarrabuwa)([71]) ".

Muhibbuddin Dabari ya ruwaito daga Aliyu (a.s.) yana cewa: "Manzon Allah (s.a.w.a.) ya ce: "Taurari aminci ne ga mazowa sama, idan taurari suka tafi, mazowa sama sai su tafi, Ahlulbaitina kuwa aminci ne ga mazowa kasa, idan Ahlulbaitina sun tafi, mazowa kasa sai su tafi". Sai al-Dabarani ya ce: "Ahmad bn Hambal ya ruwaito wannan hadisi cikin al-Manakib([72]) .

4- Hadisul Kisa'i (Hadisin Mayafi)

Hadisin Mayafi shi ne hadisin da ya zo daga Manzon Allah (s.a.w.a.) dangane da Aliyu, Fadima, Hasan da Husaini (a.s.) yayin da Ayar Tsarkakewa ta sauka. Mun riga da dai mun gabatar da wannan hadisi kuma mun yi magana a kan shi tare da kawo ra'ayuyyukan wasu malaman tafsiri, da kuma ruwayoyin da suka yi batun wadannan wadanda aka tsarkake a cikin babin "Ahlulbaiti (a.s) Cikin Alkur'ani". To amma a nan za mu kawo wasu ruwayoyi ne daban domin karfafa wannan fikirar da kuma kafa wannan manufar da Manzon Allah (s.a.w.a.) yake da ita wajen yin hakan (wato lullube su da mayafinsa da kuma yi musu addu'a).

Hanyoyin da wannan hadisi ya zo suna da yawan gaske cikin littattafan hadisi da ruwaya da tafsiri, to amma za mu ambaci wasu daga cikinsu ne kawai:

"Dangane da abin da aka ruwaito daga Ummu Salama, matar Annabi (s.a.w.a), Imam Ahmad ya ruwaito shi cikin Musnad dinsa har ya zuwa ga Ummu Salama, inda ta ce: "Wata rana Manzon Allah (s.a.w.a.) yana dakina, sai wani hadimi ya zo ya ce: 'Aliyu da Fadima na nan bakin kofa', sai ta ce: sai Annabi (s.a.w.a) ya ce da ni: "Ki tashi ki kauce wa Ahlulbaitina". "Sai na tashi na kauce gefe guda. Sai Aliyu da Fadima da Hasan da Husaini suka shigo. A yayin nan Hasan da Husaini suna yara kanana, sai Annabi (s.a.w.a) ya dauke su ya dora su a kan cinyarsa, ya sumbace su, ya rungume Aliyu da hannunsa, Fadima kuma da dayan, sannan ya lullube su da wani bakin mayafi, ya ce:

"Ya Allah! Zuwa gare Ka ba zuwa wuta ba, ni da Ahlulbaitina". Sai Ummu Salama ta ce: 'Da ni ya Manzon Allah', sai ya ce: "Na'am da ke([73]) ".

Al-Wahidi ya ruwaito cikin littafinsa Asbabun Nuzul marfu'i ta hanyar Ummu Salama (r.a.) ta ce: (Wata rana Annabi (s.a.w.a) ya kasance a dakinta sai Fadima (a.s.) ta zo da tukunya da wani abinci na alkama a ciki, sai ta shiga da shi. Sai yace da ita: "Ki kira mini mijinki da 'ya'yanki biyu". Sai Ali da Hasan da Husaini suka zo, suka shiga suka zauna suna cin abincin, Annabi (s.a.w.a) kuma yana zaune a kan wani benci, a kan wani mayafi wanda aka saka a Khaibara. Sai Ummu Salama ta ce: Ni kuma ina cikin dakin, kusa da su, sai Annabi (s.a.w.a) ya kama mayafin ya lullube su da shi, sannan ya ce: "Ya Allah! Mutanen gidana, kebantattuna (kenan), to Ka tafiyar da kazanta daga gare su Ka tsarkake su, tsarkakewa".

Sai ta ce: Sai na shigar da kaina, na ce: "Ni ma ina tare da ku, Ya Manzon Allah". Sai ya ce: "Ke kina tare da alheri, ke kina tare da alheri". Sai Allah Mai girma da Daukaka Ya saukar da ayar:

"...Allah na nufin Ya tafiyar da kazamta kawai daga gare ku, Ya ku mutanen babban gida, kuma ya tsarkakeku tsarkakewa([74]) ". (Surar Ahzabi, 33:33)

5- Hadisin Soyayya

Mun riga da mun yi magana kan Hadisin Soyayya wajen tafsirin Ayar Soyayya, kuma mun ambaci wasu masu ruwaya da suka ruwaito shi da kuma daga wajen wadanda suka ruwaito shi. A nan za mu sake ambaton hadisin ta hanyoyin daban ne, kuma zai kasance mai amfani mu ambaci sashin abin da ya taho daga Annabi (s.a.w.a) a kan son Ahlulbaiti (a.s) da kaunarsu a wasu ruwayoyin na daban.

(Imam Ahmad da Dabarani duk sun ruwaito daga Ibn Abbas (r.a.) ya ce: "Yayin da Ayar Soyayya, wato "Ka ce: "Bana tambayarku wani lada a kansa face dai soyayya ga makusanta", ta sauka, sai mutane suka ce: Ya Manzon Allah, su wane ne makusanta wadanda soyay-yarsu ta wajaba a kanmu?, sai yace: "Aliyu da Fadima da 'ya'yansu guda biyu".

Al-Bazzaz da Dabarani sun ruwaito cewa Hasan dan Aliyu (a.s.) yayi huduba wata rana yana cewa: "Wanda ya sanni to ya sanni, wanda kuwa bai sanni ba, to ni ne Hasan dan Muhammadu (s.a.w.a). Ni ne dan Mai albishir, ni ne dan Mai gargadi, ni ne dan mutanen gida wadanda Allah Ya farlanta son su a kan kowane musulmi, Ya kuma saukar a kansu (da ayar), "Ka ce: Ba ni tambayar ku wani lada a kansa face dai soyayya ga makusanta. Kuma wanda ya aikata wani abu mai kyau, Za mu kara masa kyau a cikinsa". To aikata kyawawan shi ne soyayyarmu, Ahlulbaiti([75]) ".

Al-Saddi ya ruwaito daga Abi Malik daga ibn Abbas (r.a.) dangane da fadin Allah Madaukaki cewa: "...wanda ya aikata wani abu mai kyau, Za mu kara masa kyau a cikinsa".

Al-Saddi ya ruwaito daga Abi Malik daga ibn Abbas (r.a.) dangane da fadin Allah Madaukaki cewa: "...wanda ya aikata wani abu mai kyau, Za mu kara masa kyau a cikinsa". Inda ya ce: "Soyayyar ta Alayen Muhammadu (s.a.w.a) ce([76]) ". Hadisan da suka zo game da so da kaunar Ahlulbaiti (a.s) da kuma yin musu da'a da lizimtarsu, ba za su kirgu ba cikin wannan dan karamin littafi, sai dai mun zabi sashi ne daga cikinsu kawai, don kuwa kowanne daya daga cikinsu (Ahlulbaiti) (a.s.) rana ce mai haske a cikin littattafan hadisi da ruwayoyi.

To amma domin a kara arzurta mai karatu da kara karfafa abin da zai kara masa sanin Ahlulbaiti (a.s) da kuma karfafa dangantaka da su, da mai da shi mai ta'allaka da su, mai rayuwa bisa tafarkinsu, don ya samu nasarar samun cetonsu, bari mu sake ambaton wasu daga cikin hadisan da suka zo game da su:

(Dabarani ya fitar da hadisi cikin littafin al-Awsad daga ibn Hajar (r.a.) cewa; "Karshen abin da Manzon Allah (s.a.w.a.) ya furta shi ne: "Ku wakilce ni cikin Ahlulbaitina([77]) ").

(Dabarani ya fitar da hadisi cikin littafin Al-Awsad daga Jabir bn Abdullah (r.a.) ya ce: "Manzon Allah (s.a.w.a.) ya yi mana huduba, na ji yana cewa: "Ya ku mutane! (Duk) wanda ya fusata mu, mu Ahlulbaiti, Allah Zai tashe shi ranar kiyama yana bayahude([78]) ".

(Muslim da Tirmizi da Nasa'i duka sun ruwaito daga Zaid bn Arkam cewa, Manzon Allah (s.a.w.a.) ya ce: "Ina tunatar da ku Allah game da Ahlulbaitina([79]) ".

Alkhatib ya fitar a cikin littafin Tarihinsa daga Aliyu (r.a.) cewa: Manzon Allah (s.a.w.a.) ya ce: "Cetona ga al'ummata, na ga wanda ya so Ahlulbaitina([80]) ".


3

4

5

6

7

8