Kalu balanta Da Amsoshinsu
Kalu bale na farko: shi ne, wannan nau;in tawassuli ko kamun kafa bai kasance ba a lokacin sahabbai da tabia'i?
Amsa: Ta fuskar ka'idoji na ilimi, aikin ma'asumi yana nuni a kan halascin abu, amma barinsa a kan aikata wani abu ba ya nuni a kan haramcin abu. Idan muka dauka cewa sahabbai ba su yin sabo ko kuskure, wato muka yi musu hukuncin ma'asumai, a nan rashin aikatawarsu ba ya zamar mana dalili a kan haramcin abu ba. Bayan haka, ma'auni a wajen sanin haramci ko halascin abu shi ne maganar Manzo ko magadansa ma'asumai (A.S) don haka muna iya ganin wannan nau'i na Tawassuli a fili a cikin ruwayoyin Manzo da addu'o'in Ahlul baiti (A.S)
Kalu balanta ta biyu:
Halittu ba su da hakki a kan Allah: Wannan nau'i na tawassuli kamar wani dora nauyi ne ga Allah ta yadda dole ne Allah ya bayar da wannan hakki da ya hau kansa, alhali kuwa babu wani nauyi na wani abin halitta wanda yake a kan Allah madaukaki.
Amsa: Hakkin abin halitta a kan Allah muna iya kallon sa ta fuska biyu:
A-Sakamakon wasu ayyukana bawa yakan iya samun wani hakki a kan Allah kamar yadda mai bin bashi yake da hakki a kan wanda yake bi bashi. Irin wannan hakki ba zamu iya tunaninsa ba a kan Allah madaukaki daga bangaren bawa, domin kuwa bawan Allah bai mallaki komai ba, ta yadda ta hanyar wannan zai samu wani hakki a kan Allah.
B-Hakin da shi da kansa Allah ta hanyar wani lutfi wanda ya yi ga shi bawa, ta wannan hanyar sai bawan ya samu hakki a wajen Allah. Wato hakikanin kuwa shi ne wata falala ce wacce Allah ya yi wa bawa sakamakon haka sai ya sanya bawan yana da wani hakki a kan Allah madaukaki, ta yadda ya sanya kansa matsayin wanda ake ba shi, shi kuma bawa matsayin mai bin bashi, bayan kasantuwar cewa wannan yana iya yiwuwa a cikin Kur'ani akwai dalilai masu tabbatar mana da hakan.
Wani lokaci Allah yana daukar kansa matsayin wanda ya dauki bashi daga bayinsa, shi kuwa bawa masatyin mai ba ba bashi, a kan hakane yake cewa: "Wa zai bai wa Allah rance mai kyau".
Bayan wannan akwai ayoyi da yawa wadanda suke bayani a kan cewa sakamakon wata baiwa da Allah yake wa bayinsa, zasu kasance suna samun wani hakki na musamman ga Allah wanda yake ba shi da farko ba shi da karshe. A wasu wurare ga abin da yake cewa:
1-"Ya kasance hakki a kanmu mu taimaki muminai" .
2-"Alkawari ne a kan Allah kuma hakki ne a cikin Attaura da Injila" .
3-"Kuma hakki ne a kanmu mu taimaki muminai" .
4-Karbar tuba ya wajaba a kan Allah ga wadanda suke ayyuka mummuna sakamakon jahilci, sannan sai suka tuba ba tare da jinkiri ba" .
Sannan a cikin hadisai da dama zamu iya ganin irin wadannan hakkoki. Don haka a nan kawai zamukawo daya daga cikin a matsayin misali kamar haka: Manzo (S.A.W) yana cewa ya wajaba ga Allah ya taimaki wanda ya yi aure domin tsoron kada ya fada a cikin haram.
Kalu bale na uku:
Wannan nau'in na kamun kafa ko Tawassuli kiran wanin Allah ne. Ayoyi da yawa a cikin Kur'ani mai girma sun yi bayani a kan cewa musulmi bai halatta ba ya kira ko ya roki wanin Allah, kamar yadda Allah madaukaki yake cewa: "Kada ku kira wani tare da Allah" "Lallai wadanda kuka kira suma bayi ne kamar ku" .
Daga wadannan ayoyi guda biyu muna fahimtar cewa a wajen addu'a babu wanda ya kamata a kira sai Allah madaukaki shi kadai ba wanin Allah ba, don haka kamun kafa da wani ko matsayin wani kiran wanin Allah ne.
Amsa: Abin da yake mafi rashin tushen a cikin kalu balantar da ake yi dangane da kamun kafa ko Tawassuli shi ne wannan wanda aka ambata a sama, wanda kuma da wannan ne masu kin amincewa da tawassuli suke riko da shi, ta yaddacikin rashin adalci suke dora ayoyin da suka zo a kan mushrikai masu bautar gumaka a kan musulmai da manyan bayin Allah. Duk da cewa wadannan ayoyi sun sauka ne a kan mushrikai wadanda suke daukar gumakansu matsayin alloli komasu tafiyar da duniya. Ba kamar yadda musulmi ba ya dauka cewa Manzo (S.A.W) bawan Allah ne kuma mai kira zuwa ga kadaita Allah madaukaki, sakamon ana yin amfani da irin wadannan ayoyi a wajen irin haka, don haka zamu yi dan bayani a kan wadannan ayoyi kamar haka:
1-Ayoyin da suke cewa: Kada ku kira wanin Allah, wadannan ayoyi suna nufin kiran Allah da ma'anar bauta ne, ba wai da nufin kira ba kawai ga wani mutum mai matsayi koda kuwa da niyyar cewa shi kawai wani mutum ne mai tsarki, domin kuwa a matsayin sheda a ayar da ta gabata yana cewa: "Kada ku kira wani tare da Allah". Idan cikin wannan aya ana nufin kira ko roko ne kawai ba yana nufin bauta ba ne, to zai zamana ma'anar wannan aya ta sabawa umurnin Kur'ani, domin kuwa Kur'ani yana ba da umarni ga musulmi cewa su tafi wajen Manzo su neme shi da ya roka musu Allah gafara, sannan shi ma ya gafarta musu.
A nan mutum yana kiran Ubangiji yayin da yake neman gafarar Allah da kansa, sannan yana kiranmanzo yayin da yake so ya gafarta masa. Saboda haka ma'nar cewa kada ku kira wani tare da Allah shi ne, kada ku hada wani tare da Allah wajen bauta.
Kamar haka ne a cikin aya ta biyu ma babu bambanci, domin kuwa abin da ake nufi da "kuke kira" a cikin aya ta biyu ana nufin bauta ne, domin kuwa jimalar da ta zo a bayanta wacce kuma take haramta yin hakan tana cewa: "Domin kuwa su bayi ne kamarku". Wato kada ku bautawa wadannan gumakan na karya domin kuwa ba su da wani bambanci da ku, suma kamarku suke bayi ne na Allah.
Saboda haka hanin da aka yi na kada a kira wani tare da Allah ko kuma a kira shi ba tare da Allah ba, ana nufin kira ne wanda yake da ma'anar bauta, wanda ya samo asali ne daga imanin mutum da cewa shi wannan abin a matsayin Allah ne, ba wai kawai kira ba tare da wannan imanin ba, domin kuwa rayuwar dan Adam baki daya ta doru a kan haka ne. Kur'ani mai girma yana cewa: "Zamu kirawo 'ya'yammu kuma ku kirawo 'ya'yanku" .
Sannan a cikin wata aya ana cewa bai kamata ku kira Manzo ba kamar yadda kuke kiran sauran mutane a tsakaninku, ga abin da ayar take cewa: "Kada ku sanya kiran Manzo kamar a tsakaninku kamar yadda kuke kiran junanku" .
Saboda haka kiran da ake magana a cikin wannan aya ba ana nufin kawai kira ba haka nan, ana nufin kira da sunan bauta ga Allah ko ga wani wanda mutum ya dauka cewa shi ne yake tafiyar da wasu ayyukan Ubangiji.
Don haka wadannan ayoyi guda biyu da wasu misalinsu, wace alaka suke da ita dangane da rokon da muke wa Manzo a matsayinsa na bawan Allah mai matsayi, ko kuma kawai mu kira shi ba tare da nufin ibada ba.
A cikin Littattafan masu inkarin kamun kafa da wani bawan Allah, sun tattaro duk ayoyin da suke magana danagane da mushrikai da suke kiran gumakansu na karya, sannan suka dora wadannan ayoyi a kan musulmai masu kamun kafa da ruhin manyan bayin Allah. Duk da cewa tare da la'akari da wasu abubuwa guda biyu sun fita daga bahsimmu kamar haka:
1-Wadannan ayoyi suna magana ne a kan mushrikai ba masu kadaita Allah ba.
2-Kasantuwar mashrikai sun yi imani da cewa wadannan gumakansu su suke tafiyar da wasu ayyukan Ubangiji (rububiyya) shi ya sanya kira ko rokon da suke wa gumakan ya zama ibada, amma musulmai sakamakon tsarkin imaninsu da kadaita Ubangiji suna girmama bayin Allah kuma suna kamun kafa ne da su sakamakon Allah ne ya ba da iko a hakan.
A takaice: haramta kira da aka yi a cikin wadannan ayoyi guda biyu, ya kasance ne sakamakon suna yin hakan ne a matsayin bauta, ba wai ko wane kira ko roko ba wanda yake baya tattare da wannan siffa. Domin kuwa mu gane wannan shiri na masu inkarin Tawassuli da bayin Allah, zamu ka wo wasu daga cikin ayoyin da suke kawowa a wajen bayanai da rubuce-rubucensu, ta yadda zai bayyana yadda suka yi amfani da wadannan ayoyi suka canza wannan al'amari, ta yadda suka dora ayoyin da suka sauka a kan mushrikai a kan musulmai, ga wadannan ayoyi kamar haka:
"Wadannan wadanda suke kira ba su amsa musu da komai" .
"Wadannan wadanda kuke ba zasu iya taimakonku da komai ba, sannan ba zasu iya taimakon kawunansu ba" .
"Wadannan wadanda kuke kira suma bayi ne kamar ku" .
"Wadanda kuke kira sabanin Allah ba su mallaki koda bawon dabino ba"
"Ka ce yanzu mun kira wanin Allah wanda ba ya amfanar da mu kuma ba ya cutar da m u" .
"Kada ka kira wanin Allah wanda ba ya amfanar da kai haka nan ba ya cutar da kai"
Masu inkarin Tawassuli da bayin Allah a wuraren wa'azuzuwansu da rubuce-rubucensu suna kafa hujja ne da wadannan ayoyin suna dora su a kan musulmi masu kamun kafa da bayin Allah ba tare da wani dalili ba, alhali kuwa wadannan ayoyi ba su da wata alaka da tawassuli da ake yi a cikin musulunci. Masu karatu suna iya komawa zuwa ga tafsirai domin su ga dalilan saukar da wadannan ayoyi a bayyane.
Wadannan ayoyi suna magana ne da masu bautar gumaka wadanda suke da imanin cewa amfani da cutarwa, daukaka da kaskantarwa duk suna hannun wadannan allolin nasu na karya, haka nan samu nasara a wajen yaki duk yana hannunsu, ta haka ne abin da suke yi ya zama bauta, domin su samu wadannan abubuwan da suke gani suna zuwa ne daga gare su. Amma musulmi masu kamun kafa da bayin Allah akidarsu kilo mita dubu ta nisanta da wannan akida batacciya, cin nasara da kariya dukkansu suna zuwa ne daga Allah. Don haka girmamawar da suke wa ma'asumai (A.S) sam ba shi da alaka da cewa sun dauka ne su alloli ne ballantana ya zama bauta, suna haka ne domin suna ganinsu bayin Allah ne masu girma da daukaka a wajen Allah.
Mafi yawa cikin addu'o'immu muna cewa ne; "Ya Allah don matsayin Manzonka Muhammad da alayansa" wannan mastayi kuwa ya yake? Wannan matsayi kuwa shi ne matsayin da Allah ya ba su, sannan Kur'ani mai girma yana ambatar wasu daga cikin annabawa da wannan matsayin kamar yadda yake cewa dangane da annabi Musa (A.S) "Ya kasance yana da matsayi a wajen Allah" Haka nan yana cewa dangane da annabi Isa (A.S) "Yana da matsayi a duniya da lahira" Wannan shi ne matsayin da Allah da kansa ya ambata a cikin kur'ani dangane da bayinsa, wanda sakamakon haka ne suke da kusanci da matsayi a wurin Allah madaukaki.
Kalu bale na hudu:
Kamun kafa yana nufin neman taimako daga wanin Allah, Mutumin da yake tawassuli a lokacin da ya shiga cikin halin kaka- na-kayi, wannan yana nufin yana neman taimako daga wanin Allah, duk da yake cewa babu wani wanda za a iya neman taimako daga gare shi sai Allah, kamar yadda Kur'ani yake cewa: "Kawai gare ka muke neman taimako".
Amsa: wannan kuwa yana zama matsala ne ga mutumin da yake bai san wani abu ba daga Kur'ani, domin kuwa a baya mun yi bayani a kan cewa ana iya jingina aiki guda daya zuwa ga Allah a lokaci guda a jingina shi zuwa waninsa, haka nan mun kawo wurare da dama daga cikin Kur'ani da suke bayani a kan hakan, kamar misalin daukar rai ko rubuta ayyukan bayi, sannan muka yi bayani cewa wannan ba shi da wata matsala, domin kuwa jinginawa zuwa ga Allah a matsayin komai yana zuwa daga gare shi ne kuma sai da izinisa, jingina shi kuwa ga wani bawan Allah da ma'anar ya yi wannan aiki ne karkashin ikon Ubangiji.
Allah madaukai ba tare da ya nemi taimako ba daga wani wuri yake aiwatar da ayykansa, amma waninsa yana yin hakan ne tare da izinin Ubangiji, don haka aikinsa ma aikin Allah ne da wannan ma'ana.
Don haka babu matsala a lokaci guda cewa babu wanda za a nemi taimako daga gare shi sai Allah kuma a nemi taimako daga waninsa, domin kuwa neman taimako daga wani bawan Allah ba yana nufin cewa neman taimako daga gare shi maimaikon Allah. Domin kuwa yana yin komai ne da izinin Ubangiji, bisa haka ne Kur'ani yake cewa a wajen Allah kawai ake neman taimako, kuma a wani wuri yake cewa mu nemi taimako daga wanin Allah, kamar yadda yake cewa: "Ku nemi taimako daga hakuri da salla, domin kuwa suna da girma a wajen masu tsoron Allah".
Zulkarnaini lokacin da yake so ya gina bango domin ya kare mutane daga harin yajuju ga abin da yake cewa mutanensa: "Abin da Allah ya hore mini ya fi abin da zaku yi mini, don haka ku taimaka mini da masu karfi"
Duniya musamman duniyar mutane ta kafu ne kan taimakekeniya, sun kuma kasance suna neman taimako da sunayen annabawa da manyan bayin Allah daga junansu, sannan sam ba su ganin wannan ya saba wa asalin kadaita Allah madaukaki, domin kuwa taimakon wanin Allah yana karkashin iko ne na Allah madaukaki, wanda ya bai wa mutum wannan damar.
Abin mamaki a nan shi ne wadanda suke inkarin neman taimako daga wanin Allah suna ganin ana iya neman taimako daga wanin Allah a lokacin da yake raye, amma bayan ya mutu ya haramta kuma yin hakan ma shirka ne, alhalin idan abu shirka ne kasantuwar bangare guda yana da rai da bashi da rai ba ya canza wannan abu, saboda haka neman taimako daga wani idan har ya kasance muna ganin cewa yana iya yin hakan ne tare taimakon Allah sam ba shirka ba ne, wannan kuwa ya kasance yana da rai ne ko kuwa bayan mutuwarsa ne. Daga karshe zamu yi tunatarwa a kan wasu abubuwa guda uku kamar haka: