Muassasar alhasanain (a.s)

Hakkin Sarki

0 Ra'ayoyi 00.0 / 5

MARUBUCI: Hafiz Muhammad Sa'id hfazah@yahoo.com
Hakkin Sarki (Jagora Shugaba)
Imam Aliyyu Zainul-abidin (a.s) yana cewa: "Amma hakkin jagora shi ne ka san cewa shi jarrabawa ce gareka, kuma shi abin jarrabawa ne game da kai saboda abin da aka sanya a hannunsa a kanka na iko, kuma ka tsarkake masa nasiha, kada ka yi gogayya da shi, ka ga ke nan ka sanya shi ya sanya hannunsa a kanka sai ka kasance dalilin halakarka -da gamawa da kai- da halakarsa -da zaluntarka-.
Ka kaskan da kai da tausasawa domin ba shi yarda da kai da abin da zai kame shi daga gareka, kuma ba zai cutar da addininka ba, kuma ka nemi taimakon Allah a kansa a cikin dukkan wannan.
Kuma kada ka dora kanka a kansa, kada ka yi gaba da shi -da saba masa-, domin idan ka yi haka to sai ka sanya shi ya yi laifi a kanka -ta hanyar gamawa da kai- kuma ka yi laifi ta hanyar sanya shi -yin ukuba- a kanka, sai ka sanya kanka fada wa abin ki, ka sanya kansa ta halaka saboda kai, kuma kai ne ke nan ka zama mai taimaka masa a kanka, kuma mai tarayya da shi a abin da ya yi maka na mummuna. Babu karfi sai ga Allah".
Asalin hakkin mulki na Allah ne gaba daya, kuma ayoyi masu yawa sun yi nuni da hakan a cikin Kur'ani mai girma da hadisai madaukaka. Fadinsa madaukaki: "Mulkin sammai da kasa na Allah ne", yana nuni da hakan. Sai Allah ya mika wannan lamarin a hannun annabawansa, ya aiko su ba domin komai ba sai domin dan Adam ya bi su ya samu rahamarsa, amma sai mutane suka bijire musu, suka saba wa Allah madaukaki game da biyayyarsu.
Wadannan hikimomi na Imam Aliyyu Zainul-abidin (a.s) suna nuna mana yadda mutum zai yi taku da shugaba a cikin al'ummarsa cewa kada ya yi wani abu da zai sanya shi ya kasance abin gaba da shi da jagoransa har ya kai shi ya zama abin fadansa. Domin yin haka yana nufin su biyu da shi da shugaban duk su halaka, domin idan shugaban ya kashe shi ko ya daure shi ko ya doke shi a kan saba masa to yana da zunubin zaluntarsa, shi kuwa idan ya yi haka har ya tunzura shugabansa ya yi masa haka to shi ma ya yi laifin sanyawa a zalunce shi.
Imam Aliyyu asSajjad bai tsaya nan ba, har sai da ya yi nuni da babban laifin shi wanda ya sanya jagoransa ya kashe shi da cewa; shi ma ya yi tarayya da jagoransa wurin kashe kansa!.
A nan ne zamu fahimci cewa sarki ko shugaba da Imam Sajjad (a.s) yake nufi a cikin wannan bayanin shi ne jagoran da yake ba ma'asumi ba ne. Domin jagora kamar annabi ko wasiyyin annabi ba shi da siffofin da Imam Sajjad (a.s) ya kawo, domin shi ba ya fusata don kansa sai don Allah madaukaki.
Da sannu zai bayyana gareka cewa shi jagoranci asali Allah ya ba wa annabi ne da wasiyyinsa bayansa, amma sakamakon mutane sun ki jagorancinsu sai suka yi gaban kansu, sai dai ita shari'a sau da yawa akan samu wani abu da ba ta yarda da shi ba, sai dai tun da ya samu, to sai ta kasance tana da nata hukunce-hukunce a kanta.
Don haka ne zamu ga tun da hukuma ta kubuce wa wasiyyan annabi (s.a.w) amma wannan ba yana nufin su yi banza da wannan sarakuna da shugabanni ba, don haka sai suka dauki matakin shiryar da wadannan jagororin da kuma al'umma, da nuna musu hanyar gaskiya, da yi musu nasiha, da gyara akidu da tunanin al'umma kan mene ne gaskiya domin su dace da abin da Allah yake son a sauran janibobin rayuwarsu. Sannan sai Allah ya yi musu hisabi gwargwadon saninsu da nisantarsu da wadanda Allah ya yi umarnin biyayya garesu na wasiyyan annabi (a.s).
Wasiyyan annabi (s.a.w) su ne wadanda aka sanya musu alhakin fassara Kur'ani ga mutane domin suna da ilimi daga annabi da ilhama daga Allah, don haka ne Manzon Allah (s.a.w) ya hada su da Kur'ani a matsayin alkawari karami kuma nauyi bayan Kur'ani wanda yake shi ne alkawari babba nauyi mafi girma, don haka ne suke da wannan alhakin a kansu.
Sannan su ne suke da hakkin jagoranci kamar yadda yake shi ne ra'ayin Shi'a da ya tafi a kan cewa mulki na Allah ne shi ne yake bayar da shi ga wanda ya so, don haka Allah ya ayyana wanda zai jagoranci al'ummar nan, sai dai al'ummar ce ta ki, kamar yadda al'ummun baya suka ki wadanda Allah ya ayyana musu. Ahlussunna da dukkan kashe-kashensu da kuma Wahabiyawa suna ganin mulki yana hannun mutane ne da suke zabar wanda suka so, don haka duk wanda suka zaba shi ne jagora, kuma ayyana shi ba ya hannun Allah!.
Sai dai Shi'a duk da suna ganin iko na Allah ne da ya sanya shi hannun annabi (s.a.w) da wasiyyansa (a.s) sai dai ba su da ikon dankara shi kan mutane sai idan mutane sun yarda. Don haka da mutanen Madina ba su yarda da shugabancin annabi (s.a.w) ba, da ba shi da ikon dora shi da karfi kan mutane, da har ya koma ga Allah bai kafa hukuma ba, kamar yadda sauran wasiyyansa suka yi bayansa.
A nan ne ya kamata mu yi magana kan siyasar musulunci wacce take lamari ne da ya shafi jagorancin jama'ar musulmi kamar yadda yake bisa dokokin shari'a. Amma musuluncin siyasa abu ne maras kyau, domin shi ne amfani da wata manufa domin samun cimma wani hadafi da guri.
Ma'anar farko wato siyasar musulunci tana da kyau domin amfani ne da siyasa domin yin hidima ga addini, kuma hanyar jagoranci kamar yadda musulunci ya gindaya. Amma ma'ana biyu ta munana matuka domin tana nufin a yi amfani da musulunci ne domin cimma wani buri ko hadafi na siyasa, wannan lamari matuka ya munana kuma mun ga misalansa a siyasar duniya a kasashe daban-daban.
Mece Ce Siyasa?
Wasu Suna Cewa: Siyasa a dunkule ta kunshi jagorancin al’umma da tsarin tafiyar da al’amuransu (da yake cikin tsarin da dan’Adam yake a kansa a kasashe da ya hada da majalisar dokoki da ta yin doka (kotu) da ta zartarwa (wacce ministoci da shugaba suke cikinta).
Ashe kenan muna iya cewa jagorancin al’umma a dunkule shi ne ake nufi da siyasa, kamar yadda kalma ce ta larabci da take nufin jagorancin al’umma da tafiyar da al’amuransu. Ko da yake kada mu manta da yadda ake amfani da wannan kalmar da ma’anar yaudara, ko kuma sanya bangaranci a cikin warware wasu al’amura ko kuma kushe wani abu da ya fito ba daga namu bangaren ba, da makamantan hakan.
Idan mun duba tarihin rayuwar dan’Adam tun farkon samuwarsa yana tare da siyasa ne, sai mutum na farko ya kasance shugaba da zabin Allah a kan zuriyarsa, sai ya kasance annabi ne da yake karbar sako daga Allah (s.w.t) kai tsaye domin ya shiryar da shi kan yadda zai tafiyar da al’amuran jama’a a duniya, kai wani tunani da ya zo mini a kwakwalwata da na dade ina mamakinsa shi ne; cewar Allah (s.w.t) a farkon maganarsa game da dan’Adam da zai halitta ya fara ne da maganar siyasa yayin da yake gaya wa mala’iku cewa; zan sanya halifa a duniya. Halifa kuwa yana nufin mai maye gurbin Allah (s.w.t) a kowane abu a duniya da ya hada da tafiyar da al’amuran bayi wanda shi ne bangare mafi muhimmanci, domin kuwa shi ne ya shafi shiryar da dan’Adam kan al’amuransa na duniya da lahira.
Duba ka gani yayin da Allah (s.w.t) ya ce da mala’iku: “Ni mai sanya halifa (mai wakiltata) a bayan kasa ne…” Bakara: 30. Da fadinsa: “Ya kai Dawud mu mun sanya ka halifa (mai wakiltar Allah cikin tafiyar da al’amuran bayi) a bayan kasa, sai ka yi hukunci tsakanin mutane da adalci…” surar Saad: 26.
Da wannan ne zamu iya gane cewa tun farko addini yana damfare da siyasa kai tsaye, kuma tushen addini ya kafu kanta koda kuwa wasu daga malaman musulmi sun ki yarda da hakan.
Amma dayawan ruwayoyi sun nuna mana ba yadda za a yi a cire jagoranci daga tushen addini, don haka imani da jagorancin annabawa (a.s) da kuma wasiyyoyi da wasiyyai (a.s) da suka bari yana daga tushen addini, kuma idan mutum bai yi imani da su ba koda kuwa ya fi kowa biyayya ga Allah a sauran bangarori Allah ba zai karbi ibadarsa ba, don haka ne ma duk wanda ya mutum bai san jagoran zamaninsa ba to ya yi mutuwar jahiliyya. (Minhajul karama, Allama Hilli, Shafi: 27). Domin zai zo a lahira babu wani abu da Allah zai karba na ayyukansa. Don haka yarda da manzon Allah (s.a.w) da wasiyyoyinsa da wasiyyansa (a.s) wanda ya hada da Kur'ani da halifofinsa (a.s) wadanda bai bar mutane ba sai da ya gaya musu wadannan halifofin nasa kuma ya fadi adadinsu cewa su sha biyu (a.s) ne kuma ya fadi sunanyensu sannan kuma Manzon Allah mai tsira da aminci ya gaya wa mutane ba zasu taba kauce wa hanya ba suna tare da Kur'ani har sai sun riske shi a tafkin alkausara a ranar lahira.
Ashe ke nan siyasa ita ce tushen addini da idan ma ba ka zama dan siyasa ba karkashin jagorancin da Allah (s.w.t) ya gindaya maka to kai ayyukanka ba zasu karbu ba har abada, zaka yi mutuwar jahiliyya ne. Don haka ne ma halifan manzon Allah (s.a.w) da ya yi wasiyya da shi na farko kuma jagoran Ahlul-bait (a.s) ya tambayi manzon Allah (s.a.w) bayan ya gaya masa kamar yadda al’ummar annabi Musa (a.s) da Isa (a.s) ba su bi wasiyyansu ba shi ma al’ummar nan ba zata bi shi ba, ya tambayi manzon Allah (s.a.w) cewa; zan yi wa al’ummar nan hukuncin kafirai ne ko kuma hukuncin wadanda suka fada fitina? Sai manzon Allah (s.a.w) ya amsa masa ya yi musu hukuncin wadanda suka fada fitina ne. Wannan kuwa lallai fitina ce, domin babu bala’in da ya kai ga cewa; Allah ba zai karbi duk ibadojin mutum ba!! A nan ne zamu samu natijar amsar tambayarmu cewa; shin addini yana tare da siyasa. Don haka muna iya gani cewa; asali ma tushensa ya doru ne kan siyasar.
Amma tun da al’umma sun kauce wa siyasar Allah (s.w.t) da manzonsa (s.a.w) da wasiyyansa (a.s) kuma jam’iyyarsu mai cike da tsiran dan’Adam a duniya da lahira wacce take jam’iyya ce ta imani na gaskiya, to mene ne hukuncin sauran jagorori da ake rikonsu a matsayin shugabanni? Kuma mene ne sakamakon da ya samu al’umma sakamakon kauce wa siyasar Allah (s.w.t) da jam’iyyarsa. Kuma me ya kamata wannan al’ummar ta yi game da jagoran gaskiya kuma halifan annabi (s.a.w) na sha biyu da yake wannan ne zamaninsa?
Wannan sai ku biyo mu ba shi idan Allah ya sa mun samu lokaci a nan kusa…
Amma tun da al’umma sun kauce wa siyasar Allah (s.w.t) da manzonsa (s.a.w) da wasiyyansa (a.s) kuma jam’iyyarsu mai cike da tsiran dan’Adam a duniya da lahira wacce take jam’iyya ce ta imani na gaskiya, to mene ne hukuncin sauran jagorori da ake rikonsu a matsayin shugabanni? Kuma mene ne sakamakon da ya samu al’umma sakamakon kauce wa siyasar Allah (s.w.t) da jam’iyyarsa. Kuma me ya kamata wannan al’ummar ta yi game da jagoran gaskiya kuma halifan Annabi (s.a.w) na sha biyu da yake wannan ne zamaninsa?
Musulunci addini ne na tsari wanda bai yarda dan’adam ya zauna haka nan babu daula ba, don haka ne ma ya kasance ya dauki matakin kiyaye tsarin rayuwar al’umma da yake akwai maslaharsu a ciki, sannan kuma sai ya shimfida dokokin da yake kiran su hukunci na biyu wadanda sun saba da na asali. Ina ganin domin fahimtar wannan al’amari yana da kyau mu kawo misalan wasu kissoshi da suka zo a littattafan addini:
1. Wata rana Annabi Ibrahim (a.s) yana tafiya a gaban sarkin da ya so ya kwace matarsa amma ya kasa, wanda daga baya ya ba shi kyautar Hajara babar Annabi Isma’il (a.s) sai suka fito suna tafiya gaban farfajiyar fadar sarkin, sai Annabi Ibrahim (a.s) ya shiga gabansa yana tafiya, sai Allah madaukaki ya yi masa wahayi cewa; ya kai Ibrahim (a.s) ka sani babu makawa al’umma ta samu shugaba nagari ne ko fajiri; abin da ake nufi da nagari a nan shi ne wanda Allah (s.w.t) ya zaba a shar’ance a matsayin jagoran al’umma ko kuma jagoran da yake kiyaye kansa daga haram kuma yake aikata duk wajiban da suke aknsa, kuma yake aiwatar da adalci, fajiri kuwa yana nufin duk wanda yake ba bisa wannan ba.
Sai sarkin ya ga Annabi Ibrahim (a.s) ya koma bayansa yana tafiya, sai ya tambaye shi me ya sa na ga ka koma bayana, sai ya ce: Ubangijina ne ya yi mini wahayi da in girmama ka. Wannan al’amarin ya sanya sarkin ya ga girman Ubangijin Ibrahim (a.s) har ya karkato zuwa gareshi.
kissar Annabi Yusuf (a.s) ba nesa take da mu ba, a cikin kur’ani mai girma yayin da ya nemi a ba shi ministan arziki da albarkatun kasa, don haka ne ma wani wanda ya yi wa Imam Ridha (a.s) rashin kunya yana zarginsa da shiga fadar sarki Ma’amun dan Harunar Rashid, sai Imam Ridha (a.s) ya ba shi amsar da ta sanya shi yin nadama, yana mai nuna masa cewa; tsakaninsa (a.s) da Annabi Yusuf (a.s) ya zabi wanda ya fi laifi a wurinsa yayin da shi Imam Ridha ya karbi sarautar Yarima ne bisa tilas, amma Annabi Yusuf (a.s) ya nemi ministan arziki da albarkatun kasan Misira yana mai rokon sarki ya ba shi wannan matsayi, sannan kuma Imam Ridha (a.s) ya kasance a fadar musulmi ne masu shaidawa da Kadaitar Ubangiji madaukaki, yayin da Annabi Yusuf (a.s) ya zauna a fadar mutane ne da suke bauta wa gumaka!
A nan ne zamu ga muhimmancin kare tsarin al’umma da kuma yin hidima ga al’umma da kiyayewa bisa adalci, mu sani Imam Ali (a.s) yana cewa: “Mulki yana wanzuwa tare da kafirci amma ba ya wanzuwa tare da zalunci”. (Sharhi usululkafi: Mazandarani, j 9, s 300.
Sai dai wani yana iya tambaya cewa; Me ya sa wadannan manyan bayin Allah (s.w.t) guda uku: Annabi Ibrahim (a.s) da Annabi Yusufi (a.s) da Imam Ridha (a.s) suka dauki wadannan matakai, ashe ba hakkinsu ba ne su rike jagorancin al’umma sai kuma suka dauki wadannan matakai a gaban wadannan sarakunan lokutansu?
Sai mu ce: matakai ne da suke sassabawa da sabawar yanayi, don haka ne ma hukuncin Allah a kowane fage da ya hada da siyasa yake sassabawa, misali da Imam Hasan (a.s) ya zo lokacin Imam Husain (a.s) da zai yi yaki ne da Yazid, kamar yadda da Imam Husain (a.s) ne a lokacin Imam Hasan (a.s) to da zai yi sulhu da Mu’awiya. Don haka ne mukan ga wani lokaci Annabi (a.s) ko Imami (a.s) ya dauki matakin da ya saba da na waninsa (a.s) kamar matakin Annabi Isa (a.s) a daular Rum da ya saba da matakin Annabi Musa (a.s) a daular Misira kafinsa da kusan shekaru 1100. Ko kuma Annabi daya ya daukin matakan siyasa da suka saba a lokuta biyu kamar yadda Annabi Ibrahim ya kira sarkin Babil a kan Tauhidi har ya kona shi, amma sai kuma bai yi wannan kiran ba ga sarkin Siriya da na Misira. Kuma muna iya ganin Imam Ali ya yi hakuri ya zauna lafiya da halifofin farko bai dauki matakin yaki ba, amma sai ya dauki wannan matakin tare da Mu’awiya, wanda da ya kyale tabbas da ya zama shugaba a zamaninsa shi ma bayan Usman dan Affan, kuma a zahiri yake wadannan matakai sun sassaba.
Wani yana iya tambaya ya ce: To yaya zamu gane wadannan matakai sai in ce yana da wuya ka gane domin abu ne wanda yake bukatar shiriya daga Allah (s.w.t), kuma mutane sun ki yarda su karbi wannan shiriya don haka duk wani bala’in da suka fada su suka jiyo wa kansu, kuma duk da ba zamu iya ganewa ba saboda wahalar sanin wane yanayi ne, kuma wane mataki ne, kuma a wane lokaci ne, kuma waye zai yi, da sauran wahalhalu da suka dabaibaye wannan lamarin amma wasiyyin Annabi (a.s) na karshe ya zartar da matakan wadanda suka gaje shi suka san koyarwarsa suka dauki ilimi daga abin da ya bari suka kai matakin sani na koli duk da kuwa zai iya kasancewa cike da kurakurai, amma da yake bisa hasken doka ne don haka sai ya kasance kuskure ne wadannan manyan malamai zasu iya yi mai lasisi daga Allah, sabanin wani wanda ba a ba shi lasisi daga Allah ba ko Annabi (s.a.w) ko wasiyyin Annabi (a.s), kuma bai ma san koyarwarsu ba.
Wahalar wannan al’amarin ta kai ga cewa; tun da ake tashi domin gwagwarmayar yakar sarakuna masu mulki a cikin sama da shekaru dari biyu da hamsin na wasiyyan manzo (s.a.w) har zuwa karamar boyuwar wasiyyinsa na sha biyu kuma halifansa na karshe da ya yi albishir da shi, ba mu samu wata gwagwarmayar siyasa ta kifar da daula ba da ta samu goyon baya daga wasiyyan Annabi (a.s) sai ta Mukhtar da ya dauki fansa ga makasan Imam Husain (a.s) shi ma ba yarda ta karara ba ce, sai kuma gwagwarmayar Zaid bn Ali tare da karfafawar da suka yi cewa; ba za a taba samun nasara ba, al’amarin da ya kai ga kashe dukkan wadanda suka tashi suka yi wannan motsin.
Idan mun duba a fili yake cewa shugabannin addini na gaskiya da Allah da manzonsa suka ayyana sun riga sun bayar da matakan da ya dace a dauka na shiryar da al’umma zuwa ga tafarkinsu da tarbiyyarsu ga sanin Allah (s.w.t) da hakkokinsa da kuma hakkokin ‘yan’adam da kuma wadanda suka hau kansu, da kuma komawa zuwa ga malamai masu gadon tafarkinsu kawai banda sauran malaman da suke hana mutane saninsu kamar yadda suka kira su da sunan masu fashin imani wanda ya fi na rayuka da dukiyoyi muni. Kuma su ne zasu nuna yadda za a yi mu’amala da kowane mutum ne tun daga sarakuna da shugabanni da kowane jagoran wata al’umma ba tare da rikon su a matsayin su ne jagororinsu na shiriya ba, don haka rikon wani mutum daban jagora kuma shugaba mai shiryarwa ga tafarki sabaninsu to daidai yake da mutuwar jahiliyya!!!
2- Amma abin da ya samu duniya sakamakon kauce wa siyasar Allah (s.w.t) da jam’iyyarsa wannan wani abu ne da yake a fili, muna iya ganin yadda duniyar dan’adam ta bace kan al’amarin duniya da lahira ta fada cikin alakakai da surkukiya; amma al’amarin lahira a fili yake cewa mutane sun kasa sanin addinin gaskiya ko mazhabar gaskiya suna ta dimuwar da ta fi dimuwar shekaru arba’in ta Banu-Isra’ila muni, domin dimuwar yau ta rashin sanin gaskiya ce, wannan kuwa sakamakon ‘yan fashi da suka yi yawa a kan hanyar isa zuwa ga Allah madaukaki ne, sannan kuma dimuwa ce da ba wanda ya san sanda zata kawo karshe. Don haka kamar yadda suka dimauce kan al’amarin lahira ta yadda suke bin kowane irin kira doo. Haka nan ma suka dimauce kan lamarin duniyarsu ta yadda babu wani wanda ya isa ya fitar da duniya daga dimuwarta ta al’adu da zamantakewa da siyasa da tattalin arziki da tarbiyya da makamancinsu ta yadda zai fito da ma’anar adalci a kowane fage wanda yake nufin gaskiya a komai ba tare da tauyewa ba sai wanda yake ya san Allah (s.w.t) hakikanin sani wanda kuma babu wani wanda yake haka sai wanda Allah (s.w.t) ya zaba na annabi (s.a.w) ko kuma wasiyyinsa (a.s), amma su ma da sharadin al’umma ta yarda da jagorancinsu.
Amma abin da ya yake cikin tunanin wasu masu ganin cewa don me ya sa Annabi (s.a.w) ko kuma imami (a.s) bai dauki wasu matakai ba na shari’a? sai mu ce duk wannan yana komawa ne zuwa ga rashin yardar mutane; Misali me ya sa jagororin da manzon Allah (s.a.w) ya yi wasiyya da su ba su riki jagoranci ba? Sai mu ce: yana daga sharuddansu mutane su yarda da su sannan sai su riki jagorancin al’umma. Muna iya ganin yawancin annabawa (a.s) ba su riki jagorancin al’umma ba na tafiyar da mulkinsu saboda al’ummar ba ta yarda ba, don haka ne ma zabe yake da muhimmanci a wannan zamani namu, kuma shari’a ta ki yarda da wani ya jagoranci mutane koda kuwa annabi (a.s) matukar mutanen ba sa so.
Manzon Allah (s.a.w) yana cewa: Allah ya tsinewa mutumin da ya jagoranci mutane alhalin ba sa sonsa.
Don haka ne ma Imam Ali (a.s) ya ki jagoranci saboda mutane ba su zabe shi ba, amma da suka zabe shi ya riki mulki kuma da wani ya tashi domin ya kwata daga gareshi sai ya yake shi da mutanen.
Mulki a hannun bayin Allah (s.w.t) nagari da ya zaba ita ce hanyar shiryar da bayi, don haka idan suka ki Allah madaukaki bai yarda a tilasta su ba. Amma kuma idan mutane suka ki yarda da zabin Allah (s.w.t) -duk da Allah ya kyale su bai yarda a tilasta su karbar wanda ba sa so ba- amma bala’o’in duniya da na lahira zasu durfafe su.
Mu duba mu gani mana a lokutan jagorancin manzon rahama (s.a.w) da Imam Ali (a.s) ba a taba samun wani ya mutu da yunwa ko talauci ba, kuma ba a samu yawaitar jahilci da rashin tsaro ba, kuma ba a samu karancin abinci da yunwa ba saboda tsarin da suka zo da shi a hukumarsu duk da kuwa kowannensu hukumarsa cike take da yake-yake!
Muna iya gani abin da Imam Ali (a.s) ya yi yayin da ya ga wani tsohon bayahude a hanya a Kufa yana bara sai ya tambaya ya ce: me ye haka! Mu duba mu gani bai ce wane ne wannan ba, sai ya ce mene ne wannan, wato bakon abu ne a daularsa a samu bara. Sai ya yi fada kan cewa; wannan bayahuden ya yi wa mutane ayyuka yana saurayi sai da ya tsufa sannan sai a kyale shi!? sannan ya sanya masa albashi daga Baitul mali!
Me kuwa zai sanya dan’adam ba zai wahala ba alhalin ya kauce wa tsarin da zai fisshe shi daga bala’in duniya da lahira, mu sani duk duniya babu wani wuri da ake bin tsarin addinin musulunci kamar yadda Allah (s.w.t) da manzonsa (s.a.w) suka zo da shi, wani wurin ana gaba da addini ne, wani wurin kuma ana jahiltarsa ana yin wani abu daban da sunan addini amma addini ba haka ya ce ba, ba komai ake yi ba sai fahimtar mutanen wurin game da addini. Wani wurin kuma an fahimci addin kamar yadda manzo (s.a.w) da wasiyyansa (a.s) suka zo da shi, amma fa al’adu sun hana a aiwatar da shi. Wannan sai ya sanya duk duniya ba inda ake yin addini koda kashi 50% cikin dari a duk fadin wannan duniyar.
Wasu sun dauka an zo duniya domin shan wahala ne don haka sai suka dauka wahalar da ake sha da ma haka duniya take! wannan lamarin kuwa ya taso daga jahilcin dan’adam ne, ko kuma daukar da ya yi wa abin da yake faruwa kamar daman haka ya dace ya faru! Mu sani duniya da lahira duka an yi su domin samun kamalar dan’Adam ne, bambancin al’amarin shi ne akwai wahalar ibada a wannan duniya. Kuma rashin lafiya da cututtuka duka Allah ya bayar da maganinsu sai dai dan’adam ya nisanci wanda zai yi masa maganin ne. Sannan muna ganin yadda manzon Allah (s.a.w) da Imam Ali (a.s) suka yaki talauci da yunwa ta karfin tsiya da kuma kawo aminci da ilimi da tarbiyya da sauransu. Imam Ali (a.s) yana cewa: Da talauci mutum ne da na kashe shi (Sharhu Ihkakul hakk: J 32, shafi: 257)
Arzikin duniya ya ishi dan’adam amma ya wanzu a bankunan masu mulki da iko ana boye shi ana juya shi, kuma wannan lamarin shi ne abin da Allah ya yi gudunsa yana mai cewa; “…domin kada ya kasance yana juyawa tsakanin mawadata daga cikinku…”(Hashari: 7), amma dan’adam da aka yi arzikin saboda shi sai ya kwana cikin yunwa da musibu da talauci.
Amma batun cewa; me ya kamata wannan al’ummar ta yi game da jagoran gaskiya kuma halifan annabi (s.a.w) na sha biyu da yake wannan ne zamaninsa?
Kuma me ya kamata wannan al’ummar ta yi game da jagoran gaskiya kuma halifan annabi (s.a.w) na sha biyu da yake wannan ne zamaninsa?
3- Amma abin da ya kamata wannan al’ummar ta yi game da jagoran gaskiya kuma halifan annabi (s.a.w) na sha biyu da yake wannan ne zamaninsa shi ne ta koma zuwa ga koyarwarsa, ta san wane ne shi sannan sai ta san wadanda ya ce ta koma musu wajen sanin addininsu, to da wannan ne zasu iya zama ‘yan jam’iyyar Allah madaukaki.
Da wannan ne zasu koma zuwa abin da ya fada a littafinsa: “Kawai hukunci na Allah ne” (al’an’ami: 57). Da fadinsa: “…Hukunci nasa ne…” (al’kasas: 88). Da kuma dukkan ayoyin da suka yi nuni da fasikanci ko kafirnci ko zaluncin wanda bai yi hukunci da abin da Allah ya saukar ba, da wannan ne sai su aikta ayyukan da suke kansu na mu’amala da dukkan wani dan’adam bisa yadda shari’a ta ce musu kamar yadda ya zo daga wajen Allah madaukaki. Sai ya kasance alakokinsu da kowa bisa yadda Allah ya so ne kuma jagoransu na wannan zamani ya tsara ya nuna musu. Da wannan ne zasu kasance ‘ya’yan jam’iyyar Allah madaukaki wacce take da sakamakon yardarsa duniya da lahira.
Irin wadannan malamai da suke bin tafarkin Allah madaukaki da manzonsa (s.a.w) da wasiyyansa (a.s) su ne wadanda manzon rahama (s.a.w) yake cewa: “…hakika malamai magada annabawa ne” (kafi: j2, sawabul ilm, hadisi: 1) da fadin Imam Ali (a.s) cewa; “Malamai su ne masu jagorancin mutane” (Gurarul hikam: 137), da fadin manzon Allah (s.a.w) da yake nuna cewa; idan malamai suka bata to zasu batar da wannan al’umma.
Wani abin mamaki shi ne yadda wasu malamai suka ki fahimtar al’amarin jagoran al’umma bisa gurbatacciyar fahimta sakamakon kaucewa wasiyyar da annabi (s.a.w) ya yi na su bi abin da yake kunshe cikin Kur’ani bisa fahimtar ahlin gidansa (a.s) wadanda Allah madaukaki ya tsarkake su kuma manzon Allah (s.a.w) bai bar wannan duniya ba sai da ya yi wasiyya da su kamar yadda muka yi nuni a baya da halifofinsa goma sha biyu ne kamar yadda ya kawo su kuma ya yi wasiyya da su.
Wani abin mamaki shi ne yadda wasu sukan yi kokarin su boye wasiyya ko su yi musunta, ko kuma su daukar wa kansu yarda da cewa; manzon Allah (s.a.w) ya fadi sha biyu amma bai kawo sunayensu ba, don haka sai su shiga neman kawo sunayen da kansu kamar dai Allah ya yi wahayi cewa; manzonsa (s.a.w) ba zai cika addininsa su ne zasu zo daga baya su cika. Irin wannan son rai yana nan kunshe cikin littattafai daga wasu masu irin wadancan mahanga ta su cika addini da kansu! Allah ya tsare mu tabewa!
Mu sani cewa; tafiyar da al’amarin siyasa da jagorancin al’umma abu ne na wadanda Allah ya zaba ya mika musu ya sanya shi a hannunsu wadanda muka ce imma dai annabi (a.s) ko kuma wasiyyin annabi (a.s) idan kuwa ba haka ba to wanda ya hau wannan mahalli a wajen Allah sunansa fajiri fasiki komai kuwa takawarsa ta zahiri, domin ma’aunin da muke hange da shi, shi ne dai ma’aunin da Allah yake hange da shi.
Idan kuwa yana son kada wannan suna ya hau shi to kada ya sake ya hau wannan mataki sai idan annabi (a.s) ko wasiyyin annabi (a.s) ko kuma wanda wasiyyin annabi (a.s) ya ce ya hau wannan matsayin sakamakon ba a gane shi a fili koda kuwa an gan shi, sai ya mayar da mutane zuwa ga malamai masu wasu siffofin da shi ya ayyana su da kansa da shiryarwar ubangijinsa madaukaki da kuma ta annabin rahama (s.a.w).
Imam Ali (a.s) yana cewa da alkali shuraihu: Ya shuraihu ka zauna a mazaunin da babu mai zama a wurin sai annabi (a.s) ko kuma wasiyyin annabi (a.s) ko kuma tababben tsinannen mutum (al’wasa’il: babin hukunci: babi 2, h 2, shafi: 6). Kamar yadda Imam sadik (a.s) yake cewa: Ku ji tsoron mulki domin shi mulki na malami ne masani da hukunci da adalci wanda yake shi ne annabi (a.s) ko kuma wasiyyin annabi (a.s) (Daga al’wasa’l: kamar na bayansa). Don haka ne ma ake fassara ma’anar malamai a irin wadannan hadisai da annabi (a.s) ko kuma wasiyyin annabi (a.s).
Amma hanzari ba gudu ba: Dayawan malamai sun tafi a kan cewa; idan aka samu wani mumini da yake karbar shawara daga malamai wadanda suke kan tafarkin manzon Allah (s.a.w) da koyarwarsa sahihiya (a.s) ya kasance yana karbar shiryarwa da yadda zai tafiyar da al’amuran al’ummarsa daga garesu to wannan ya fita daga cikin wannan tabewa kuma irin wadannan mutane ba sa ciki saboda su ma yanzu suna karkashin umarnin Allah da manzonsa da wasiyyansa da kuma malamai mabiyansu ne, kuma sun fita daga sunan fajirci, ko dagutanci.
Kamar yadda malamai suka yi fahimta ga hadisin da yake cewa duk wata tuta da aka daga (wato duk wata gwagwarmaya da ake yi) kafin bayyana Sufyani to ta dagutu ce (wato; ba halattacciya ba ce), wasu malamai sun tafi a kan hakan, amma muna iya ganin Imam khomain (k) jagoran juyin musulunci a Iran a 1979, yana ganin hadisin bai hada da tutar da aka daga kuma ta kasance ba ta saba da koyarwarsu ba, sai ya kasance kenan ya halatta malamin da yake bin hanya sahihiya da sharadin ya samu lasisin wasiyyan annabi (a.s) zai iya yin wani motsi bisa sharuddan da suka gindaya. Sai ya kasance wannan kauce hanya bai hada har da shi ba, wannan dai mas’ala ce mai girma da ta tayar da jijiyar wuya saboda santsinta da kuma wahalarta kamar yadda dai sauran mas’alolin siyasa suke. Kuma nan ba zauren karatu ba ne balle mu fadada magana.
Cibiyar Al'adun Musulunci
www.hikima.org
hfazah@yahoo.com
Hafiz Muhammad Sa'id
Sunday, January 09, 2011
 

Ku yi bayanin Ra'ayinku

Ra'ayoyi Masu Dubawa

Babu wani Raayi
*
*

Muassasar alhasanain (a.s)